*🌈DARASI!!🌈*
BOOK 1
✨Rabiatu Bashir
Ummu maher(miss green)🍀💚
*@Wattpad link*
https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_campaign=invitefriends
*@Arewa book link*
https://arewabooks.com/chapter?id=62a48949772e179ad6e54443
Tsokaci:ban yadda wani ko wata yayi amfani da wannan littafin ba wajen canza wani abu ba,wannan littafin mallaki na ne a kiyaye doka ce.
Bismillahir-Rahmanir_Rahim.
*_My parents_*
01
......."Wai ni indo me kika dauki kanki ne da ban isa in gaya miki magana kiji ba,kullum sai kin dorawa wannan yarinyar tallah saboda me zaki ringa kokarin keta duk wata doka da zan saka agidannan?".
"Mlm bafa ka isa ka hanani dorawa wannan yarinyar tallah ba tunda ba kaine kake daukar dawainiyar ta ba,matukar kanason in daina dora mata to kadinga kula da komai nata ciki harda ciyar damu dukkanmu",tana kaiwa nan tayi tafiyarta tana yan kunkuni da karfi.
Shiru Mlm yayi ya goge wata kwalla da ta zubo masa a Idanunsa.
Talla ne akan Fahima itama tana goge hawayen daya cika mata kurmin idanunta sannan ta shigo gidan,ta karaso inda mahaifinta yake ta ce"Baba don Allah kayi hakuri ka daina biyewa Amma saboda ranka zai dinga baci ni kuma banason abinda zai bata maka rai don Allah kayi hakuri".
shafa kan kyakkyawar yarinyar yayi sannan yace"Fahima Allah yayi miki albarka kinji,kema Allah yabaki masu yi miki biyayya kinji".
Cikin tausayin mahaifina na ce"Amin Baba".
Ina tafe ina waiwayen mahaifina da ya kasa fita har yanzu yana nan wajen dana barshi,haushin mahaifiyata ya kara ninkuwa acikin zuciyata,da wannan tunanin na karasa shiga cikin gidan.
"Ke!"
Da sauri na kalli Amma wacce ta kasance mahaifiyata sannan ta ce"Saboda kinyi tsiyar taki kin zubarmin da kudi shine ko sallama ba zakiyi min ba kawai sai ki shigo gida kina neman fadamin kan tukunyar girki ki jazamin siyan maganin da ban shirya ba".
Kallon mahaifiyata nayi wadda na mayar kamar tv tun shigowa cikin gidan,wato ita babu ruwanta da konewa ta ita kudinta ne ya dameta,Amma kenan ita babu ruwanta kudinta kawai ta saka a gabanta.
Jiki na a sanyaye na shige cikin dan rubabban dakinmu wanda kana ganin ginin gidan kasan tsohon ginin ne,runtse idanuna nayi na kalli silin din dakin ina tunanin rayuwar da mahaifana suke yi,kwatata Amma wato mahaifiyata bata mutunta mahaifina kullum cikin fada da gaya mishi bakaken maganganu kawai don bashi da kudi,ina cikin tunanin Kannena suka shigo dakin da na ke,Khalil,sai nusaiba,da Haruna,kannena ukune kacal don Amma tun kan Harun tace ta daina haihuwa da babanmu wai ta gaji da haihuwa ba'a yi mata ragon suna,don haka yanzu shekarun Harun Biyar Amman Amma ta daina Haihuwa,hatta Harun Amma Bata ji kunyar Dora masa talla ba,duk kannena suna talla,kowa da Safiya tayi zai tafi nashi tallan.
Muryar Nusaiba ce naji tana cewa,Anty Fahima wannan mutumin nan da kika hanani zuwa wajenshi,shine yau ya kirawoni wai inzo zai Bani alewa shine ni kuma na gudu.
Kallon yarinyar na Shiga yi hawayen tausayin yarinyar suka Shiga zarya a idanuna,"Anty kuka kike don Allah ki daina kuka idan kina kuka Nima zanyi".
"Ba kuka na ke ba y'ar kanwata,ki gayawa Amma wannan maganar kinji,don ba'asan zuciyarshi ba ".
"Wallahi Anty Amma ba zata yarda ba dukana za tayi rannan ba na Gaya mata ba,shine tace wai k'arya nake kuma wai Kada na sake in gayawa kowa,idan ba haka ba zata zaneni".
"Amma n ce tace Miki haka"?.
"Eh wallahi Anty haka tace wai ko ke da Baba Kada na Gaya muku idan ba haka ba zata k'unani in mutu".
Rungume Yarinyar nayi ina sheshshekar kukan tausayin Nusaiba Yarinyar da Bata fi shekara8 ba Amman har wani Dan iskan ya Fara hakar rayuwarta,gaskiya ya Zama dole asan abin yi,don tasan halin Amma ko don cinikin da Nusaiba ta ke mata zata iya barin Yarinyar har aje a lalata mata rayuwa a banza.
Da daddare muna zaune muna cin tuwon Dare Amma kuma taje barkar haihuwar kawarta,na kalli Mahaifina da yake ta cin tuwonsa cikin farin ciki,na ce"Baba inason zamuyi magana ne"?.
"Ina Jin ki Fahima".
"Baba daman Akan Nusaiba ne,wai kullum ta dauki talla sai wani ya kirawota shagonsa wai zai Bata alewa,da ta fadamin sai nace mata ta dinga guduwa,shine yau ma mutumin ya Kara tare ta",na Fadi hakan ina sheshshekar kuka,don a rayuwata ina matukar son kannena musamman Nusaiba.
Shiru Baba ya yi min baice komai ba ya sha ruwan Dana debo masa ya wanke hannunsa ya saka ta kalminsa ya fita.
Wata kwalla ce ta sauka akan fuskata,to me hakan yake nufi?shima Baba ya Fara bin goyon bayan Amma ne ko me?ai Naga koda na fada masa ya nuna damuwarsa tunda yarsa ce Amman me yasa baiyi wani Abu ba?,duk ni kadai nake wannan surutun daga bisa ni,kuma na koma cikin dakinmu zuciyata babu dadi.
Cikin dare na jiyo hayaniyar Iyayenmu,Baba na yana cewa Amma"Wallahi duk ranar da kika Kara dorawa Nusaiba talla to a bakin aurenki,shasha wacce Bata San inda yake mata zafi ba,kowa yana tattalin nashi yayan Amman ke Banda ke,saboda wani dalili mara tushe da kike tutiya dashi,iya abinda naji Kenan daga nan Mahaifina Bai Kara magana ba sai Amma ce naji ta bude kofar gida ta fita a cikin wannan Daren, Mahaifina ya biyo ta yana Kiran sunanta.
Wani kuka ne ya kufcemin a shekaruna wadanda Basu Gaza 14, ba Amman babu abinda bana ganewa a game da Zaman Iyaye na.
Da k'er Baba na ya shawo Kan Amma ta dawo tana ta sababin fadanta,wai wallahi ita ba zata Kara dorawa Nusaiba talla ba Amman fa ya dinga Nemo abinci a gida.
"Eh naji Insha Allah Zan dinga nemowa da dai a lalatamin rayuwar Y'aya na".
To daga haka kuma ban karajin bakinsu ba,Baba ya rufe kofar ya shigo ya kwanta.
Sai da na Dade banyi bacci ba daga Baya baccin ya daukeni,ina tuna caftar Baba da Amma don Baba na a rayuwarshi ya tsani b'acin ran Amma yanzu zakiji sunyi fada an jima zasu shirya.
****************
Wani kyakkyawan gida na hango me kyau da kuma tsari,colour din Gidan fari ne k'al,tun daga bakin kofar Gidan sojoji ne fal tsaye da bindigunsu sun sai ta gabas dasu,a cikin gidan kuwa wasu flowers ne masu kyau koraye da kuma pink sun haska gefe2 Gidan tsakiyar kuwa yaji wani rantsatstsan interlock me matukar kyau,gida babban gida Wanda idan Ka shige Shi ma sai kayi 2hour ba kaje wani wajen ba.
Wow Kada dai na Gama cikaku da surutu kyaun wannan Gidan sai Wanda ya gani,don Gidan Yadda kukasan white House na America.
Wata mata na hango zaune a wata farar kujera wacce ta gaji da haduwa a garden din Gidan matar ba zata wuce 35 ba,tana waya da wata tana cewa"Falmata wallahi abinnan yana damun kwakwalwata, Haihuwa na ke son Samu ko ta halin kaka,wajen da kika rakani rannan nake son ki sake rakani,zanzo Maiduguri gobe ki rakani,don Yallabai Baya nan sai nan da kwana 3 zai dawo.
Daga cen b'an garen Falmata tace"oky ranki ya dad'e ina jiran zuwanki,yawwa ni kuwa kin Samu kinje Yola din kuwa wajen Maman Yallabai Ammar?".
"Banje ba kuma bazan je,don wallahi na rantse Miki da Allah abinda matarnan tayi min Nima saina Rama,don tana tutiya d'anta ne ni kuma ina tutiya da mijina ne".
"Hhh mutuniya ta Kenan shiyyasa na ke son ki,kiji dadinki matar Yallabai,Insha Allah sai kin haifi magajin Gidan Yallabai Ammar".
Wata dariya Sakinat tayi sannan ta ce"ai ni wando Ce dai dai nake da k'ugun kowa"itama dariya Falmata tayi sannan tace"to ina jiran zuwanki don akwai Wanda mukayi alkawarin fita dashi.
Suna Gama wayar ta shigo cikin sashenta Wanda fadin iya haduwarsa ma b'ata Baki ne,har zata Shiga dakinta sai kuma ta dawo sannan ta nufi wajen wani kyakkyawan hoton wani matashi Wanda ya saka kakinsa na soja,yayi bala'in kyau sai Ka kasa gane Balarabe ne ko kuwa wani half-caste ne,don yana da wani irin sirrin kyau na ban mamaki.
Shafa hoton Sakinat tayi sannan tace"ilove u mijina inason Ka da yawa".
Ganganci ne mace ta rabe Ka,na sani ko ban sani ba ciki kuwa harda wacce ta kawoka duniya,don ni kadai a kayi Ka General Ammar Muhammad Lamido ina matukar so da kaunarka,dafatan Ka wayi gari lfy tana fadin hakan tayiwa hoton kiss ta shige daki abinta,tana kulla Yadda za tayi don itama taga ta ajje kwanta a acikin wannan babbar gonar.
