💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKI NA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚
*Labarin gaske*✍🏻
Na
*Rabi'atu.B.Abdullahi*
(Ummu Maher)
Miss green💚💚
_BISMILLAHIR_ _RAHMANIR RAHIM_
GABATARWA:dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah(S.W.T)Salati Mara Adadi Zuwa ga Manzon Rahma(S.A.W)
Tsokaci:Wannan littafin Ban rubuta shi don cin mutuncin wani/wata ba duk wanda yayi dai dai da rayuwarshi to yayi hak'uri akasi aka samu,Wannan littafin gaske ne ma'ana ba labari ne k'irk'irarre ba.
Sadaukarwa:Ga dukkanin mosayana Ummu Maher,Mu samman👇👇👇
Nabila dikko
Nabiha Aminu
Ummu Najma
Zahara'u Nasir Aliyu
Amina .m.Baso
duk ina godiya,da dukkanin mutanen da ban ambato su ba to suyi hak'uri.
Abbakar.Ak saraki
da
Ahmad isah Koko
Inq godiya sosai da kulawarku gareni🙏
*Babi na d'aya📝*
Malam!Malam!!Malam!!fito kaga i'kon Allah yarinyar nan ta suma,Malam ya fito da gudu yana kallon yarinyar ya kalli Inna Majaifiyarta yace maza ki d'auki Mumtaz ki ku fito bari in kirawo Alhaji mu tafi asibiti,Sunan yarinyar kenan Mumtaz.
Kafin Malam ya dawo Inna ta kalli k'afar Mumtaz sai taga jini yana malala kamar ruwa da gudu ta fito k'ofar gida tana kiran Malam.
*Wacece Mumtaz*
Mumtaz dai shine asalin sunan ta wanda Mahaifinta ya saka mata saka makon sunan Mahaifiyarshi ne ya saka wa Mumtaz, Asalin Malam Abdullahi Mahaifin Mumtaz y'an jihar Bauchine wanda sun kasance y'an kasuwa ne sosai gidansu suna siyar da kayan masa rufi ta hanyar ne suke samun na cin abinci kuma i'tace hanyar abincin su.
Kwatsam sai karayar Arzik'i ta samu mahaifinsu Malam Wannan abun ba k'aramin tada musu da hankali yayi ba.
dalilin da yasa karayar Arzik'i ta same shi shine Mahaifinsu su Malam Wato Alhaji Jibrin shine yanada wani aboki d'an asalin Maiduguri Alhaji Bukar kusan ma Amininshi shi ne sana'ar Alhaji Bukar shine siyar da dabbobi daga wannan gari zuwa wannan gari.
Kwatsam sai wataran Malam Bukar yakawowa abokinshi Alhaji Jibrin ziyara yaga yadda ya bunk'asa da kasuwancinshi na siyarda kayan masa rufi.
Abun ya tsayawa Alhaji Bukar har yaushe Jibrin zai zama haka a kasuwanci bayan ya fishi tunda ga nan Alhaji bukar ya kafawa abokinshi Jibrin tsana mai tsanani Ya fara bin bokaye don ya raba shi da dukiyarshi,Har yayi nasarar rabashi da komai nashi ya zamo duk abunda ya tab'a sai yayi asararshi tun daga wannan lokacin Alhaji jibrin Mahaifin Abdullahi ya shiga wani mummunan talauci ya zama na koda kayan da zaisa ma sun fara lalacewa sai ya shiga wanka sun bushe sannan ya saka su.
Ana haka wataran Alhaji jibrin ya fita neman tai mako gidan wani mai kud'i kawai sai ya jiyo kukan wata jaririya cikin bolar kusa da k'ofar wani gida kamar zai wuce kuma sai ya dawo ya duba yaga jaririya ce aka yar kyakkyawa da'ita kamar y'ar larabawa ya d'auketa hannunshi yana kakkarwa ya nufo gida,yana zuwa gida ya nunawa matarshi Adama mahaifiyar Abdullahi da yake ita kad'ai ce matarshi kuma Abdullahi shi kad'ai ne D'an ta don haka koda Alhaji jibrin ya kawo mata wannan jaririya ba k'aramin jin dad'i tayi ba sosai don haka ta rik'e yarinyar da hannu bibbiyu.
Abdullahi kuwa duk duniya ya nuna ba shi da wacce ya keso sai Wannan yarinya wacce Alhaji ya saka mata suna Maryam,Tun tana k'arama yake sonta duk abunda ya samo to na k'anwarshi ne Maryam koda ta girma sai abun ya koma soyayya sosai koda iyayen suka gani sunyi murna sosai.
don haka da taimakon y'an uwa da mak'ota aka hahhad'a akayi musu Aure.
Ranar bikinsu ne wani mummu nan labari ya samesu'cewae Mota ta buge Alhaji Jibrin ya mutu Har lahira.
Sunyi kuka sosai da mutuwar mahaifin nasu mai son Su da nuna musu k'auna.
Koda akayi Auren Inna Adama mahaifiyar Abdullahi tace su zauna agidan tunda gidan yana da girmanshi haka kuwa akayi suka zauna agidan.
Ana haka wataran Inna adama ciwon ciki ya kamatq cikin dare ko kafin a kaita asibiti tace ga garunku nan ta mutu har lahira tashin hankali sosai Abdullahi da Matarshi Maryam suka shiga,Ana hakane kuma Maryam ta samu Ciki watanshi biyar ya zube saboda rashin kulawa don har yanzu suna cikin talauci sosai.
Saida Maryam tayi shekara Goma sannan ta haifi Mumtaz wannan shine labarin Mahaifan Mumtaz.
*Ummu Maher ce* Miss green💚
*Vote*
*Share*
And
*Comments*📝
*Tyiping*🖌️
ABOUT MY WORK✍🏻
💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚
*Labarin gaske✍🏻*
Na
*Rabi'atu.B.Abdullahi*
(Ummu Maher)Miss green💚📗
بسم الله الرحمن الرحيم
_________________
______
🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚🖊
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_
🏔🅙︎🅦︎🅐🏔
*BABI NA 2*📝
Malam kazo da sauri Mumtaz tana zubar da jini da sauri "Alhaji yace to Mumtaz d'ince babu lafiya yanzu Malam yake fad'amun bari muyi sauru mu tafi Asibiti kiyi sauri ki fito da'ita.
Umma tayi saurin komawa gida ta fito da Mumtaz suka tafi Asibiti,shan kwanarsu kefa wuya su hancin motarsu Amal ya kawo kai Amal tace Mama kamar Motar Dadyne naga yafita daga gidan kuma naga yana sauri sosai Allah dai yasa lafiya Mama tace to Amin.
Amal da zumud'inta ta nufo gidansu Mumtaz tana son ta nuna mata kayan da ta suyo akasuwa sai taga gidan Arufe an saka kwad'o ta ce Afili to yau kuma ina su Umma suka tafi dukkansu Allah dai yasa lafiya tayi saurin komawa gida don gayawa Mamanta.
Likitan tace Alhaji munyi iya k'ok'arinmu don ganin cikin jikinta ya tsira Amman hakan ya faskara sakamakon maganin zubarda ciki da tasha.