Ammar yana zaune cikin k'aya taccen office dinsa Wanda ya gaji da haduwa,kyakkyawan matashi ne wanda ya gaji da haduwa cikin kayansa na kaki,ya d'aga kansa yana wani tunani,Anya kuwa yana yiwa kansa da mahaifiyarsa adalci kuwa,rabonsa daya saka k'afafunsa a Yola yau shekara 5 Kenan fa,yaso ace kafin wannan tafiyar da ta kamasa zuwa kasar Tunesia yaso yaje,Amman ya dauki alkawari Insha Allah idan ya dawo zai je,ya share wata kwalla da ta cika mishi idonsa,yana cikin tunanin yaji k'arar wayarsa Wanda yasan ba kowa bane illa matarsa Sakinat don ita kadai ce ta ke da numbersa.
"Ranka ya dad'e dafatan kana lfy,Allah ya Kara maka lfy,Allah ya Kara mana dank'on soyayya Amin,shima amsawar yayi da Amin.
nan dai suka Bata lokaci suna soyewarsa da sahibarsa Sakinat.
*UMMU MAHER ce*
*🌈DARASI!!🌈*
BOOK 1
✨Rabiatu Bashir
Ummu maher(miss green)🍀💚
*@Wattpad link*
https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_campaign=invitefriends
*@Arewa book link*
https://arewabooks.com/chapter?id=62a48949772e179ad6e54443
*SIRRINKI👂🏻*
Ki zami mai yi wa mijinki biyayya yin hakan zaisa ki rabauta duniya da lahira👏🏻.
02
......yana Gama waya da Matarsa Sakinat ya d'aga wayarsa ya Kara a kunnensa cikin nutsuwa shiru sukayi gaba kidayansu sanin halin Ammar,Amir ya ce"Kai fa haka kake Ammar Amman sai Ka bugowa mutum waya Ka yi shiru"?.
Shirun Ammar ya k'ara yiwa Amininsa Amir Wanda yanzu ya ke a America da Matarsa da yayansa 4,Gajiya Amir yayi sannan ya ce"Ammar lafiya me ya faru?cikin damuwa Amir yake fadar hakan don yana matukar Jin tausayin abokinsa Ammar don ya hadu da shu'umar mata,baiyi tsammani ba yaji Ammar ya ce"so na ke Ka turomin da number Umma"!.
Mamaki da wasu hawaye ne suka Fara zubowa a fuskar Amir, bakinsa yana kakkarwa ya ce"yanzu Ammar number mahaifiyarka karasa acikin wayarka? abin ya daure min Kai".
"Don Allah Amir Ka tausayamin Ka turomin number Umma,na kasance cikin bakin ciki, kwakwalwata tana gab da tarwatsewa kunnuwa na suna yimin kuwwar muryar Umma na,ina San inji Muryar Umma na",sai wasu hawaye masu zafi suka zubo masa.
Kashe wayar Amir ya yi hawaye yana fitowa a idanuwansa ya saka handcachiep dinsa ya goge hawayen da ya zubo masa,ya Danna message ya Nemo number Umma yana kuka ya turawa Ammar number.
Tunda Amir ya kashe wayar Ammar ya tashi tsaye a office dinsa ya buga tebur idanuwansa sukayi jawur sosai kamar garwashi,allurar Soja ta tashi,gashin jikinsa ya Fara mimmik'ewa,ya Rasa abinda yasa duk wata mace in dai ba Sakinat ba,Baya taba ganinta da gashi ciki kuwa harda Mahaifiyarsa wato Umma,wacce take matukar sonshi da k'aunarsa itace ta dauki nauyin karatunsa tun kafin ya Zama wani Abu ta shige mishi a gaba ya zamo abinda ya Zama tun bayan rasuwar Mahaifinsa,yana cikin wannan tunanin Yaji k'arar shigowar sako,da sauri ya dauka yana sharce wata uwar zufar da ta zubo masa,hannunsa yana kakkarwa ya dauka ya duba number Umma ya kirawo Hannunsa sai k'erma ya ke.
Wayar tana hannun Khalisat wato kanwar Ammar,tana Assignment an Kira yafi sau 3 taki dagawa sai tsaki take tana cewa"gaskiya ko waye wannan ya iya nacin jaraba",ta Fadi hakan cikin yaran Fillo wato fulatanci,sai da wayar ta kusa tsinkewa sannan ta d'aga cikin dakusasshiyar murya tace"waye"?.
"Common ki kawai wa Umma stupid!".
Da sauri jikinta ya Fara kakkarwa don tabbas ta gane muryar yayanta,hawaye suka Fara zubo mata da sauri ta haye step,tana kwalawa Umma Kira wacce alokacin ta ke sallar duha,wato sallar walaha, Khalisat cikin kuka ta ce Umma ya Yaya Ammar a waya"!.
Lokaci daya Umma taji kanta ya Shiga sarawa sosai,zuciyarta taji tana bugawa ta saka hannunta ta danne saitin zuciyarta daya tsananta buga mata.
Khalisat tasan za'ayi haka Amman sai ta goge hawayenta ta ce"Umma ki daga wayar nan kiji me zaice Miki,ki ajje fushinki a gefe ki janyo danki a jikinki don Allah".
Hannun Umma yana k'erma ta saka hannunta ta amshi wayar,sai dai ta kasa saka wayar a kunnenta.
Yaron da ta keso ta ke k'aunarsa Amman yau an wayi gari ya wofantar da ita,ya guje ta tamkar wata mujiya,idan Bata manta ba yau tsahon shekara 5 rabon da ta saka Ammar a idaniyarta balle har ya bugo mata waya.
Duk abinda a keyi Ammar yana Ji,kuma yana jiyo kukan Amminsa,hankalinsa ya tashi jijiyoyin kansa suka tashi sosai ya dafe kansa yana kuka.
Da sauri Khalisat ta saka wayar a handsfree don Umma taji muryar d'anta sosai,ai kuwa tana saka muryar taji Ammar yana cewa.
"Ammina"!
Sai kuka yaci k'arfin Ammar wani amai ya taho masa,ya ajje wayar ya ringa kwarara amai kamar me yaron ciki,ta cen bangaren Umma tana Jin Ammar ya Fara amai,hankalinta ya tashi ta Fara Kiran sunansa tana cewa"Ammar don Allah Kada Ka saka kanka cikin wani Hali Nima Ka sakani,don Allah kayi magana inji Muryar Ka".
Itama anan kukan yaci k'arfinta ta yarda wayar tana matsanancin Kuka,Khalisat ma hawayen ta ke tana sharewa Umma hawayen sannan tana bubbuga bayan Umman kamar k'aramar yarinya.
Kiran wayar Ammar Khalisat ta ringa yi Amman Bai daga ba,k'arshe ma taji an kashe wayar,hankalinta ya tashi ta Rasa Yadda zatayi gashi,ga Umma ciwon zuciyarta ya tashi da k'er ta Samu ta balli maganinta ta Bata ta Samu bacci,gashi kuma Yaya Ammar shima yana cikin wani Hali.
Kifa kanta tayi tana kuka me tsuma zuciya,tana kuka tana cewa"Anty Sakinat Baki kyauta mana ba kin rabamu da sanyin idaniyarmu,kin raba D'a da uwa,kin raba soyayya me k'arfi,Why me yasa kika yi mana haka?Meye ribarki?".
Nan dai Khalisat ta ringa surutai marasa Kan gado,daga Baya ta tashi ta yi alwala ta Fara sallar Nafila tana kuka tana rokon Allah subhanahu wata'ala ya kawo musu sauki da haske cikin wannan lamarin.
************
"Wallahi Fahima Kada ki sake ki dauki tallannan ki zubarmin da kudi,kika yarda kika zubarmin da kudina ranar saina ci ubanki a Gidanan".
"Na gode"
Na ji muryar Baba ya fito daga ban d'aki ya cigaba da cewa"Fahima Kada ki Dade kina zuwa idan kiga babu ciniki ki dawo".
Cikin sassanyar Murya ta na ce"Insha Allah Baba bazan dad'e ba".
Na dauki tallan na tafi ina tunanin Hali irin na Amma,ita dai zata Samu kud'i babu ruwanta da matsala,ko da hakan yana barazanar lalacewar rayuwar y'ayanta.
Yauma banyi wani cinkin kirki ba na taho gida saboda ƴan garuwar da muke siyarwa duk sun tafi gida don haka yanzu babu ciniki,gaba yana dukan 3 na taho gida don nasan yau Amma Bala'in ta akan babanmu zai ƙare.
Tun daga soro na kejin hayaniyar atika mai kayan gonjo da amma ana ta hira ana shewa,sam ban son matar Ƙwata2 saboda Atika duk wani rashin mutunci itace ta ke koyawa amma shi,ko kallon Atika banyi ba nayi hanyar ɗakinmu tare da yiwa Amma sannu da gida,ko amsamin bata yiba sai kallon kayan tallan kaina ta ke tana hararata,jikina ya hau rawa don idan nayi sa'a ne ma zai tsaya a zagi don nasan har duka sai ta yi.
"Ke zo nan don ƙaniyarki".
da sauri naje har ina haɗa hanya don tsoron Amma na ke ji kamar mala'ikan mutuwa.
"Yanzu ita Atikan itace abin wulaƙantawa a wajenki?idan Adama ƙanwar ubanki ce zakiyi mata haka?tsugunna ki gaisheta kafin inci ubanki la'ada waje don bazan zuba miki ido kina rashin mutuncin da kika dama ba.
"Hmm Amma dama kin ƙeleta yaran yanzu ai sai a hankali ballantana ma idan suka ga sun fara tashen balaga sai kaga abubuwa kala2".
"haba Atika ba tashen balaga ba Allah yasa tashen tsuntsaye ne wallahi ni babu ruwana dukan kawo wuƙa zanyi mata, daman ga haushin ubansu ina fama dashi ayi namiji kamar mai zuciyar karya baya ajje komai sai yawon ƙasan bishiya daga wannan ta tafi ya koma wancan inuwa."
zuciya ta ce naji tana ta tafarfasa kamar zata ƙone don naƙi jinin a zagar min uba abin yana taɓa min zuciyata sosai.
Ina cikin wannan tunanin sai kuwa naji Atika tana cewa"ni wallahi Amma dama birni kika bayar da wannan yarinyar aka kaita aiki da mun huta da ganinta tsogai2 tana yawo a gari.
Saurin ɗago kaina nayi jin maganarta wai a kaini aiki?
*ummu maher ce*
*🌈DARASI!!🌈*
BOOK 1
✨Rabiatu Bashir
Ummu maher(miss green)🍀💚
*@Wattpad link*
https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_campaign=invitefriends
*@Arewa book link*
https://arewabooks.com/chapter?id=62a48949772e179ad6e54443
*SIRRINKI👂🏻*
Yin tsarki da ganyen magarya yana taimakawa wajen kashe Ƙwayoyin cuta musamman lokacin gama al'ada.
-----------------------------
03
.. . . . . ."Wallahi Amma ni babu wani gidan aiki da za'a kaini ina jin fa yadda ake bada labarin duk yaron da aka kaishi aiki yanke kanshi ƴan birni suke su cinye namanshi har da romanshi".
"Ai wallahi ƙaryarki kuwa ki zauna min a gida muna haɗa kafaɗa da ke a cikin gidannan dolen ki tafiya birni kije ki nemo mana kuɗi wallahi,kullum mu kenan cikin talauci ke ko kunya ma bakyaji kullum kina yawo da wannan koɗaɗɗan zanin".
Kuka ne ya kufcemin na fita waje zuwa gidan kaka ta wacce ta haifi mahaifiyata,ina zuwa gidan na tarar da ita a bakon murhun ƙasa zata ɗora sanwar dare,na fashe mata da kuka sosai harda majina.
"Ke ƴar nan lafiyarki kuwa kika shigo min gida kina sharce hanci kamar wata tatsitsiyar yarinya"?.
"ba Amma bace ita da Atika wai birni zasu kaini aikin wanke2 da shara,ni kuma wallahi ba zanje ba."
"yanzu Amma son kuɗin nata har ya kai ta kaiki birni aiki? ni wallahi spn kuɗin yarinyar yana bani mamaki,don kawai Allah ya jarabci mahaifinki shikkenan sai ta shiga yawon neman kuɗi kamar wata wacce ta fito a turu,"maza tashi ki share hawayenki insha Allah babu wanda zai kaiki aikatau kinji".
sai da daddare sannan na koma gida amman a wannan lokacin Nusaiba ta dawo daga tallan kayan miya,tsaye nayi ina kallon ikon jalla mai duka,na kirawo sunanta da Ƙarfi har sai da ta tsorata.
"Daga ina ki ke Nusaiba"?.
"Yaya daga talla na ke,ban siyar da wuri bane shine wani mutumi yanzu ya siye duka yace gobe idan na ɗakko in kawo mishi wani kango zai siye duka,kinga na huta da dukan Amma".
Ƙwalla ce mai zafi ta zubo daga ƙwarmin idanuna na ce"Nusaiba daga yau ba zaki sake talla a gidannan ba wallahi",ina faɗar hakan naja hannunta tana wai gawa ko zata ga Amma don dukkanmu tsoranta muke sosai.
Gidan Inna na kaita inda na baro yanzu, har ta ja ƙofarta za ta rufe sai ta ganmu ni da Nusaiba mamaki ya hanata magana amman fuskarta fal ta ke da mamakin ganinmu.
"Inna don Allah don Annabi ga Nusaiba nan ta dawo wajenki da zama,saboda zamanta wajen Amma babban hatsari ne babba",na fashe da kuka Inna tana rarrashi na.
Nan na ƙwashe duk abinda ya faru tun daga farkon tallan Nusaiba har kawo yanzu,shiru Inna tayi tana tunanin hali irin na ƴarta wato Amaturrahman.
A yanzu hankalina ya ƙwanta sosai don riƙon Nusaiba ya koma gun Inna har ta saka ta a makarantar islamiya da ta boko,sai dai fa har yanzu aƙwai sauran Rina a kaba don yanzu Amma ta ƙara ƙaimi wajen kaini aika tau daman ga haushin na kai Nusaiba gidan Inna wai tunda ni ce na kaita dole yanzu in dinga yin tallan Nusaiba na kayan miya,da yamma kuma tallan taliya da mai da yaji,babu yadda na iya dole ne inyi abinda Amma tace don ni a yanzu daɗi na ke ji da riƙon Nusaiba ya koma gun Inna.
*** *** ***
Jirgin ƙarfe 10 ya hayo daga Tunesia zuwa Abuja,kana ganin yadda ya ke tafiya kasan bashi da cikkakiyar lafiya ajikinsa,don Ammar fari ne daman ƙal mai matsaicin jiki don haka duk wanda ya sanshi zai tabbatar da tabbas ba lafiya ya ke,motoci ne sun kai biyar suka zo tararshi a Airport ɗin suka shiga daskarewa suna sarawa ogansu wato general Ammar.
Kai tsaye ɓangarensa ya nufa sakamakon da sashen Sakinat ya ke fara zuwa amman yau sashensa ya nufa,babu wanda ya faɗawa zuwanshi Nigeria hatta da aminansa basu san da maganar dawowarsa ba.
Sai da daddare bayan yasha baccinsa tare da mafarkin aminsa,ya fito zuwa sashen Sakinat tsit kamar babu kowa sai masu aikinta suna ta kai kawo,da Lantana ya fara haɗuwa sabuwar mai aikin da ta yi,ta durƙusa har ƙasa tana gaisheshi cikin girmamawa ya amsa ba tare da ya kalli inda ta ke ba,sai jin muryarta yaji tana cewa"ranka ya daɗe ai Hajiyar bata nan yau kwananta 4 kenan".
Cak yaja ya tsaya sai a lokacin ya jiyo,Lanta ta haɗiyi wani yawu 'maƙut' don tsabar tsoronsa da ta ke yi,ƙyaunsa da ƙwarjininsa yana ƙara ninkuwa a azuciyarta.
"Kika ce ta yi tafiya?".
"eh yallaɓai" ta faɗi hakan cikin tsoro da fargaba.
Wucewarsa ya yi sama bai ƙara bi takanta ba,har ya zaro wayarsa zai kirawo ta sai kuma ya fasa ya sakko zuwa ɓangarensa yana tunanin hali irin na Sakinat,a shekara 8 ɗin da sukayi da Aure zai iya ƙirga sau nawa Sakinat ta tambayesa zuwa unguwa duk sanda ta yi niyya kawai tafiyarta ta ke yi,har zuwa wasu ƙasashen ma,a kullum tambayar kansa ya ke me yasa duk abinda Sakinat ta ke yi mai bai taɓa tsawatar mata ba duk da yana da matuƙar zuciya amma ta zama ta banza,duk izzar da ya ke da ita in dai ya shigo gida ko baya tsoron Allah to ya zama dole ya zama bawan Sakinat don mugun tsoronta ya ke.
Sakinat ce zaune gaban boka tsidau tana cewa"boka so na ke nima in haihu ko ta halin ƘaƘa ne don ba zan yadda wannan dukiyar da na ke gani ta tafi a tutar babu ba,ayi duk abinda za'ayi ko nawa ne zan biya matuƙar dai nima zan samu abinda na keso."
wa wa keken bakinsa ya buɗe ya ce"ni boka tsidau na yi miki alƙawarin haihuwa a gidan multibuloniya Ammar,akwai abinda zamuyi miki matuƙar kika yi to tabbas za ki samu Haihuwa don haka ki saka aranki ma kin samu". sai ya bushe da wata irin dariya mara daɗin sauraro.
"Tashi ki biyoni kin samu Haihuwa kin gama".
dariya ce ta kama ƙawar Sakinat wato Falmata don tasan abinda bin boka tsidau ya ke nufi,ɗan jiyowa Sakinat ta yi ta kalli ƙawarta da ayar tambaya a bakinta sai dai babu ikon yin maganar don boka tsidau tuni ya yi gaba cen ƙarshen dutsen inda wata ƴar ƙaramar bukka ta ke.
Wa iya zubillah wannan boka aranar sai da sukayi alfasha da Sakinat kuma ya tabbatar mata cewa buƙatar ta kamar ta biya ne.
Masha Allah Ammar shirye ya ke cikin wata tsadaddiyar shaddarsa ruwan arsh ya gyara gashin kansa wanda ya ƙwanta luf luf irin na asalin fulanin usul,fatarnan sai walƙiya ta ke yasha agogonsa na rolex ya yi matuƙar ƙyau,wani irin nishaɗi ya ke ji don ayau zai ga Amminsa bayan shekara 5cif ba tare da sun haɗuba.
Yana shiga motar dieban yaja sauran motocin suka biyosa ya rufe idanunsa kamar mai jin bacci daman kuma aƙidarsa ce kuma haka Allah ya halicce sa baya mintina ba tare da ya yi hakan ba,hakan baƙaramin ƙara masa ƙyau ya ke ba,ga waɗanda basu sanshi ba sai suce iyayi ne.
Wata muguwar harara Sakinat ta bugawa ƙawarta Falmata ta ce"gaskiya Falmata baki da mutunci da ki ka haɗani da wannan bokan gashi yanzu ya haɗa jiki dani in banda wari da hamami babu abinda ya ke,ni wallahi Allah ya isa kawai kuma yanzu ba sai
Anjima ba Zamu je hospital a dubani".
Dariya Falmata ta yi bata ce komai ba suka cigaba da tafiyarsu har suka kai bakin titi suka tari mota suka tafi,duk jikin Sakinat ciwo kawai ya ke.
Ko da aka duba ta lafiya ƙlau babu wata cuta sai anan taji wani babban abu ya wuce a maƙogoranta ta amshi ruwan sanyi ta kora,suka hau mota Falmata ta wuce gida ita kuma Sakinat ta wuce Adamawa wajen mahaaifinta.
Jiniya ce ta cika titin baki ɗaya ko da ba'a gaya maka ba kasan wani mai babban muƙami ne zai wuce don haka sai matsawa a ke.
Salati Sakinat ta yi ganin motocin mijinta G.A M wato general Ammar Muhammad.
*Ummu Maher ce*
*🌈DARASI!!🌈*
BOOK 1
✨Rabiatu Bashir
Ummu maher(miss green)🍀💚
*@Wattpad link*
https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_campaign=invitefriends
*@Arewa book link*
https://arewabooks.com/chapter?id=62a48949772e179ad6e54443
*SIRRINKI👂🏻*
Shan kayan marmari yana taimakawa wajen bunƘasa lafiyar jiki.
----------------------------
04/05
. . . . . Sakinat aranar ta koma Abuja Don firgici da tsoro,duk hatsabibancin Sakinat tana matuƙar jin tsoron Ammar don shima hatsabibin kanshi ne,wannan asirin da ta yi mishi ma da wani babban jigo ta haɗashi har aka samu abinda a keso.
Har gudawa Sakinat ta yi don ta tsorata da ganin Ammar a Adamawa,to yaushe ma ya dawo ba tare da ya sanar mata ba?kuma me yaje yi Adamawa?abin tambayar ta shine ba dai gidan mahaifiyarsa yaje ba?da sauri ta tashi daga zaunen da ta ke,tana girgiza kai tana cewa"no.no.no ba zai yiyu ba ace yaje wajen mahaifiyarsa ba,don tafi kowa sanin cewa farraƙu ta saka aka yi musu a tsakaninsa da mahaifiyarsa.