Malam da Alhaji harda Umman Mumtaz saida abun ya tab'asu sosai sakamakon jin wai Mumtaz ce take da ciki ne da'ita to waye yayi mata cikin? suka had'a baki wajen fad'ar hakan likitan kuwa har tayi tafiyarta ta barsu anan sunata sambatu su kad'ai.
Banko k'ofar da'akayi ne yasa Mumtaz bud'e idonta da k'er don jin yadda sukayi mata nauyi sosai kamar ba jikinta idon yake ba.
Umma tace Wallahi Mumtaz kin cuceni yanzu daman cikine dake kika d'aukomun abun kunya kinsan kuwa abunda kika Aika ta,yanzu duk i'rin tarbiyyar da muka baki abanza saida kika zubar mana da mutunci yanzu sai ki fad'amun waye yayi miki ciki,eyeh dake nake kike kallona munafuka,Kuka na shigayi ina cewa Wallahi Umma ban zubar muku da tarbiyyar da kuka bani,k'addarace tafad'amun Umma ta k'ara sha k'o Mumtaz tana tambayar cikin d'aga murya wanda duk wanda ke kusa zai iya jin ta.
Su Alhaji ne da Malam mahaifin Mumtaz suka shigo cikin d'akin saboda yadda suka jiyo hayaniya cikin d'akin,Alhaji yace haba Umma kiyi hak'uri ki k'eleta tayi mana bayani da kanta,Umma ta saki Mumtaz tana haki tare da hararar Mumtaz.
Alhaji yace Mumtaz ki fad'i tsakani da Allah Muntaz ki fad'a mana waye yayu miki ciki,domin idan kika b'oye mana Allah yana sama yana kallan ki don haka ki fad'ama na kinji.
Mumtaz ta share hawayen da ya b'ata mata fuska tace hak'ik'a zan gaya muku gaskiya,Alhaji yace to Mumtaz muna jinki?Muntax tayi shiru tabbas tana son gayawa i'yayenta gaskiya Amman tana tsoron Abubda zaije ya dawo domin tasan Iyayenta baza su tab'a i'ya jayayya da iyayen wanda yayi mata wannan Aika Aikar ba saboda nesa ba kusa ba sunfi duj yadda kake tunani kud'ine dasu kamar Bankin CBN saboda suna da kud'in da ko shugaban k'ada bazai had'a k'afa dasu ba,koda Kuwa Alhaji ne Mahaifin Aminiyarta Amal.
don haka sai tayi k'arya dacewa,Don Allah Umma ku ya feni hak'ik'a wadannan mutanen da suka saceni wata biyu da ya wuce har nayi tsawon wata biyu agidansu sune suka yimun wannan Aika Aikar mu biyarne y'an mata kuma duk saida suka lala ta mu.
Alhaji yace to meyasa Mumtaz baki gaya mana ba don mu d'auki mata ki kinga yanzu gashi sun sakaki cikin wani hali muma sun saka mu tabbas biri yayi kama da mutun tabbas nasan Mumtaz ba mazina ciya ce ba bazata tab'a Aikata abunda kuke zarginta dashi ba.
Malam ya shard'e wata zufa da ta tasomai yace hak'ik'a nafi kowa sanin halin Mumtaz yarinyace kamila maijin tausayin iyayenta akoda yaushe gata da Addini,hak'ik'a mungodewa Allah da yasa cikin ma ya zube saidai muce Allah ya bata lafiya dukkansu suka Amsa da Amin.
*Asalin labarin rayuwar Mumtaz da kuma abunda ya shafi rayuwarta dan gane da cikin da akayi mata*
★★ ★★
Tunda Muntaz ta taso da wayonta taga iyayenta suna cikin wani matsanancin talauci sosai,hakan yasa ta taso da jin tausayin iyayenta duk abunda tasan zata tai maka musu dashi tanayi indai baifi k'arfinta ba akan Aikin gida tun tana k'arama take Aikin gidansu,sannan Mahaifinta yana faskare dashi suke ci suke sha don haka duk ranarda Mumtaz taga Mahaifinta ya tashi zai tafi Aikin faskare sai ta tashi tace nima Malam zan bika,don gaskiya bazan iya bari kana shan wahala ba jibi yadda fa hannunka yake duk ya farfashe,Sai Malam yayi dariya yace Mumtaz kenan kinga duk aikinnan da nakeyi don ke da mahaifiyarki ne don hakk'inku yana kaina kuma sannan inason insakaki makaranta kiyi karatu kinji,sai Mumtaz ta wangale kyakkyawan bakinta tace Malam nidai i na girma inason inzama irin matar nan da kullum kake jinta aradion ka wadda take shiri nima inason inzama mai Aiki a gidan Radio don in taima ka muku da jama'ah baki d'aya.
Malam kuwa inda sabo ya saba don kusan kullum sai sunyi wannan hirar da y'arshi tilo aduniya wato Mumtaz ya lura yarinyar ta taso da wani ginshik'i azuciyarta wanda ta keso ta cika burinta akanshi Ma'ana tana son ta zama ma'aikaciyar gidan Radio ma'ana y'ar jarida don haka duk ranarda wannan zancen sai yaji yanason ya cika mata burinta,don haka sai yace Mata babu komai Mumtaz Insha'Allah zaki cika burinki na zama y'ar jarida don ni zan tabbatar miki da kin cika burinki don Insha'Allah zan sakaki makarantq don kema ki amfana da karatu kinji.
Suna wannan abun Kullum Umma sai ta lab'e tana jinsu cike da sha'awar y'arta da mijinta Allah ya sani suna son su bunk'asa rayuwar yarinyar wajen sakata makaranta don ta Amfana Amnan ya zamar musu dole wajen cikawa Mumtaz burinta bunk'asa karatunta har ta zama y'ar jarida kamar yadda kullum take muradi.
To fah wasa farin girki don yanzu wannan labarin ya soma kubiyoni don jin tarihin Mumtaz kachokan.
*Ummu Maher ce*
*Vote*
*Share*
And
*Comments*✍🏻
*Tyiping*🖌️
ABOUT MY WORK✍🏻
💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚
*Labarin gaske✍🏻*
Na
*Rabi'atu. B.Abdullahi*
(Ummu Maher)
Miss green💚📗
بسم الله الرحمن الرحيم
_________________
______
🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚🖊
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_
🏔🅙︎🅦︎🅐🏔
*BABI NA 3&4*📝
Mumtaz ta taso da wata irin baiwa wadda take bawa kowa mamaki saboda yarinyar akwai gaskiya bata tab'a yin abu ta nuna rashin gaskiya kosa zaka kashe ta sai ta fad'i gaskiyar lamari,Ana haka Malam ya samu Aikin nik'a ya nayi albashinshi na farko ya saka Mumtaz makaranta da shi Mumtaz kuwa ta ringa murna saboda mahaifin nata ya cika mata burin ta nayin karatu,Kullum Malam i'dan zai tafi wajen nik'ansa tare suke tafiya da Mumtaz ya sauketa amakaran ta ya siya mata biskit da alawa sannan ya tafi wajen Aiki yana mata Bye bye i'tama Mumtaz bata tafiya sai taga Mahaifin nata ya tafi sannan take shiga aji.