Har dare Sakinat tana sukuku gashi ta kira aminiyarta Falmata ringing yafi goma bata ɗaga ba,ƙarshe ma taji an kashe wayar wayar.
"Wato ma kada in dame ta shiyyasa ta kashe wayar ko?shegiya mayya kawai ai nasan tunda ta ce baƙo za tayi to lallai tana cen tare dashi"ta yi wurgi da wayar hankalinta a tashe,ga ta da tarin tambayoyi amman kuma babu mai amsa mata.
Sai kusan ƙarfe uku sannan bacci ya ƙwashe ta daman babu halin yin sallar asuba don Sakinat sai taga dama ma take yin sallah,wa iya zubillah.
Sai kusan ƙarfe uku sannan bacci ya ƙwashe ta daman babu halin yin sallar asuba don Sakinat sai taga dama ma take yin sallah,wa iya zubillah.
Ammar kuwa yana isa Adamawa ya kira Aliyu babban abokinsa mazaunin Adamawa amman wani lokacin yana Abuja Babban gidan da Ammar ya sai mishi,yana kiransa bugu ɗaya ya ɗaga yana tsokanarsa da angon sakinat,"mlm bar wannan tsokanar kana cikin gari ne?kazo zaka yimin jagora wajen AMMI."
"Welldone aboki na ina yiwa Allah godiya da ya karkato da hankalinka akan mahaifiyarka,insha Allah yanzu zanzo.
Sai da Ammar ya jira yazo sannan suka tafi suna ta hirarsu ta abokai,daman su uku suka tashi Amir,Ammar,sai Aliyu,ana kiransu da first A.
Khalisat tana tafe tana bitar karatunta na hadda alokacin ta fito kenan za taje islamiyya,sauri ja da baya ta yi don ganin motoci kala sunfi goma a bakin gate Ɗin gidan kana ganin motocin ba sai an gaya maka ba kasan sun haɗu sosai.
Aliyu ne ya fara fitowa yana kallonta cikin murmushi,itama murmushin ta mayar masa tana sake kallon motocin gabanta yana faɗuwa.
Ƙafar sa ya fara sakowa kafin ya fito,da sauri Khalisat ta ja da baya kamar za ta faɗi badon tsohuwar motar Ammi ta tare ta ba da tuni ta faɗi.
Ya.ya.ya.ya.sai kuma ta zunduma da gudu ta yi cikin gida tana kiran Ammi!ammi!!Ki fito kiga wani abu,kafin ta gama rufe bakinta tuni Ammar ya shigo shi da amininsa Aliyu.
Kusan daskarewa Ammi ta yi a tsaye tana kiran sunan Allah tare da godewa Allah daya dawo mata da farin cikinta wato ɗanta Ammar.
Da gudu ya rungume Amminsa yana kuka yana kiran"ilove u my Ammi na ki yafe min don Allah,na tuba bazan sake ba ya haɗa hannayensa alamar neman yafiya.
Ita ma kukan ta ke tana "son na yafe maka Allah na gode maka da ka dawo min da farin cikin raina".
aranar waɗannan Familyn suna cikin farin ciki sosai,ya yiwa Ammi alƙawarin sai ya yi sati biyu kafin ya koma don ya samu hutu,sosai Ammi taji daɗi tana ƙara saka mishi albarka,don tasan duk abinda ya yi ba da sanin sa bane asiri ne.
Tunda Ammar yaje bai kira Sakina ba,hankalinta ya tashi sosai ta dinga kiransa a waya amman yana gani yaƙi ɗaukar wayar ƙarshe ma ya kashe wayar.
Suna zaune da daddare suna cin abinci Khalisat ta kalli yayanta,ta ɗauki ruwa ta fara sha ai Ammar yana ganinta ya yi saurin ƙwacewa yana ce wa"inye lallai Khalisat kin samu sarari yanzu ruwa ki ke sha kina cin abinci?.
"Wallahi Yaya" ranƙwashi Ammar ya kai mata yana ce wa"me ɗan ƙaramin baki kawai.
Murmushi Ammi ta yi tana kallon ƴaƴan na ta cikin so da Ƙaunar su,tana roƙon Allah ya bar maya ƴaƴanta guda biyu da ta mallaka a duniya.
*** *** ***
Amma ta ƙara matsamin sosai yanzu don talla na ya ƙaru yanzu inyi na safe inyi na rana inyi na dare,bani da lokacin hutu Baba na babu yadda zaiyi don yanzu ma har ya fara shiru da bakinsa,tunda ita dai amma ba dai na wa za ta yi ba,don haka ya tattara ta ya watsar da ita don rashin kunyar da ta ke mishi abin yana damunsa.
Ni daman ba a zancen arabi ballan tana boko kullum ina yawo a gari gayyar talla.
Rannan da daddare ina tafe tsoro fal a ciki na don ban taɓa yin dare irin na yau ba,don nasan idan na koma gida sai Amma ta yi gunduwa2 dani.
Wani kango nazo wucewa naji wari kamar nawiwi,na toshe hancina ina kakarin amai,kawai sai naji wani yana ce wa"kai Ba-ba waccen yarinyar me ta ke toshewa hanci ne?".
"oho bari muje muji me ta ke toshewa hanci. . . ...
Anan zan tsaya don rashin comments.
*🌈DARASI!!🌈*
BOOK 1
✨Rabiatu Bashir
Ummu maher(miss green)🍀💚
*@Wattpad link*
https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_campaign=invitefriends
*@Arewa book link*
https://arewabooks.com/chapter?id=62a48949772e179ad6e54443
*SIRRINKI👂🏻*
Ki yawaita yiwa ƴaƴanki addu'ah yin hakan zai taimaka miki wajen shiryuwar ƴaƴanki.
-------------------------------
06/07
. . . . .har nazo ƙwanar layinmu sai naji kamar ana bina a baya,ga warin taba dana wiwi ya haɗe waje ɗaya suna bada wani irin ɗoyi me wari,sauri na fara yi ina waiwayansu don tun ina hangosu daga nesa yanzu kurkusa na ke hango su.
Gudu sosai na fara yi amman kun san gudun mace dana miji ba iri ɗaya bane dai gashi sun cimma ni,kuka na farayi ina basu haƙuri amman ko sauraro banga suna yi ba,don ko ɗigon tausayi babu a fuskarsu,abinda naga ɗaya daga cikinsu yana shirin aikatawa ne yasa na buɗe bakina na taƙarƙare na rusa uban ihu,yana zuge ta zugen wandonsa yana lasar
Baƙin bakinsa wanda ya gaji da shan tabar wiwi.
Wata shaƙa babban nasu ya kawo min tare da duka na akai nan da nan na daina ganin komai sai duhu,saurin ɗaukata suka yi da ya ke dare ne babu wanda ya gansu suka shiga dani wani kango.
"Kai ba-ba ya zamuyi da wannan yarinyar kada fa a kamamu".?
"au tsoron kamen ka
Ke kai" ?,kawai mu ƙwashi rabonmu mu mu wuce mu bar ƴar talla masu son kuɗin jaraba ai daman ƙarshen son kuɗi kenan",ya faɗi hakan yana lashe bakinsa.
"Haba Amma ta ya ya zaki ƙwanta ki yi ta bacci amman kuma ƴarki bata dawo ba har yanzu?ki duba agogo ƙarfe goma na dare fa?gaskiya Amma wannan mummunar ɗabi'ar da ki ka ɗakko ba za ta haifa miki ɗa mai ido ba",yana faɗar hakan ya yi hanyar waje yana cigaba da mitarsa kamar zai cinye ta,amman matar nan Ƙara juyawarta ta yi tana baccinta har da minshari,Haruna ma da ya ke ƙarami kuka ya dinga kuka ganin Fahima bata dawo ba,don ya saba ita ke kaishi ya yi fitsari.
A hankali ya ke tafiya yana ɗan duba lungu2 na layinsu,ƙwatsam ya hango wani lungu,ci ke da ƴan daba suna shawarwari a tsakaninsu akan su aikata mata ko kada suyi.
Shahada ya yi yaje wajen ya haskosu da babbar fitilarsa,da sauri suka jiyo dukkansu kana ganinsa kasan shine mahaifin yarinyar nan don har hasken da ƙyau irin na fulani duk na shi ne.
"Aha kace kazo ne ka karɓi ƴar ka ko"?.
sai suka tuntsire da wata mahaukaciyar dariya suna nuna baban Fahima.
Kukan kura ya yi ya bige mutum biyu Alokaci guda da ya ke sun bugu sosai suka zube a wajen,saura mutum biyu,da sauri ya yo kansu suma suka fita da gudu,ya tsugunna yana hawaye har sun fara yagawa Fahima kayanta abin tausayi.
Kawai sai yaji saukar wani abu a bayansa tun daga nan bai ƙara sanin inda ya ke ba.
*** *** ***
Da wuri Sakinat ta dira a garin yola babban birnin adamawa,tana sanye da glass baƙi no respect wanda ya gaji da haɗuwa yana sheƙi da walwali.
Ta saka ƙananun kaya komai na jikinta ana gani ita daman ƙirar slindium ne da ita babu cinya babu sharaɓa sai fari wanda har yawa ya yi mata saboda bleaching.
Chewin gum ne abakinta tana taunarsa yana ƙara ƙara ras-ƙara ras,alamar za ta yi rashin mutunci kenan .
Bata sha wahalar gane gidansu Ammar ba don rabonta da zuwa shekara shida kenan,kallon gidan ta ke tana ya mutsa fuskarta,taja trolley ɗinta tana wani yauƙi da yanga kamar mutanen gidan suna kallonta.
Hanan tana sama tana hango ta,da sauri ta sauko don ba ta son Ammi tasan abinda zai faru don wallahi ba za ta bari wannan matar ta shigo musu gida ba,suna cikin farin cikinsu ta kawo musu baƙin ciki.
"Ke makira ina zaki"?.
Hanan ta faɗi hakan tana ɗaga mata gira tare da tare hanya.
Wani banzan kallo Sakinat ta yi mata ta cire gilashinta tana kallonta ta ƙasan glass ɗin, sannan ta ce"Hmm Hanno ki ke ko wa?to ma dai ko me ye sunanki?,ko wannan siririyar bafulata na bata isa ta ce za ta hanani shiga wannan ruɓaɓɓan gidanba wanda ko albarkacin fenti ba ya samu.
Idanun Hanan suka yi jawur jin zagin rashin mutuncin da Sakinat ta ke musu,da sauri ta nuna Sakinat da hannu ta ce"Hmm da ba asan asalin balbela ba da sai ta ce daga misra ta ke,ke kin manta gidan na ki uban ko albarkacin siminti bana tunanin ya samu"?.
"kuma kinga gidannan kaf babu siriri sai wannan makauniyar uwar ta ki wacce har ta mutu bata gani saboda baƙin cikinki dana wannan baƙin basa muden uban na ki,kuma kaf gidan na mu babu wanda ya fito ba ta hanya ta halak ba,wani kuwa sai da a kayi cikinsa sannan aka yi aure. . .
Cikin matsanancin fushi Sakinat ta kaiwa Hanan wani mari,Hanan ta shafa wajen da hannunta ta ce"ko yanzu Sakinat na fiki cin ribar zance tunda gashi har kinyi mari saboda fusata,amman fa baki mari banza ba don ba a marin wannan ƙyaƙyawar fuskar tawa a zauna lafiya ko mijinki ne kuwa ballan tana ma ke."
wani mari Hanan ta kaiwa Sakinat wanda sai da yasa ta riƙe hannun ƙofar shiga farlon,wata shaƙa Sakinat ta kaiwa Hanan,ta kama maƙogoron ta Hanan ta kama kararin mutuwa,Ammi ta fito za ta gidan barka ta hango abinda ya ke faruwa.
Da sauri ta ƙaraso tana rabasu tana mamakin ƙarfin hali irin na Sakinat,sa ƙer Ammi ta ɓanɓare Hanan ta ƙwanta luf a hannun Ammi kamar ba ta numfashi.
Sakinat tayo kan Ammi za ta haɗasu duka,suka jiyo sallama Ammi na kallon tsinanniyar shigar da Sakinat ta yi wai a matsayin matar Aure matar ɗanta tilo.
Amir ne da matarsa har da ƴaƴansa biyu,sosai sukayi mamakin ganin Sakinat a gidansu Ammar don sun san takun saƙar da ke tsakaninsu.
Amir ya ce"Ammi lfy me ya samu Hanan ɗin?wani abu ne ya same ta?."
gaba ki ɗaya ya tambayeta,Ammi ta shaida masa duk abinda ta gani a lokacin da tazo,bata gama ƙarasawa ba me gayya me aiki ya fito yana sanye da kayan motsa jiki don bai san abinda ya ke faruwa ba,yana zuwa Sakinat ta saki kuka ta faɗa jikinsa kamar ƴar yarinya.
*** *** ***
A wajen mahaifin Fahima ya faɗi baya motsi,ƴan patrol suka zo wucewa suka hango ƴan daban nan suna Ɗaukar Fahima,da sauri suka zo wajen suna zuwa suka arce da gudu amman an kama guda ɗaya.
Aka kai su Fahima asibiti aka fara yi musu taimakon gaggawa,sai dai mahaifin Fahima har yanzu bai farfaɗo ba amman Fahima ta farfaɗo.
Allah sai kun fara comments zan fara yin sa da yawa.
*Miss green ce*
*🌈DARASI!!🌈*
BOOK 1
✨Rabiatu Bashir
Ummu maher(miss green)🍀💚
*@Wattpad link*
https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_campaign=invitefriends
*@Arewa book link*
https://arewabooks.com/chapter?id=62a48949772e179ad6e54443
*SIRRINKI👂🏻*
Kada ki bari kishin mijinki ya kaiki ga halaka,ki yi kishi na sunnah wayo da dabara,yawan kishi yana kaimu ga halaka ƙarshe kuma kibar mijin saboda kishi.
-----------------------------
08/09
. . . . .har yanzu mahaifina bai farfaƊo daga suman da ya yi ba,sai dai yana numfashi,hankali na ya tashi sosai don likitoci sun faɗamin Mu biyu aka kawo mu ni da mahaifina,kuma tunda aka kawo mu ƴan sintirin da suka kawo mu sune suke biyan kuɗin.
Amma tana gidan goggo mahaifiyarta sai faɗa ta ke mata na rashin mutuncin da ke yi,gashi yanzu daga ni har mahaifina babu mu babu labarinmu,sharce hawaye ta yi da majina ta ce"wallahi Goggo ni fa ban san yadda a kayi yarinyar na neme ta na rasa ba,daga tura ta talla tun jiya bata dawo ba,idan zubarda kuɗin tallan ta yi ta dawo mana,shi kuma Malam da karan baninsa ya tafi nemo ta,gashi yanzu babu labarinsu su duka".sai ta cigaba da kukanta.
Tun da ta fara maganar Goggo ke yi mata wani banzan kallo,sai da ta gama sannan ta ce"wai ni kuwa Amaturrahman kina da kirki kuwa?"cewa fa ki ka yi wai mahaifinta ya yi karanbani?shi da ƴarsa sai yaƙi fita nemanta saboda sakaci da kuma rashin hankali?,ke irin wannan riƙon na yi miki a rayuwarki?tambayar ki na ke yi?".kamar za ta daki Amma ranar ta yi suna cikin wannan halin ne a kayi sallama a ƙofar gida.
Kallon banza Goggo ta yiwa Amma sannan ta ce"w/kslm waye?".ta ɗauki mayafinta ta leƙa.
Salati ta fara yi tana kiran sunan Allah tana cewa"to shikken Mlm Bashir yanzu zamu taho insha Allah",da sauri ta dawo tana faɗawa Amma wai ƴan sintiri ne jiya suka kai su Fahima da mahaifinta asibiti,kuma tunda safe akaje cen gidan Amma ba a sameta ba,shine Bashir ya ce yasan kina nan gidan.
Bakin Amma bai mutu ba da abinda ya faru da mijinta da ƴar ta ba sai cewa ta yi"Hmm su Bashir an riƙa wajen iya gulma yanzu har yasan nan na taho?".
lokacin har Goggo ta saka hijabi ta ɗakko kuɗi ta ɗaure a bakin zaninta"ta ce to maras tunani idan kin gama gulmar mutane ki tashi mu tafi?wa wiya kawai mara tunani,har a wannan halin da ake ciki bakin ki bai mutu ba".
*** *** ***
abin mamaki Sakinat tana fara kuka hankalin Ammar ya tashi,ya kalli Khalisat da ke jikin Mahaifiyarsa tana kuka ya daka mata wata uwar tsawa ya ce"shut up!ki yiwa mutane shiru munafuka wato daman bakya son matata ko?to wallahi ko waye zai ƙi matata ko waye wallahi tallahi saina rabu dashi".ya faɗi hakan cikin yaran fillanci ya riƙe hannun Sakinat suka yi wuce warsu,Sakinat harda wani la fewa ajikin Mijinta tana yiwa su Ammi gwalo.
Ni kuwa na ce oh Sakinat kamar abin arziƙi haɗa ɗa da uwa,Duniya ina zaki damu😭.ya Allah ka haɗa mu da surukan arziƙi Amin.
Sororo Ammi ta yi tana kallon bayan ɗanta Ammar,shi kuma tasa ƙaddarar kenan mace,jiya i yanzu yana tare da ƙanwarsa suna hira kamar abin arziƙi,amman yau daga zuwan matarsa har komai ya watse.
Wasu zafafan hawaye ne ya fara zubowa Ammi a ƙwarmin idanunta, bata san sanda Khalisat ta saka hannu ta fara share mata hawaye ba,ita ma Khalisat ɗin kuka ta ke na tausayin kansu"Ammi ki yi haƙuri don Allah kinji,komai ya yi farko yana da ƙarshe kada ki saka wannan abin a ranki kinji?".rungume junansu sukayi suna tausayin kansu dana Ammar.
Har sun manta da tsayuwar Amir sai da sukaji yana cewa"haƙiƙa Sakinat ba ƙaramar butulu ba ce da ta manta,da duk abin arziƙin da ki ka yi mata ta butulce miki,ta zaɓi taci miki mutunci ta kassara miki rayuwaɓ,ta zaɓi hanyar musguna miki ta hanyar mallake miki ɗanki,amman babu komai aƙwai Allah."
Matar Amir ma har kuka ta yi don ganin abinda ya faru,tana yawan ji a littafin hausa da sauran kafofi yadda ƴaƴa suke wulaƙanta iyayensu, amman bata taɓa gani da idanun ta ba sai yau.
a ranar Sakinat ta saka mijinta a gaba kamar mayya suka tafi Abuja,shi kuwa Amir saboda haushi daman alokacin ya tafi gida,saboda takaicin hali irin na Ammar ace ka rasa wanda zaka ƙunta tawa a rayuwarka sai mahaifiyarka wacce tasha wahala a rayuwarta don rayuwarka ta ginu?gaskiya abin aƙwai lauje cikin naɗi.
Ranar gidan Ammi kamar ana zaman makoki,gidan shiru don ɗan wannan zuwan da Ammar ya yi komai sun ƙara shaƙuwa sosai,ranar kusan raba dare Ammi da Khaisat sukayi suna kaiwa Allah kukansu ta hanyar yin nafilfilu.
Abin mamaki ranar Amma ta saka rigima wai mu koma gida alhalin har yanzu mahaifina bai farfaɗo ba,aranar na sake tabbatar da rashin tausayin Amma,Goggo ce tace mata idan ta gaji a yini ɗayan da ta yi,to ta tafi gida ita za tayi jinyar sa tunda shima ɗanta ne,jin wannan da Amma ta yi yasa ta zauna amman ba don ranta yaso ba don biyunnan da ta yi bata yi sana'a ba abin yana matuƙar damun ta sosai.
Hmm kuji fa rashin tausayi irin na wasu matan,mijinki yana ƙwance bashi da lafiya,mijin da ki ke saka ran samun aljanna ta ƙarƙashinsa amman ace kina nuna masa rashin tausayi haka?😭.
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un.
A ranar likitoci sukayi bincike wai mahaifina ya. . . .
Yasin idan kuna comments da yawa zan ƙara yawan tyiping oh.
*Miss green ce
*🌈DARASI!!🌈*
BOOK 1
✨Rabiatu Bashir
Ummu maher(miss green)🍀💚
*@Wattpad link*
https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_campaign=invitefriends
*@Arewa book link*
https://arewabooks.com/chapter?id=62a48949772e179ad6e54443
*SIRRINKI👂🏻*
Ki yawaita yiwa ƴaƴanki addu'ar ƙwanciya bacci yin hakan zai tsaresu daga dukkanin sharri.
--------------------------------
10/11
A ranar likitoci suka yi bin cike suka gano mahaifina ya kamu da ciwon ɓarin jiki,kuma suka rubuta magani da allurai masu tsada wai saboda idan aka yi mishi zai samu reliep kuma idan yana samin kulawa zai warke baki ɗaya,magani da allura shine ya tashi dubu sittin da biyar,kai tsaye Amma ta ce wai mu tafi gida ba sai anyi masa ba,wataran idan Allah ya kawo ayi aikin.