Karatu sosai Mumtaz ta keyi don bata wasa a makaranta sam,ga ta bata surutu a'aji kawai i'ta karatu ta saka a'gabanta.
makarantar Mumtaz tayi nisa gashi Allah ya taimaki Malam yana biya mata kud'in makarantar ta akan kari baya bari lokaci ya k'ure bai biya ba kuma yana jin dad'in yadda take karatunta tana mayar da hankali,Mumtaz duk cikin ajinsu babu wanda ya kaita k'ok'ari da mayar da hankali wajen karatu gata da k'ok'ari don duk term ita take zuwa na d'aya ko Na biyu A'ajinsu haka duk Malam man makarantar sun san cewa Muntaz tana da baiwa sosai gata tun tana k'aramarta akwai ta da hankali da hangen nesa.
Mumtaz tana dawowa daga makaranta ta ajje jakarta ta cire unifoam d'inta na makaranta ta fito tsakar gida don taya Umman ta Aiki,ta gumin da taga Umman ta tayine tace Umma lafiya me yafaru kike ta gumi me akayi miki?ta jerowa Umman tata tambayoyi lokaci d'aya,Umman tata tayi saurin cire ta gumin da tayi tace Mumtaz kin dawo ne?Eh Umma na dawo Amman meya faru naga kin rik'e kunkuminki?Umma tace Mumtaz nasan kina jin yunwa ko?Eh Umma inajin yunwa sosai me kika dafa,Umma tace Mumtaz babu abunda na dafa shiyyasa ki kaga nayu tagumi kuma na buga na buga ban samu ba,Mumtaz tace to Kuma Umma shine kika saka kanki cikin damuwa ki daina damuwa kinji,Indai na girma na samu Aiki zaki huta indunga siyo miki kayan dad'i,Umma tayi murmushin da yafi kuka ciwo tace to Mumtaz Allah dai ya cika miki wannan burin naki,Mumtaz tace Amin Ummana.
Umma tace yanzu ki tashi akwai wata y'ar sauran kamu da na dama miki da kwad'on k'anzo ki tashi kici kinji Umman ta kalleni tana mai jin tausayin d'iyar tata.
Akwana atashi asarar mao rai wataran asamu aci wataran kuwa Iyalan Malam mahaifin Mumtaz basa cin abun abinci wataran haka suke kwana abunsu,gashi Allah ya basu yarinya mai hankali da tausayi ko ta samu ko kar ta samu bata tab'a d'agawa iyayenta hankali wai don tana jin yunwa ko wani abu haka take hakura taci koda bai mata ba haka ta ke hak'ura taci.
Har Allah ya kawo lokacin da su Mumtaz suka zana jarrabawar fita daga primary Mumtaz da iyayenta sunyi murna sosai gashi ta fito da saka mako mai kyau.
Mumtaz tace Malam ina Addu'ah Allah ya cika mun burina na zama y'ar jarida sai dai bansan aikin da zanyi ba in taimaka muku ba kuna shan wahala kaida Umma,wajen biya mun buk'atu na,Malam yace babu komai uwata Allah zai taima kamana matuk'ar ba muyi bacci ba muna rok'on Allah ya kawo Aikin da zai zi mun na sakaki makarantar gaba da Primary kinji ki daina da muwa,Mumtaz tace to Baba na Allah ya tai ma keka yacr Amin uwata.
•••••••••••••••••
Ranka ya dad'e har yanzu Mu'taz d'in bau kira ka ba Allah dai yasa lafiya mai martaba inajin tsoro kada wani abu ya samu yarima,Mai martaba yace gaba Fulani babu abunda zai sameshi kinsan yace i'dan ya dawo baya buk'atar muje d'aukoshi motar haya zai shiga kinsan halinshi don haka kada ki damu,Fulani tace haba Mai martaba yanzu haka zamu zubamai idanu gamu da motocin agidanmu wasu ma saidai mu bayar Anma d'anmu yana shiga motae haya so yakeyi duniya ta zagemu ace mun kasa kula da d'an cikinmu ballanta na Al'umma gaskiya nidai banasan wannan halin nashi Ai ba sai yayi haka ne duniya zata san cewa shi mai tausayi ne ba.
Fulani bata gama rufe bakin ta ba,Jakadiya tayi iso k'ofar d'akin tace gafaranki dai Yarima yana neman i'so,Fulani tace anyi mai iso ya shigo Yana shigowa ya gaida mai martaba da mahaifiyarshi Fulani,tace ikon Allah kaidai yarima kaji tsoron Allah wallahi duk yawan motocin gidannan kace wai kai bazaka hau ba sai motar haya zaka hau wannan wacce irin rayuwa ce haka.
*UMMU MAHER CE*
Please share
And
Comments✍🏻
*Tyiping*🖌️
ABOUT MY WORK✍🏻
💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚
*Labarin gaske*✍🏻
Na
*Rabi'atu.B.Abdullahi*
(Ummu Maher)
Miss green💚📗
بسم الله الرحمن الرحيم
_________________
______
🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚🖊
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_
🏔🅙︎🅦︎🅐🏔
*WATTPAD LINK*
https://www.wattpad.com/?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends.
__________________👉🏻👉🏻
*BABI NA 5&6📝*
Nan Fa Fulani ta dage tanawa Mu'taz fad'a akan me zai dinga hawa motar haya,Mu'taz dariya ma Mahaifiyar tashi ta bashi Ya kama kunnenshi yace Allah yabawa Fulani hak'uri Allah yaja da ranki Uwargida Awajen Mai marta ba takawarki lafiya,Ai bai gama Rufe bakinshi ba Mai martaba Sarki Mahaifin Mu'taz ya k'elk'ele da dariya yace kaimu son i'rin wannan kirari haka nida kwanannan Zan k'ara Aure in Auro Baturiya Mai jan bakii,A'i Fulani k'ara har zuk'a tayi tana cewa daman Kai da d'an ka haka kuke da anfara magana sai kuyi sauri Ku Fara wayan cewa,Kai kuma da amfara magana sai kace zaka Auro baturiya ka Auro Agwa ma.
Dariya Mu'taz yayi shida Mahaifinshi Mu'taz yace haba a kwai wata baturiya da ta Kai Fulani wani Abu ai babu shi ya fad'a yana dariya,Fulani tace kwaji da shi dai.
Oyoyo Bros Wata y'ar budurwa ce da baza ta wuce Sha shida ba ta rungume Yayan Nata tana yimai sannu da zuwa cikin so da kulawa na y'an uwan taka.
Da ka ganta kasan k'anwar Mu'taz ce saboda yadda sukayi matuk'ar Kama da juna,Oyoyo My sister shima ya fad'a Mata yana Mai Jan hancin ta.
Bros ya naji kuna tsokanar My mom d'ita,Hanan Ashe kinji i'rin tsokanar da suke yimun KO?Hanan ta rungume Fulani tana cewa K'elesu My mom zamu rama,har wata baturiya ce za'ah had'a ta da my Mom d'ita Tauraruwar Mata kyakkyawa acikin kyawawa.
Fulani tace yauwa gaya musu dai suji?Hanan ta fakaici idon Fulani suka tuntsire da dariya i'tada yayan nata.
Fulani tace waifa akan na fad'a mishi gaskiya akan hawa motar hayar da yake yi shine Mahaifinku ya goyi Bayan shi,Hanan tace gaskiya My Bros kadaina hawa motar haya don Allah.
Mu'taz yace to Fulani kiyi hak'uri na daina,Fulani tace yau d'ana haka nakeso shiyyasa kullum nake k'ara sonka saboda kanajin magana ta.
Sarki Abubakar wato Mahaifin Yarima Mu'taz yayi dariya yace mu kuma da ba'ah sonmu sai ajefar damu ko?kuma tunda abun haka ne kwanannan Baturiyar nan zata shigo tunda abun haka ne.
Fulani tayi dariya tace Hhhh Mai Marta ba kenan Ai kaga y'ay'annan nawa sun isheni duniya da lahira don haka ba Baturiya ba ka Auro Balarabiya.
Mai martaba yayi dariya tare da cewa Hhhh Fulani kenan kishi KO?to naga ne miki kwantar da hankalinki Akwai wata mace da zata kaiki ai babu ita,Ai kuwa yaran nasu suka tun tsire da dariya .
Nandai suka ci suka sha suna maijin dad'in dawowar d'an nasu daga America,Bayan sun gama ne Mu'taz ya d'auki wayar shi ya kirawo Amininshi kuma d'an uwanshi Murat.
Kiran farko Murat ya d'auka yana jin muryar Abokin nashi ya ture Mima daga kusa dashi don yadda ta mak'alk'aleshi sai kace wata mayya ta kalli Murat cikin takaici daga zuwanta gidan za'ah Fara wulak'antata.
don Mima irin mutannan nan ne masu son Kansu matuk'a shiyyasa take mafarkin ace Murat ya zama Nata i'ta kad'ai,saboda yadda Murat yayi Mata yanzu ya tabbatar Mata da cewa Wanda ya bugo yanada wani bugire tare da wani matsayi arayuwar Murat.
Murat shine kasan Na dawo KO kazo mugaisa shine kak'i zuwa KO?Murat ya Sosa kanshi yana cewa Haba Life kayi hak'uri wallahi wani Uziri ne ya b'oye ni Amman yanzu ganinan zuwa ya fad'i hakan yana Mai kashe wayar ya nufi inda Mima take wacce ta gwalalo idanuwa tare da bud'e kunnuwa taji me'ake fad'a.
Ganin Murat yayi hanyar ban d'aki abun ya k'ara k'ular da Mima yau me Murat yake nufi da'ita daga zuwan ta saiya nemi wulak'anta ta,koda ya fito daga ban d'aki kud'i ya watsawa Mima Wanda baisan KO nawa bane.
Ba tare da ya kalleta ba yace inkin gama ki rufemun gida bai jira me zata ce ba yayi tafiyarshi tana ta masifa tare da nadamar zuwa don ba haka bokanta yace Zai faru yace Mata matuk'ar ta kwanta da Murat to komai yazama Nata domin Murat zai dinga binta kamar wani doki da akala.
Hira ce ta kaure sosai don tsakanin Murat da Abokin nashi kuma Amininshi Murat kuwa wani Abu ne acikin zuciyarshi a game da Aminin Nashi yana rok'on Allah ya nuna mishi Ranar da zaiyi maganin shi ranarda zai cika burinshi akanshi Ni kuwa Nace KO wani buri ne Murat yake b'oyewa oho?.
Hanan ce ta fito sanye cikin Doguwar wato Arabian gown gaban rigar yasha ado gata farar fata fatarnan Tasha jan lalle Wanda zaka rantse da shi aka haifeta dashi, Murat ya bita da I do kamar maye.
tana zuwa tayiwa kanta mazauni akusa da yayan Nata,ta kalli Murat ba tare da sakin fuska ba kamar yadda ta taho tace Ina wuni tana wani yauk'i kamar ba tason yin magana.
Murat ya shafa kanshi yanajin son yarinyar har Cikin zuciyarshi don duk wulak'amcin da Hanan take yimai bai tab'a nuna Mata ba saboda tun tana k'arama yake sonta.
K'anwa ta KO Nayi miki laifine kike kame mun fuska Murat ya fad'i hakan lokacin da ya d'auko tufa ya saka abakinshi yana jin dad'in tufar har Ranshi,Hanan tayi saurin cewa Wallahi babu abunda yake damuna kawai dai Kaina ne yake ciwo,cikin tashin hankali yace Hanan kinsha magani kuwa,Hanan ta tashi tana tafiya tana cewa Eh nasha yanzu ba tareda ta sake magana ba ta fita daga farlon don kwata kwata yanzu batason Murat tun Ranar da ya nemata da wata buk'ata ta tsaneshi ba kuma wai tsanarshi tayi ba A'ah kawai dai abun da yayi Mata ne ya saka gaba d'aya yanzun bata son ganin shi,har a zuciyarta tanason Murat sosai Amman yariga da ya b'ata rawarshi da tsalle.
Mu'taz ya kalli k'anwar tashi Bayan ta fita sannan ya kalli Aminin nashi yaga gaba d'aya hankalinshi yana kan k'anwar shi Hanan,KO meye ya shiga tsakanin su Oho?.
Shidai A'iya saninshi yasan cewa Murat da Hanan suna matuk'ar son junansu to meye ya faru,to KO Hanan ta gano Aminin nashi yana Neman matan banza Oho?A kullum Addu'ah ya keyiwa Abokin nashi na Neman tsari daga halinda Murat ya fad'a.
Mu'taz yace Murat ka k'eleta zata sakko kasan Mata kaidai Ka cigaba da Jan hankalinta asannu komai zaizo da sauk'i sai Abu na gaba da Zan gaya maka Murat kayi k'ok'ari kadaina kula matan banzan nan kasani Allah bata bacci kuma yana kallon ka don haka ka kiyaye dokokin ubangiji sai shima ya kiyaye ka daga fad'awa azabarsa.
Murat yaji haushin maganar Abokin nashi don haka ba tare da ya nuna mai ba aka cigaba da hira Inda Murat ya nuna wa Aminin nashi ya daina duk wani hali na banza.
★★★★★
Mumtaz kiyi sauri fa mutafi makaranta kinsan fa yau Malamin nan zaizo kinsan ba shida mutunci KO kad'an Amal ta fad'i hakan tana Mai shiga d'akin don ganin Aminiyar tata bata da niyyar fitowa,Wow wata yarinya a hango wacce ba zata wuce sha biyar ba tana shafa Mai A fatarta Mai kyau da tsantsi,Mumtaz kenan yadda mak'erin budurci ya k'erata komai Nata yayi kyau masha'Allah.