Hankali na dana Inna ya tashi sosa ta fashe da kuka tana cewa"oh Allah sarki Abu kin bani amanar Ɗanki yanzu gashi na kasa riƘewa",,sai ta fashe da wani kuka mai cin rai.
Fahima tana gefe itama tana wani irin kuka wanda harda amai sai da tayi kamar ance mahaifin ta ya rasu ne.
Ƙwanci tashi asarar mai rai yanzu watan Baba na huɗu da samun matsalar ɓarin jiki wataran ma har yamma baya samun abincin da zai ci,ya rame ya zama wani kamar tsoho ɗan shekara sittin abin dai gwanin ban tausayi.
Rannan na fita talla ina tafiya ina hawaye bana ganin gaba na ballan tana baya na,kawai sai ga wata mota ta yi saurin yin ribas don ashe ina tsakiyar hanya kuma motar tana ta yimin horn amman ban sani ba.
A hankali na cikin motar ya fito yana cewa"haba beauty ya zaki fito kan hanya kina tafiya bakya kallon hanya,me ya yi zafi haka shi ba wuta ba?".
a hankali nima na kallesa hawaye yana zuba a idanuna nace"yi haƙuri ban gani ba ne".na faɗi hakan cikin ƙaguwa don na matsu in siyar in koma in ga Baba na.
Handcachep ya ɗakko sai naji kawai hannayensa yana gogemin idanuna,cikin sanyayyar murya na ce"na gode".
"Dont mentioned beauty".
kallonsa na yi don ban san me yace ba,ya fuskanci hakan don haka ya ce"nan gaba ki dinga kula da hanya kinji don ke haryanzu girl ce".
da ɗan sauri na wuce ina ƴan dariya don rabon da inyi dariya har na manta,amman ban san abinda ya sakani dariya yau ba,ammn ni dai nasan tunda na kallesa naji wani abu ya tsaya azuciyata ko meye hakan oho".
Biyoni ya yi ya ajjemin kuɗi da yawa akan farantin sanman yace"idan kinje gida ki yiwa almajirai sadaka".kamar bazan amsa ba ammn dai na daure na amsa don tuno da masifar Amma idan na koma gida.
Abuja
Sai da Ammar ya ƙarasa hutunsa a Abuja sannan ya koma Tunesia don ƙarasa aikinsa,Sakinat kuwa kamar ta zuba ruwa a ƙasa tasha don tsabar farin cikin ta raba ɗa da uwa,Sakin duniyar nawa ma take baki ɗaya wataran mutuwa zamuyi.
Tana zaune tana waya tana cewa"am gaskiya yakamata kazo don tun jiya general ya koma,kuma kasanshi Ɗan ra'ayi ne ba ko da yaushe muke kasan cewa ba,don ɗan ra'ayi ne kuma gaskiya ina buƙatar zuwanka,ta faɗi hakan cikin shagwaɓa,a ɗaya ɓangaren kome aka oho?tace oky sai na jika ta kashe wayar tana ƴar dariya.
Sai kuma ta gimtse fuska tana cewa"aikin banza ko ta yaya ma mutum zai samu ciki oho".
duk abinda ta ke faɗa Raliya tana jin ta mai yi mata aikin sashenta tace"Hajiya na gama aikin nawa in tafi gida ne"?.
Ai wata Uwar ashar Sakinat ta ƙundu mawa Raliya ta ce"gidan uwarki zakije da zakizo ki tsayamin akaina munafuka shegiya ƴar talakawa,kuma wallahi ina fatan ko kinji me nake cewa kika nemi tona min asiri wallahi sai na saka an ɓatar ɓin dake".
tana faɗar hakan ta yi gaba abinta,Raliya ta bita da idanu,tasha kama Sakinat tana kawo maza amman har yau bata taɓa ganin fuskar wanda ya ke zuwa ɗin ba ballan tana ma ta bada shaida.
Ko wadda ta turo ta don ta ɗaukar mata rahoto amman har yau bata fara ɗauka ba don Sakinat ta iya takun ta sosai.
Kuyi haƙuri bani da lfy ne👏🏻.
*miss green ce*
*🌈DARASI!!🌈*
BOOK 1
✨Rabiatu Bashir
Ummu maher(miss green)🍀💚
*@Wattpad link*
https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_campaign=invitefriends
*@Arewa book link*
https://arewabooks.com/chapter?id=62a48949772e179ad6e54443
*SIRRINKI👂🏻*
Ki guji ha intar mijinki wajen fita ba tare da ya sani ba,Allah ya tsaremu da cin wuta Amin.
------------------------------
12/13
. . . .Ina zuwa gida na miƙawa Amma cinikin duka harda ɗoriyar kuɗin da wannan bawan Allah n ya bani,murna harda rawa Amma ta farayi ni kuwa kallonta kawai na ke yi ta ɗoramin talla na ɗari biyar,na kawo mata kusan dubu uku amman bata nemi ba asi ba,sai nice na ce"Amma wannan kuɗin baki tambayeni inda na samo shi ba?".
sai a sannan ta ɗan ɓata rai ta zauna kan turmi tana yimin kallon tuhuma ta ce"ikon Allah ke kuwa a ina kika samo wannan kuɗin me yawa haka?gaskiya kasuwar yau ta yi ƙyau sosai."
ɗan yatsina fuska na yi sannan na ce"wani mutumine ya haɗu dani a hanya shine ya bani kuɗin sannan kuma ya ce inyi sadaka da sauran".
na faɗi hakan ina kallon ɓangaren da mahaifina ya ke,idanunsa a rufe kamar me bacci,na lumshe idanuwa na inajin wani irin raɗaɗi a cikin zuciyata,ban sanda hawaye ya shiga sakkomin ba,sai ji na yi Amma na cewa.
"Ai wannan cinikin yanzu kasuwa zanje in saro kayan koli don mu ƙara jari,idan wannan ya tashi ki gyara mishi jikinsa ni ns tafi,ta nuna mahaifina da hannu a ya yinda ta ke saka mayafinta don fita,babu neman izini babu komai haka Amma ta saka mayafinta ta yi tafiyarta kuma tana bani sallahun wai idan ya ɓata jikinsa in gyara masa.
Kuka na shigayi babu ji babu gani don yadda zuciyata ta ke ta faman raɗaɗi sosai,ina Allah wadai da hali irin na mahaifiyata Amma.
Ko babu komai ai bai kamata ta ce in kula dashi ba saboda zai iya fitsari a zaune har ma da kashi,kenan ni ya kamata in ga tsaraicin mahaifina a wannan shekarun nawa da basu gaza sha huɗu ba,duk da a nahiyarmu ta ruwan kanya,da wuri a ke yiwa yara aure saboda mu fulani ne na usul.
Ni kaɗai na ke ta maganganu na babu mai bani amsa a haka na tashi na fara gyaran gidanmu ina cikinyi,na ga kamar alamar mahaifina ya buɗe idanunsa ƙwalla ta cika ƙwarmin idanuwansa tana ta sakkowa.
Jiki na a sanyaye na ƙarasa kusa dashi ina sharemai hawayen nasa,ya juyo ya kalleni yna son yimin magana amman bakin baya fitowa sosai,don bakin ya yi gefe gaba ki Ɗaya,kuka na fashe dashi kamar raina zai fita a tsugunnan da nake,da Ƙer ya ce"mama na ki daina kuka kinji insha Allah Zanji sauƙi kinji Inna woru na".
Ƴar dariya na yi na sunkuyar da kaina zara zaran gashin idona ya jiƙe da hawaye,ya tambayeni ina Amma na ce mishi bata nan,sai naga yana kiciniyar tashi alamun ya yi wani abu yana son a wanke mishi.
Ganin hakan da na yi na taimaka mishi na ɗebo ruwan na zuba mishi na rufe mishi suturarsa ya saka ɗayan hannun yana wankewa abin tausayi.
Tunda Amma ta ce ta tafi kasuwa bata dawo ba sai bayan isha'i bata bi takan mahaifina ba ta ɗora girkin dare babu ko magi a ciki ta zuba mana ni da ƙannai na muka fara ci,ita kuwa daman tazo da tsire da kuma gurasa na kasuwa ta cinye abinta,mahaifina ma wannan abincin yaci mara magi.
Kash!duniya kenan mata muji tsoron Allah mijin da ka ke saka ran zama dashi har a gidan aljanna kuma ka ke neman aljanna a wajensa amman kuma ka ga gara kyauta ta masa,Allah ka bamu ikon kyauta tawa mazajenmu Amin.
Amir yana zaune yana cin abinci amman hankalinsa baya kan abincin saboda tsananin tunanin wannan yarinyar da ya gani ɗazu gashi bai tambaye ta gidansu ba?yanzu ya ya zaiyi tunda ya ke bai taɓa jin son wata ƴa mace irin son da ya kewa wannan yarinyar da ya gani a ƙauyen Ruwan kanya,amman insha Allah kafin ya tafi zai nemi wannan yarinyar don yana ji a jikinsa matuƙar bai aure taba komai zai iya faruwa,yana cikin wannan tunanin Amira ta kirawo sa matarsa.
Yana ɗauka ta fara kuka tana cewa"Abban safna tun jiya muna asibiti safna bata da lafiya numfashinta ya ƙi saituwa har yanzu don Allah kadawo Kadawo".
da sauri ya ajje wayar hankalinsa ya yi matuƙar tashi a ranar Amir ya koma duk ya rame saboda tashin hankali.
A ranar Safna ta ce ga garunka nan Bayan Amir ya koma😭.. . .
*miss green ce*
*🌈DARASI!!🌈*
BOOK 1
✨Rabiatu Bashir
Ummu maher(miss green)🍀💚
*@Wattpad link*
https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_campaign=invitefriends
*@Arewa book link*
https://arewabooks.com/chapter?id=62a48949772e179ad6e54443
*SIRRINKI👂🏻*
Ki zamo mai suturta jikinki kada ki fita ƙariyatun ƙasiyatun,ki zamo mai lulluɓe jikinki.Allah karabamu da cin wuta Amin.
14/15
"Ammi don Allah ki daina kukan nan, da saka damuwa aranki abinda yaya Ammar ya ke buƙata a wajenki kawai addu'a ya kamata ki dinga yi masa,damuwarki za ta haifarwa da Yaya matsala sosai aruyuwarsa,don haka ki share hawayenki ki yi masa addu'a insha Allah Sakinat sai ta girbi abinda ta aikata miki,don raba ɗa da uwa ba ƙaramin abu ba ne."
"insha Allah auta na daina kukan nan daga yanzu".
dariya Khalisat ta yi sannan ta ce"Ammi a kullum idan na tuno wacece Sakinat a cen baya abin har mamaki ya ke bani,kamar ba ita ce ƴar aikin ki a baya ba,kucaka ƙazama."
dariya Ammi ta yi wanda ya fi kuka ciwo tana tuno wacece Sakinat a ba ya.
*Asalin labarin Sakinat*
kamar yadda Khalisat ta faɗa Sakinat mai aiki ce a gidansu tun zamanin mahaifinsu yana nan kafin daga bisani kuma ya yi hatsari ya rasu.
Sakinar ƴar asalin maiduguri ce a cen aka haifeta ita kaɗai ce awajen mahaifinta tun tana ƙarama mahaifiyarta ta rasu,bayan mahaifiyarta ta rasu ne suka koma garin adamawa anan kuma riƙonta ya koma gun yayar mahaifinta.
Yayar mahaifinta ita ce ta kai Sakinat wajen aiki da kanta don ta ce tunda taƙi talla dole ne ta yi aiki,gidan farko da aka kaita yaron gidan ya yi mata fyaɗe daga nan kuma suka jo ne da yaron gidan don kullum Sakinat tana ɗakinsa,duk sanda
Za suyi mu'amala sai ya bata wata ƙwaya ta hana ɗaukar juna biyu,sakinat kuwa bata san ko na me ye ba don ba tada ilimin da za ta gane.
Kwatsa rannan mahaifiyar yaron ta gansu ta yiwa Sakinat korar kare,daga nan ta koma gidan yayar mahaifinta mai suna Abuwalle.
Abuwalle mace ce mai shegen son kuɗi da son duniya don haka babu daɗewa ta samo wa Sakinat aiki a gidansu Ammar.
Tun ranar da Sakinat ta fara aiki a gisansu Khalisat Ammar ya dawo daga tafiya daga ƙasar germany,Tun da Sakinat taga Ammar hankalinta ya tashi don kyaunsa da nutsuwarsa ba ƙaramin dagula mata lissafi ya yi ba.
Ta rasa yadda za ta yi da rayuwarta don ko kallo bata ishe sa,ko mopping ta ke idan ta hangosa ɓuya take saboda matuƙar ta gansa to fa zuciyarta ta yi ta bugawa kenan,har sai ya bar wajen da kusan awanni sannan za ta samu damar fitowa don cigaba da aiki.
Ammi ba macece mai takura ba saboda ba ta ɗaya daga cikin matan da ke wahalar da ƴan aikinsu ba,saboda macece mai mutunci da kuma karamci.
Ana cikin haka ne Sakinat ta fara wani irin ciwo,idan ciwon na ta ya tashi har aman jini ta ke,babu shiri Ammi da Alhaji Muhammad Lamiɗo wato mahaifin su Ammar suka kai Sakinat asibiti.
Tashin farko bayan likita ya gama gwaji ya ce ai Sakinat tana da ciwon zuciya,adinga yi mata duk abinda ta keso saboda idan ba haka ba ciwon ba zai warke ba.
Hankalinsu ya tashi sosai bayan sun dawo gida shima Ammar ya dawo ganin da Sakinat suke tare ya yi gaba zuwa cikin babban farlon gidansu,yana zama sai ga su Ammi sun shigo.
Suka saka Sakinat a gaba da tambayar abinda ya ke damunta kai tsaye ta ce ita Ammar ta ke so. . . ..
Kuyi haƙuri wani busy ne shiga ne👏🏻👏🏻👏🏻👏🏻.
*Miss green ce*
*🌈DARASI!!🌈*
BOOK 1
✨Rabiatu Bashir
Ummu maher(miss green)🍀💚
*@Wattpad link*
https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_campaign=invitefriends
*@Arewa book link*
https://arewabooks.com/chapter?id=62a48949772e179ad6e54443
*SIRRINKI👂🏻*
Mu yawaita tunawa da mutuwa yin hakan zai rabutar damu duniya da lahira.Allah ka tsaremu daga shiga wuta Amin.
--------------------------------
18/19
Maganar ƙarshe da mahaifin Ammar ya faɗa shine"Ammar kada ka wulaƙanta wannan yarinyar kada ka juya mata baya,don kaga bani da rai,kada ka taɓa rabuwa da ita ma'ana ka saketa matuƙar ka saketa to ka saka a ranka babu ni babu kai."
wannan maganar ita ce ta ƙarshe da ya faɗa ya fara wani irin tari mai sarƙe maƙoshi daga nan rai ya yi halinsa,babu irin kukan da Ammar bai yi ba na rashin mahaifinsa ga abu goma da ashirin wai kada ya yarda ya saki Sakinat,shi ya rasa me yasa ma ƙwata2 ko kallonta ba yasan ya yi,yadda kasan wata mujiya haka take a wajen Ammar amman ya zamar masa dole ya fara sakin jiki da ita ko don nasihar mahaifinsa.
Bayan wata biyu rannan Sakinat tana zaune suna hira da Ammi,aka yi sallama da gudu Sakinat ta rungume Falmata ƙawarta ta yarinya ta,sosai taji daɗin zuwan Falmata don tunda ta yi aure ko dangin mahaifiyarta basu zo ba,don basu san ma ta yi auren ba.
Kalle2 Falmata ta shiga yi sosai irin kallon tsaf ɗinnan,Ammi sai kallonta take tana mamakin hali irin na wannan baiwar Allah.
Sai da Sakinay ta ɗan dunguri Falmata sannan ta dawo cikin hayyacinta,tana harar bayan Sakinat don gani take Sakinat bata dace da wannan gidan ba ita ce ta dace dashi,don haka ko ta halin ƙaƙa sai ta zauna itama a wannan gidan kuma ta fitar da ƙawarta Sakinat.
Tunda Falmata tazo gidan babu abinda take sai zuga Sakinat akan cewa wai tsabar baya sonta har yanzu yaƙi ya kaita gidanta ya barta a gidan iyayensa,wani lokacin kuma ta ce kinga gidansu kamar aljannar duniya ko ina gwanin sha'awa,duk yadda akayi komai shi yake a gidan kuma yana jin maganar mahaifiyarsa.
Da ya ke Sakinat sokuwa ce sai maganganun Falmata suka fara tasiri aranta har ta fara ganin ayanzu za ta iya fito na fito da Ammi don tun ba yau ba tana ganin irin abubuwan da Ammar ya ke wa Ammi,yana matuƙar girmama maganarta don har yafi jin maganar mahaifiyarsa da ta mahaifinsa.
Acikin satin Ammi babu irin rashin kunyar da ba ta gani ba awajen Sakinat kuma ta lura Falmata ce ke ƙara zugata,don haka duk sai ta watsar da su ta cigaba da sabgoginta,don dama Khalisat tana boarding Ammar kuwa ya yi tafiya zuwa ƙasar England wani aiki.
Ƙwanan Falmata biyar ta haɗa kayanta don tafiya gida,ta tambayi Sakinat ina ne ɗakin Hajiya,babu musu Sakinat ta nuna mata ta ƙwanƙwasa alokacin Ammi tana azkhar.
Ammi ta buɗe mata ta shigo tana gaida Ammi,ta amsa tana mamakin ganinta bata gama mamakin ba ta jiyo Falmata tana ce wa.
"Da man gida zan tafi shine na ce bari inyi miki sallama sannan in faɗa miki wata magana don nasan baki sani ba,lulluɓin biri aka yi muku.
Da mamaki Ammi ta ke kallonta tana mamakin hali irin na Falmata na munafurci,wato don taga ƙawarta ba ta nan shikkenan sai kuma ta yi gulmarta.
"Hajiya Sakinat fa kafin ta auri ɗanku sai da aka cire mata ciki har sau biyu,kuma wallahi har yanzu bata daina bin maza ba".
da sauri Ammi ta ɗaga mata hannu sannan ta ce cikin tsawa"get out in my room".
da sauri Falmata ta fito har tana haɗa hanya tana da na sanin zuwa wajen Ammi don yadda kasan zaki haka ta juye mata.
Akan hanya suka haɗu da Sakinat sannan ta rakata har bakin gate,tana mamakin sauyin Falmata lokaci ɗaya.
Ammar yana dawowa Ammi ta sakashi a gaba da ya tafi da Sakinat sabon gidansa na Abuja,babu yadda ya iya haka ya tafi da ita ransa baiso ba.
Wannan tafiya itace ta zamewa Ammi wannan mummunan tabo a rayuwarta don tun daga ranar Ammar bai sake zuwa wajen mahaifiyarsa ba,don tun bayan komawarsu da Sakinat ta ga Ammar ba ya ko kallonta ballan tana ta saka ya yi mata magana.
Da kanta ta nemi Falmata suka haɗa kai aka raba tsakanin ɗa da uwa Ammar da Ammi.
*Cigaban Labari*
*Fahima*
-------------------
A yanzu Amma ta matsamin wai acikin mane ma na wai in fito da mutum ɗaya don ita ta gaji da kallona babu aure,abin har mamaki ya ke bani don har yanzu ko shekara sha biyar ba amman ake min zancen aure.
A cikin masu sona aƙwai wani Alhaji Tasi'u mai nera,shine wanda Amma tafi don yana matuƙar jiƙata da kuɗi.
Ita kuwa Fahima ta yi mugun tsanarsa don mutumin mugun ɗan iska ne duk ranar da yazo sai ya nemi daya taɓa jikina ni kuma in ƙi yarda.
Kuma kamar maye gobe ma sai ya dawo,kuma a ƙalla ko da baiyi shekara hamsin ba to kaɗanne.
*miss green ce*
*🌈DARASI!!🌈*
BOOK 1
✨Rabiatu Bashir
Ummu maher(miss green)🍀💚
*@Wattpad link*
https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_campaign=invitefriends
*@Arewa book link*
https://arewabooks.com/chapter?id=62a48949772e179ad6e54443
*SIRRINKI👂🏻*
Kada ka aikata wani laifi ka ɗauka Allah baya ganinka idan kai baka ganinsa to shi yana ganinka.Allah katsaremu da cin wuta Amin.
16/17
. . .Wani Mugun kallo Ammar ya wurgawa Sakinat da ke lafe a jikin Ammi,sannan ya kalleta cikin wata muguwar tsawa yace"i hate u!i said i hate u!"shin ana soyayya dole ne,me zanyi dake kucaka ƙazama mara class,ni kuma in rasa wacce zan aura sai ke? Stupid girl kawai mssttttt".
Ya buga wani uban tsaki ya haye upstair don gani ya ke idan ya cigaba da kallon wannan mumu girl ɗin komai zai iya faruwa dashi,ƙarshe power ɗinsa na soldier ya motsa ya shiga jibgarta.