Mumtaz tace daman sauri na ke tayi kafun ki fito nasan kina zuwa zaki addabe ni shiyyasa nake ta sauri,Au haka zakice KO inji Amal dake shirin fita.
Mumtaz tayi saurin janyo ta tana bata hak'uri,Amal tace to sai kiyi sauri idan ba haka ba intafi,Nandai Mumtaz ta gama shiryawar ta suka fito don zuwa makaranta inda sukayi wa Umman Mumtaz sallama suka tafi ganin sha'awa.
*Wacece Amal*
Amal dai y'ar wani mutuncr Mai kud'i d'an Asalin jihar Kano ne matar sa y'ar Niger ce Buzuwa ce Jamal su biyu ne ita da Yayan ta Mai suna Ibrahim,Mahaifinsu Alhaji Abdullahi sun dawo Bauchi da A'iki ne saboda transfer da'akayi mishi saboda haka suka dawo Bauchi da zama,Alhaji Abdullahi bata son zama cikin masu kud'i wato bata son zaman G.R.A.saboda yace baka sanin halin da talakawa suke Cikin zama cikinsu kuma zai k'ara maka I'mani tare da tausayi da jin k'ai don haka koda ya su da mak'ofta suke da su Mumtaz don haka tunda ya bud'e i'do yaga halin da suke ciki Saiya ringa taima ka musu ya bud'ewa Malam shago a Bayan gidansu yana siyarda kayan masa rufi,Mumtaz kuwa tuni sunyi saboda Mai k'arfi tsakanin ta da Amal,hakan da Alhaji ya ganine koda za'ah saka Amal Makarantar gaba da Primary wato Secondary tare yakaisu yayi musu komai tare.
*UMMU MAHER CE*
Miss green💚📗✍🏻
Share👉🏻👉🏻👉🏻
And
*Comments*
*Tyiping*🖌️
ABOUT MY WORK✍🏻
💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚
*Labarin gaske✍🏻*
*Na*
*Rabi'atu.B.Abdullahi*
(Ummu Maher)Miss green💚📗
بسم الله الرحمن الرحيم
_________________
______
🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚🖊
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_
🏔🅙︎🅦︎🅐🏔
*WATTPAD Link*
https://www.wattpad.com/?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends.
____________👉🏻👉🏻👉🏻
*BABI NA 7&8📝*
Wannan dalilin ne yasa Mumtaz da Amal suka taso tare komai suke yi hatta abinci tare suke cinshi,suna son Junansu sosai da sosai.
hatta bacci wani lokacin tare sukeyi,I'dan safiya tayi Mumtaz ta koma gida duk ranar da basu kwana tare ba kuwa to Da sassafe zasu had'u don har mafarkin junansu sukeyi.
Mumtaz bata da tsoro ko kad'an,Amal kuwa akwai ta da tsoro don y'an gidansu ma sun santa da tsoro kamar farar kura.
Koda fad'a Akeyi da Amal to ka tabbata sai Mumtaz ta shiga ciki anyi da'ita saboda i'ta daman tun tana k'arama bata da tsoro ko kad'an hakan ne yasa yara suke tsoron Mumtaz.
Hajiya Mahaifiyar Amal bata san Wannan alak'ar tsakanin Mumtaz da Amal,A cewar ta wai Mumtaz zata shafawa Amal gayyar talauci,Shiyyasa take ta k'ok'arin rabasu ta k'arfi da yaji.
Saidai duk wannan abun da takeyi bai saka yaran sun daina son junansu ba,Gashi kullum Ibrahim Yayan Amal ya dawo daga wajen Aiki sai ya tambayi Mumtaz I'dan kuwa bai ganta ba to sai yaje gidan.
Hakanne yake k'ara tunzura Hajiya Wato mahaifiyar Amal,don gani takeyi duk Mumtaz ta kwace mata iyalai,don Alhaji Yanzu taimakon su Mumtaz yakeyi sosai.
Hajiya fa ta dage sai ta raba,Amal da Mumtaz iyakar k'arfin ta,don wataran ma Idan Mumtaz tazo gidan korar ta takeyi ko kuma tayi ta zagin iyayenta wai matalauta matsiya ta.
Zagi dai kala kala babu wanda Mumtaz bata shanshi awajen Hajiya,abun takaicin kuwa i'dan Mahaifin Amal yana nan bata nunawa Mumtaz wani abu ballantana ma har wani ya gane meke faruwa.
ko kud'in makaranta idan Alhaji ya bawa Mumtaz fakar idon Alhaji a keyi ta karb'e,Idan Amal tayi mata magana yanzu ta zane ta wannan abun ya tsayawa Amal aranta don tsakani da Allah bata jin dad'in yadda Mahaifiyar tata takeyiwa Aminiyarta.
Don haka rannan ta shiryawa Uwar tata tsiya ta d'au aniyar sai ta gayawa Dadynta don du abunda mahaifiyar tata ta keyi bai sani ba.
Rannan suna Zaune dukkansu Afarlo har Mumtaz,sai kuwa Amal ta kar kace bakinta tace Dady zanfad'a maka wata magana,Dady ya gyara zamanshi yace to Uwata ina jinki wani abune ya faru?.
Eh Dady daman nadad'e inason in fad'a maka akan abunda Momi ta keyiwa Mumtaz ne?Ai kuwa sai Momi tace to Uwar y'an sharri kedai kamar canza mun ke akayi mai bak'in hali kawai,kuma kirufa mana bakinki anan Noncense kawai.
Alhaji yace haba Hajiya ki tsaya mana yarinyar ta fad'i gaskiyar ta Tafara magana kin tsayar da'ita meye dalilinki?to banason i'dan ina magana da yara na kina saka mana baki kina jina ko?.
Momi kuwa abunnan ya k'ona mata rai ta kasa cewa komai sai zuciyarta da take mata zafi,Ita kuwa Mumtaz batason Amal ta fad'awa Dadynta wannan maganar don zai i'ya haddasa musu rigima k'arshe a dawo da abun kanta.
Alhaji yace ina jin ki Mamana me Mamanki ta keyiwa Mumtaz yanzu in d'auki mataki akanta,sai kuwa Amal tace Dady wallahi Mama kullum idan Mumtaz tazo nangidan saita zageta wai y'ar matsiya ta y'ar talakawa,Wallahi Dady wataran ma idan ka bamu kud'in skull karb'e na Mumtaz, ta keyi wataran ma ta hanata shigowa gidannan wai ita bata gaji Arzik'e ba.
Alhaji fa ranshi idan yayi dubu to yab'aci don me Hajiya zata dunga wannan jahilcin I'ta ta manta a yadda ya Aure ta take Mahaifin ta Saran icce yakeyi Amman bai talaucinsu ba ya Aureta amman yanzu har tana da bakin zagin y'ay'an mutane.
Kwala mata kira Alhaji yayi koda tazo yaci mata mutunci sosai yace kuma duk ranar da ta sake yiwa Muntaz wani abu to Wallahi bai yafe mata ba,Hajiya kamar ta shak'e y'ar tata saboda haushi.
Nandai taringa bashi hak'uri amman ko sauraron ta baiyi ba yayi tafiyarsh,yana mai jin haushin matar tashi don ko kusa bai kawo abunda ke faruwa zai faru ba.