A hankaki Alhaji Muhammad Lamiɗo ya zauna ya kalli Sakinat ya ce"tashi ki koma ɗaki ki kwanta kinji Allah ya yi miki albarka".
da sauri Sakinat ta tashi kamar daman ta matsu ta tashi ɗin,Ammi tabi bayanta da kallo ta ce"Alhaji yanzu ya ya ka ke ganin za ayi"?.
"Insha Allah komai zaizo da sauƙi amman kafin nan zanyi shawara zuwa ko gobe fatanmu Allah ya tabbatar mana da alkhairi.
***
Ammar yana ɗakin motsa jikinsa yaji a jikinsa kamar ana kallonsa,da sauri ya juyo,Sakinat ce tsaye a kansa ta lu-la duniyat tunani,wata uwar tsawa ya buga mata ita kuwa tana cen kogin tunaninsa yadda gashin ƙirjinsa ya ƙwanta luf luf gwanin sha'awa ruwan gumin jikinsa ya jiƙa duk beauty ɗin skin ɗinsa abinka da ƙyaƙƙyawa sai ya yi wani ƙyau mai ɗaukar hankali.
Wani banzan kallo ya yi mata a karo na biyu sannan ya tashi ya yi tafiyarsa.
Sakinat ta bisa dana mujiya kamar za ta haɗiyesa tsabar so da ƙaunarsa.
"Ammar!"Alhaji muhammad ya faƊi sunansa cikin babbar murya ya ce"me sunan manya Ɗazu misalin Ƙarfe uku da rabi na rana an Ɗaura aurenka da wannan Yarinyar Sakinat abisa yardar waliyyanka da waliyanta don har garinsu na je muka taho da babanta".
Kansa a sunkuye tun da Alhaji ya fara magana baice komai ba,don iyayensu sun yi matuƙar ƙoƙari wajen basu tarbiyayya,idanuwansa sunyi jawur sosai jijiyoyin kansa sun tashi ruɗu ruɗu,ba Ammar ba hatta Khalisat sai da taji wani iri har a cikin zuciyarta.
Tunda Ammar ya Tashi daga wajen mahaifansa kai tsaye motarsa ya hau ya fita,wayarsa ya ɗauka ya kirawo Aliyu ringing na farko ya ɗaga yana tsokanarsa da ango don ɗazu yaji komai na game da auran da Dad ɗinsa ya yi masa.
Banza Ammar ya yiwa Aliyu ya cigaba da shaƙiyancinsa har ya yi shiru sannan Ammar ya ce idan har ka gama ka sameni a hill&vally.
Waje ne kyakkyawan waje wanda ya tsaru,an ƙawata shi da followers da bishi yu kala kala,ga sanyi da ni ima ta ubangiji,mutane da dama suna zuwa wajenne saboda shaƙatawa,ko kuma hutawa saboda zuciyarka ta samu reliep.
Yana zaune yana ta kallon ruwan da ya ke ta zubowa ta cikin ƙasa,shima wajen an ƙawata shi sosai gwanin ban sha'awa.
Tunani kawai ya ke yi a game da makomar aurensa shi da wannan mummunar yarinyar,sam ba irin kalar Sakinat ya ke buƙata a matsayin matar aurensa ba,gaba ki ɗaya ma dai ya tsani yarinyar sosai,har bai san adadin tsanar da ya yi mata ba.
Yana zaune kiran Amir ya shigo wayarsa ya ɗaga a hankali kamar ba soja mazan fama ba,nasiha mai ratsa jiki Amir ya dinga yi mai a game da auren da mahaifinsa ya yi masa,kada ya bijirewa mahaifansa ya yi abin da suke so wataran zai tsinci haƘurin a gaba.
Tnx kawai ya cewa Amir sannan ya kashe wayarsa saboda tsabar haushi,don shi haryanzu bai yarda zai tsinci wani alkhairi a gurin wannan fush girl ɗinnan ba.
Ammi ma ta rasa mai yasa tunda Mijin na ta ya yi mata albishir da ɗaura auren Sakinat da ɗanta ta tsinci kanta a mai mummunan faɗuwar gaba ta rasa me ya ke yi mata daɗi,ba wai auran ta tsana ba a ah kawai zuciyarta ce bata aminta dashi ba,musamman yadda taga Ammar gaba ki ɗaya ya canza alokaci ɗaya,ta tsani abinda zai ɓata ran Ammar tana yi masa wani irin mugun so da tausayinsa a matsayinta na mahaifiyarsa,Allah kaɗai yasan irin zaman da zasuyi shi da yarinyar,amman koma dai menene tana roƙon Allah ya kawo sauƙinsa cikin ruwan sanyi.
Sannan tana yi masa fatan samun zaman lfy . . ..
"Tunanin me ki ke yi Zulaihat"?.
da sauri Ammi ta cire tagumin da ta yi ta yiwa mijin na ta murmushi don kada ya fuskanci halin da ta ke ciki.
Murmushi ya yi sannan ya ce"Zulaiha na sanki tun kafin ki kai shekarun haka shekararki 14 aka auramin ke alokacin ni kuma ina da kusan talatin kuma ina matsayin soja a wannan lokacin,ki kayi haƙuri ki ka zauna dani a halin da na ke ciki na yaron soja don kowa yasan halin zuciyar soja awannan lokacin harma da yanzu,to me yasa ki ka kasa haƙuri akan wannan auren dana ɗaurawa ɗanki?aƙwai abubuwa da yawa dana duba kafin in haɗa wannan aure ba da ka na yi saba,wannan yarinyar ba tada gata sai Allah akan ɗanmu ta kamu da ciwon zuciya fa?idan ƴarki ce zaki so hakan ya faru da ita?to kinga ba zaki so ba."
Tun daga nan Ammi bata sake haɗe ranta ba kullum cikin yiwa ɗanta nasiha ta ke,tare da addu'ah.
Tafiya ce ta kamasi zuwa bauchi garin aminin Alhaji Muhammad,da ammi za aje amman kuma sai ta ce ta fasa tana da buki,da Khalisat da Sakinat aka yi tafiyar sai Alhaji don shi uban gayyar Ammar yana Abuja.
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un.
Aranar bayan sun tafi kan hanya sukayi hatsari aka nufi dasu asibitin da ke kusa,shi dai Alhaji abin sai addu a,Sakinat da Khalisat kuwa ɗan kukkurjewa ne kawai.
Aka kirawo su Ammi a waya cikin tashin hankali tazo,yadda taga mijinta abin sai addu'a,ta kirawo Ammar tana kuka ta ce yazo ta faɗa masa halin da suke ciki,kai tsaye daga Abuja ya taho hankalinsa a tashe.
Da ƙer Alhaji ya fara magana yana yiwa Ammar nasiha akan Sakinat,kuka kawai Ammar ya ke na ganin halin da mahaifinsa ya ke.
*Miss green ce*
*🌈DARASI!!🌈*
BOOK 1
✨Rabiatu Bashir
Ummu maher(miss green)🍀💚
*@Wattpad link*
https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333?utm_source=android&utm_medium=com.gbwhatsapp&utm_campaign=invitefriends
*@Arewa book link*
https://arewabooks.com/chapter?id=62a48949772e179ad6e54443
*SIRRINKI👂🏻*
Mu yawaita hailala da istigfhari yin hakan zai ƙara kusan tamu da ubangiji.
----------------------------
20/21
Sakinat ce a zaune tana waya da Falmata, kana ganin Sakinat kasan ranta a ɓace ya ke ta ce"Falmata yau watanmu biyar da zuwa wajen bokannan amman har yanzu banji wani chanji ba da zaisa in gane ina da ciki,abin yana damuna Falmata ni dai idan babu hali kawai mu chanja wani bokan kawai ina ganin zaifi ko"?.
shiru Falmata ta yi tana mamakin hali irinna Sakinat don duk bin bokaye irin na Falmata bata ka ma ƙafar Sakinat ba,ko da ya ke Sakinat ta yi mata zarra a fannin kuɗi dole ta fita fitowa gari.
"Eh aƙwai wani boka da na ke tunanin zai iya wannan aikin wanda matuƙar ya yi miki aiki to fa shikkenan,zaki ganki da ciki a jikinki ko da na aljanu ne kuwa".
da sauri Sakinat ta ce"haba Falmata ya zaki ce wai ko da na aljanu ne,idan na samu cikin aljanu ai an samu matsala lafiyayye na ke son haifa".
Ƴar dariya ce ta kusa kufcewa Falmata don tasan duk wannan yawon da suke yi ba lallai ne ta haihu ba,don tun tana budurwa ta gama zubarda abinda tun a waje".
Ƙalubale gareku ƴan mata ku daure ku riƙe mutuncinku domin shi mutunci madara ne,kuma daga inda namiji ya yi amfani da ke ko da ciki bai shiga ba to kin gama cutar kanki,gwara duk rintsi ki daure ki kaiwa oganki(mijinki)budurcinki na ƴa mace,wallahu a 'alam.
Nan dai Sakinat da Falmata suka shirya zuwa har Ghana wajen wani tsohon mushriki don Sakinat ta samu Haihuwa,washe gari da wuri suka ɗauki hanya don ma jirgi zasu shiga sai Accra(Ghana).
Sun sami layi sosai don haka suka jira har layinsu yazo,suna shiga Sakinat ta fara toshe hancinta don wani irin mugun warin da wannan mushrikin bokan ya ke,Falmata ta riƙe hannun Sakinat tana janta don ta daina rufe idon,don idan bokannan ya zuciya zai iya gamaw dasu duka ya shanye musu jini.
Tun kafin su faɗi abinda ya kawosu Bokan ya fara faɗa musu duk abinda suke so ayi musu,ya janyo wani glass yana nuna musu abinda ke ciki.
Wata yarinya suka hango kyakkyawar Bafulata na suka hango yarinyar ba za ta wuce 13zuwa14 ba,cikin tsoro Sakinat ta ce"boka wannan kuma wacece?menene haɗinmu da ita?"
cikin sauri bokannan ya buɗe mushen bakinsa ya ce"ita wannan yarinyar ita ce za ta kawo ƙarshen matsalarki."
Alhmdh.
Anan na kawo ƙarshen book 1,kuma na gama free page idan ka tashi biyan kuɗinka ka neme ni ta wannan number.
07068606171
Ga
Details
*Littafin na kuɗi ne ban yarda ki karanta mun baki biyani ba,Gamai buƙata n cigaban labarin zai biya ₦300 normal* group...Vip group
₦500... Special₦1k....zaku iya Turo da katin MTN ta wannan number 07068606171
ko kuma ku tura ta wannan account number 2212328303
RABIATU BASHIR
Zenith Bank.
0 Comments