Ibrahim ya kalli Mahaifiyar tasu yace Gaskiya Hajiya wannan halin bai dace ba kwata kwata,don Allah yayi mutun cikin talauci ba yana nufin baya sonshi ba,A,ah sai don Allah yagwada imanin mutun amman bai kamata mutane suna k'ok'arin nunawa ubangiji izza ba.
Hajiya tace yumun shiru sallamammmu kawai sunje sun tsaface ku dukkanku bakwa ganin laifinsu,kullum yabonsu kukeyi mutanenda talauci gadonsu ne abarsu suyi abunsu mana amman wai taimakonsu sukeyi.
toni bana cikin wad'anda aka sallama,don haka ni bana cikin wadanda aka sallama.
kuti hakuri nqyi tyiping kad'an wani uzuri ne ya rik'eni.
*UMMU MAHER CE*
*Share*
And
*Comments*
*Tyiping*🖌️
_ABOUT MY WORK_✍🏻
💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚
By Rabi'atu.B.Abdullahi👉🏻
(Ummu Maher)Miss green💚📗
بسم الله الرحمن الرحيم
_________________
______
🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚🖊
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_
🏔🅙︎🅦︎🅐🏔
*BABI NA 9&10*📝
Ibahim yayi shiru yana sauraron Hajiya da gaba ki d'aya i'don ta ya rufe da masifa wai yanzu an asirceshi ya zama d'an hannu.
Ibrahim ya kalli Mahaifiyar tasu yace haba Hajiya Mumtaz fa yarinya ce mai hankali da tarbiyya bata damu da dukiya ba kwata kwata haka ma i'yayen ta mutanen kirki ne.
Hajiya tace yimun shiru mara kunya harni zaka kalla kace mun iyayenta mutanen kirki ne,to waye ba na kirki ba?tambayar ka na keyi kabani amsa mana?.
Amal tayi saurin cewa kiyi hak'uri Hajiya don Allah kidaina zagin Mumtaz a gaban ta babu dad'i i'rin wannan gaskiya Momi...tun kafun ta k'arasa ta wanke ta da mari tana masifa kamar wata zautatta.
Ke dan ubanki dani kike ko da ubanki?I'na cewa yanzu kika had'ani da ubanki wai na zagi Mumtaz k'anwar uwarki ko?to bari kiji wallahi tallahi ba don yau ke y'ata ce ta cikina ba yau da kinga i'skanci muraran.
Don haka this is the last worning idan kika k'ara kai k'arata wajen ubanku saina naka saki banza mara sanin ciwon kanta.
Duk abunda Momi tayi Mumtaz na kallon ta kuma tana jinta amman ba tace komai ba,saboda yadda ta d'auki Momi kamar mahaifiyar ta don haka Mumtaz ta tashi ta koma gidansu ba tare da tace komai ba.
Amal tabi k'awar tata da kallon tausayi don tasan Duk wanda aka yiwa wannan zagin to tabbas sai yaji aranshi babu dad'i,don zagine na cin mutunci duk mai hankali idan aka yi mishi wannan zagin sai yaji a zuciyarshi babu dad'i.
to haka dai rayuwa ta dinga tafiya har kawo i'yanzu da Mumtaz da Amal suke makarantar gaba da primary wanda Alhaji Mahaifin Amal shine ya d'auki ragamar karatunsu.
*Cigaban labarin*
Mu'taz ya kira Murat yafi sau goma amman bai d'aga ba, Cen aka d'auki wayar Mu'taz yayi saurin cewa haba abokina me yasa baka d'aga waya akan kari?.
Muryar wata yarinya yaji tana cewa to A'i saika k'ara kira mai wayar baya kusa,ta d'an d'aga murya kad'an tace Honey ana kiranka awaya.
Mu'taz kuwa don haushi bai jira abunda zaice ba,ya kashe wayar saboda haushin Murat ya keji sosai ba don Murat Amininshi neba da tuni ya rabu da shi yayi yadda yakeso tunda rayuwar daya zab'arwa kanshi kenan.
Ya rasa gane kan Murat da i'rin halinshi nasiha dai i'ya gwargwado yayiwa Aminin nashi amman haryanzu bai daina tsallake 2 nashi ba.
Kullum shine d'aukar Babys amota suna yawo shine gidan Club babu wanda baya zuwa yana sha shanci da k'arawa kai zunubi.
K'arar wayarshi ce yasa ya juya ya duba Life💘ya gani ajiki,sunanda suke kiran junansu dashi kenan don tun suna k'anana shida Murat suke kiran junansu dashi saboda yadda suka shak'u sosai da juna bacci ma tare sukeyi.
Murat yace Mu'taz don Allah kayi hak'uri Na d'an shiga Band'aki ne so shiyyasa,Mu'taz yace babu komai naji,Amman Murat meyasa kullum kake tuba kake koma wa ruwa ya kamata kayi k'ok'ari kadaina bin matannan ba Kai kad'ai bama duk wani Mai bin Mata k'arshen shi na dama.
Murat yayi wani gauron numfashi sannan yace Babu komai Wallahi wannan d'in ma akasi aka samu,Mu'taz yace babu komai Amman dai kayi k'ok'ari ka daina.
Duk abunda suke yi Hanan tana jinsu awayar ta samu waje ta zauna zuciyar ta nayi Mata k'una,tabbas zuciyarta tana son kasan cewa da Murat a matsayin miji.
Amman ya zamar Mata dole ta Rabu dashi tun yanzu gudun samun matsala,Amman ta Yaya zata rabu dashi don tana matuk'ar son Murat.
*UMMU MAHER CE*
*Vote*
*Share*
*Comments*✍🏻
*Tyiping🖌️*
ABOUT MY WORK✍🏻
💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚
Written by
Rabiatu.B.Abdullahi🤙🏻
(Ummu Maher)Miss green💚📗
بسم الله الرحمن الرحيم
_________________
______
🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚🖊
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_
🏔🅙︎🅦︎🅐🏔
BABI NA 11&12📝
Hanan ta kalli Yayan ta Muta'z"Tace Bros meyasa haryanzu Murat bazai daina wannan halin nashi nason mata ba?Kullum sai yace ya daina amman gobe sai ya koma.
Wallahi Bros yanzu kaf duniya babu mutumin da na tsana i'rin Murat kwata kwata shi baisan mutuncin Alk'awari ba.
to Wallahi bros badon kaiba da tabbas sai nayiwa Murat wulak'ancin da harya mutu bazai manta dani ba,saboda na lura ma badon komai yake sonka ba saidon kud'inka shiyyasa yake sonka don ya cuceka.
Hanan!Hanan!!Hanan!!!ki bud'e kunnuwanki kijini kada ki sake zagin aminina kuma d'an uwana a gabana don yace yana sonki bawai yana nufin ki ta gayamai maganar da tayi miki bane don haka ya rage naki ki soshi ko karki soshi don haka ki b'acemun da gani nonsense kawai Muta'z yayi mata wata tsawa da gudun gaske ta fita daga d'akin tana kuka Kai cin rai.
Tana fita Kai tsaye d'akin ta tanufa tana wani i'rin kuka mai cin rai,haryanzu d'an uwan ta yakasa gane halin Murat Sam don Murat mutum ne mail wayo DA son abun duniya don shi Murat irin mutananne masu k'emar mutane musamman ma talakawa don i'dan yaga talaka tamkar yaga wani Abu mummuna.
Bayan haka kuma gashi DA son mata don duk inda yaga mace musamman ma y'ar bariki i'donshi yana kanta don shi haka Allah yayi shi DA masifaffen son y'an Mata.
Lallai ya zamar Mata dole ta samarwa kanta mafita DA yayanta Mutaz don gudun fad'awa halin Azzalumin mutum i'rin Murat Mara imani.
*Mumtaz*
ta kalli Umma mahaifiyar ta tace haba Umma wannan matakin DA kika d'auka bai dace ba saboda Mahaifiyar Amal bata mutunta d'an Adam KO kad'an.
Amman yanzu kice zaki fara Aiki agidan don Allah kiyi hak'uri Umma mu tsira DA mutuncin mu please,Umma ta dafa y'arta tace Mumtaz kiyi hak'uri kada kidamu DA yadda take wulak'anta mutane saboda ko badon komai ba saboda zaman nan da nakeyi haka bbu wani neman nakai babu dad'i saboda koda Mahaifinki yana yi dole nima inyi.
tunda ba komai zamuce yayi mana ba,Nace amman Umma kinsan halin matarnan kuma kikeso kiyi aiki agidanta ina laifi ma kije wani gidan tunda kin matsa dole sai kinyi aikin.
Umma tace Mumtaz matarnan fa dakan ta tazo gidannan tace i'dan babu damuwa tanason inringa A'iki agidan ta amman idan hakan ya b'atamun rai inyi hak'uri.
Mumtaz tace yanzu Umma wannan matar ce tace zaki ringa yi mata A'iki tana biyanki yanzu tayiwa Dady adalci kenan gaskiya Umma kada kiyi Aikin nan don Allah saboda bata da mutunci ko kad'an.
Umma tace kai Mumtaz yaushe kika zama haka mai manta Alkhairi Arayuwarki yanzu duk abunda matarnan take miki saikin zageta tunda kika fara zaginta bance miki komai ba shine kika samu bakin cin mutuncin ta haka.
to bari kiji nayi shawara dake ne saboda ina ganin ko babu komai ke y'ata ce kuma kina da hakk'i akaina kamar yadda nima nake da nawa hakk'in akanki amman ba don haka ba da saidai kiji nafara A'iki na, wawiya kawai Umma tayi wani tsaki mai k'arfi tayi wucewar ta abun ta.
Mumtaz tabi bayan Umman nata da kallo tabbas batason wacece mahaifiyar Amal ba shiyyasa,domin duk k'iyayyar da take yiwa Mumtaz bata yimata gaban Umma shiyyasa, saidai ma agaban Umman ta ringa nunawa tafi ta son Mumtaz d'in.
Tana cikin wannan tunanin taji sallamar mahaifinta da sauri taje ta'amshi kayan hannunshi tayi mishi sannu da zuwa.
tana kai kayan ta dawo zata wuce Mahaifin nata yace Mama na zo mana,Nace to Baba nadawo nazauna ina jiran abunda zaice don nasan tunda ya ganni acikin damuwa saiya tambayeni abunda ya sakani damuwar.
Yace Mamana meya faru?ko bayan fitata wani abu ya faru waye ya tab'amun Mamana ta kaina?shiru nayi babu amsa don bansan ma abunda zance mai ba don tabbas mahaifina baisan cewa Mamana Zata fara A'ikatau gidansu Amal ba yanzu kuma matuk'ar nafad'a mishi to tabbas kashi na ya bushe don tabbas mamana cewa zatayi nice na fad'awa Abba na.
don haka na k'irk'iro k'arya ta nace Baba na d'an zazzab'ine yake damuna shiyyasa amman yanzu yayi sauk'i.
Baba yace to kuma shine baki fad'awa mahaifiyar taki halin da kike ciki ba saiki zauna da ciwo?Nace ai Baba yanzu ya fara yimun shiyyasa ban gayawa Umma ba.
Umma dai tana kusa da Babana batace mana cikanku ba hasalima tashi tayi ta fara k'ok'arin d'aura tuwon dare,Baba na yace to bari inci abinci sai in kaiki chemist d'in Tasi'u.
Ai da sauri nace A'ah Baba wallahi kabarshi ma naji sauk'i Wallahi,Baba yace ayi haka Mamana ai gwara abaki magani ko kada kuma yadawo miki,Nace wallahi ya daina yanzu Baba.
Yace to shikkenan Mama na,Umma kuwa kallo na tayi tace Hmmm dama kindaina k'aryar ciwo don kada na gasken yazo don i'don na gasken yazo baza kiji dad'i ba.
Baba Yace haba ke kuwa kinsan Mamana bata k'arya ballan tanama k'aryar ciwo kema A'i sheda ce ko?don Mamana bata k'arya sam.
Umma tace yaudai tayi maka don yanzu na shiga d'aki kafun infito wai har kanta yafara ciwo saboda i'ta ta i'ya k'arya mai lasisi,Baba na yace kai haba ya zakice haka naga Allah yakan kawo wa mutum ciwo yanzu anjima kuma ya sauwak'e mai.
Ko kuma yanzu yana numfashi anjima ya daina don haka ni yanzi na yarda da ciwon Mamana don nasan ba halin ta bane k'arya.
Baba na yace zo Mamana nasiyo miki wani abu mai kyau🌻dasauri na kalli Babana da shima ni yake kallo,na fad'ad'a fara'ata don ganin me yasiyomun.
Hijabi ne mai kyau da sandal na makaranta mai kyau sai sabulun wanka mai kyau harda man shafawa,godiya na ringa yiwa Mahaifina ina maijin k'ara sonshi har zuciya ta.
**********
Murat yace abokina duka duka kwananka nawa da dawowa zakace zaka koma k'asar waje Ai yakamata kad'an dad'e saidai i'dan bakason ganinmu to shine Murat ya fad'i hakan yana mai b'ata fuskarshi kamar da gaske.
Muta'z ya dafa Aminin nashi yace kayi hak'uri life A'iki nane yake buk'atata awanannan lokacin shiyyasa saboda Ina matuk'ar alfahari da Aikina saboda nasamu alfanu sosai dashi.
Kaga ayanzu inada asibitina mai zaman kanshi ak'alla yakai biyar ayanzu haka a k'asashen waje,so shiyyasa kaga nakeso inga nakoma don cigaba da Aikina.
Tunda Muta'z yafara magana kallonshi kawai Murat yakeyi gaskiya indai hakane yanada A'iki babba agabanshi saboda yadda abokin nashi ya bunk'asa haka.
Ace kanada Asibiti har 5 outside country lallai kuwa bak'aramun kud'ine da aminin nashi ba kuma bai tab'a gaya mishi cewa asibitinshi ya kai har biyar ba sai yau.
to kodai ya gane manufarshi akanshi ne?to indai kuwa hakane dole ya canza takunshi don yazamar masa dole yaga ya cimma nasara akan Aminin nashi.
Don Allah ina baku hak'uri abisa rashin jina kwana biyu da bakuyi ba saboda ina Exam ne shiyyasa,ku tayamu da Addu'ah please nasamun nasarar cin jarabawar.🤲🏻
*Ummu Maher ce*✍🏻
(Miss green)💚
*Tyiping🖌️*
ABOUT MY WORK✍🏻
💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚
NA
*RABI'ATU.B.ABDULLAHI*
(Ummu Maher)Miss green💚📗
بسم الله الرحمن الرحيم
da sunan Allah mai rahama mai jin k'ai
_________________
______
🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚🖊
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_
🏔🅙︎🅦︎🅐🏔
BABI NA 13&14📝
_________Murat ya dawo daga tunani da yakeyi don gudun kada Aminin nashi ya gano halin da yake ciki,yace to Aminina Allah yadawo dakai lafiya Allah ya k'ara Arzik'i kuma ina godiya da i'rin Alherin da kake turomun Allah yasaka da Alheri.
Azuciyarshi kuwa cewa ya keyi wannan d'an kud'in da yake turomun ko Mima ta cinyesu shine yake wani iyayi waishi gashi mai kud'i,insha Allah na kusa cika burina akanka don huta da bak'incikin da kake d'oramun.
Hanan tana fitowa ta kalli Murat ta watsar dashi batare da tace mai komai ba tayi tsaki tayi wucewarta eajen yayanta suka cigaba da hirarsu shi kuma Murat ya fita yana maijin haushin abunda Hanan take yimai saboda tasan yana sonta shiyyasa take yimai kowani i'rin tashin mutunci,kuma insha Allah saina Aureki don tabbatar da Akina ya tafi daidai batare da wani ko wata sun gane ba.
************
Washe gari da safe Mumtaz ta shirya don biyawa k'awarta makaranta Amal saidai abunda ta ganine yayi mugun razana ta,ta k'arasa wajen Dadynsu Amal da yafito ta gaisheshi inda ta kalli Maigadi yana zuba musu kayansu a boot d'in motar ga Amal ma tafito i'tada Hajiyar ta daman Yaya Ibrahim yayi tafiya tun watan jiya.
Mumtaz tace Dady tafiya zakuyi ne bamu saniba kuma?sai kuwa Hajiya tace yauwa sannu uwar Alhaji da i'dan zamuyi tafiya sai mun gaya miki uwar kinibibi kawai,to transfer akayi mishi zuwa Legos zamu koma cen idan kuma zaki hanamu ne to bismillah tayi wucewarta ta shiga mota abinta.
Amal ta dafani tace Mumtaz ban tab'a sabo da wani mahaluk'i ba kamar yadda nasaba dake ba kuma inajin dad'in zama daku saidai hakan bazai yiyuwa jiya daddare aka turowa Abbanmu cewa anyi mishi transfer zuwa Legos, sai ta fashe da kuka ta rungumeni tana kuka kamar ranta zai fita.
Nima dakaina ban tab'a tunanin sabon da mukayi yakai haka ba saboda son Amal ajinina yake don ko bacci ne kawai yake rabamu shima Hajiya ce ke hanani kwana tare da Amal saboda masifar ta.
Muka rungume junanmu kamar baza mu saki junanmu ba,Dadynsu Amal yace Mumtaz kuyi hak'uri babu yadda zamuyi don nima banason rabuwa da Malam don nasaba dashi sosai Amman babu yadda zanyi Aiki nane haka daga wannan haka daga wannan jihar sai wannan.
Share hawaye na nayi nace to Dady Allah ya kaiku lafiya Allah yahad'a fuskokinmu da Alkhairi ina fad'in haka na fito da gudun gaske na shiga gidanmu alokacin Umma tana yanke farcen ta.
Umma tace ke Mumtaz kedawa ye da kika shigo gida kamar wadda tayi gamo da Aljani?dai dai lokacin Malam ya shigo yana fad'awa Umma cewa su Alhaji motarsu ta tashi yanzu za'ah kaisu tashar jirgi zasu koma Legos.
Umma tace Legos kuma Malam Allah sarki kai amman kuwa munyi rashin makwab ta nagari kai amman banji dad'i,Malam yace ya barmun shagon da nake ciki halak malak wai inyi ta sana'ah acikinshi Sannan ya biyawa Mumtaz kud'in jarrabawar da zasuyi ta fita daga Secondary sannan yabani jari na dubu Hamsin.
Umma tace Allah sarki Alhaji Allah shima ya bashi masu yimishi Allah kuma ya tsareshi da sharrin mak'iya Malam yace Amin dai don i'rin Alhaji acikin mutane k'alilan ne kam.
Bayan Sati 1
Rayuwa nakeyi ayanzu mara dad'i don nasaba sosai da Amal don Amal mutun ce mai kirki da mutun ta mutane don duk yadda Mahaifiyarta taso ta rabamu Allah baiyi ba k'arshe ta saka mana ido.
Umma tace haba Mumtaz wai haryanzu baki daina tunanin Amal ba tatafi sai watarana idon da rabon ku had'u da'ita ammsn kidaina sakawa kanki damuwa har tazo tayi miki illa.
na kalli Umma nayi dogon numfashi sannan nace Umma nasaba da Amal sosai don Amal mutuniyar kirki ce inajin dad'in zama da'ita sosai amman tashi d'aya ace wai munrabu, saina fashe da kuka Nan dai Umma tayi ta lallashi na har Allah yasa nayi shiru.
Bayan wasu watanni Mumtaz na hango sanye cikin after dress tayi mata kyau sosai tayi rolling d'in gashin ta abun gwani sha'awa hannyen ta sunsha lalle ja abun kamar kad'au keta tazama taka.
Mumtaz!Mumtaz!!Mumtaz!!!kira najiyo har sau uku ta bayana wanda na tabbatar da nasan mai muryar amman naman ta inda nasan ta,Hanan ce cikin ran tsattsiyar mutar ta sai k'elli takeyi kamar ka d'auke ta.
Da sauri na k'araso ina cewa to yau Hanan ce agarin to yaya gidan,Hanan tace normal amman saidai nazo wajen Amal akace sun tashi ina suka koma?nace Allah sarki sun tashi yanzu haka suna Legos anyiwa Abban ta transfer.
Hanan tace oky Ai babu komai naji dad'i ma da muka had'u dake don idan naganki kamar naga Amal ne,nayi dariya nace Allah sarki Hanan yanzu duk matsayinku agarinnan kike zuwa unguwar nan tamu ta talakawa duk da dai wajen k'awarki kika zo kada fa ki manta Mahaifinki shine Sarki fa.
Hanan tayi dariya tace Mumtaz kenan Ai don munada kud'i bawai yana nufin muna k'in talakawa bane,i'dan kika ga mutum yana k'in talakawa to gaskiya bashi da imani da tausayi,Kuma kinga ni da kike ganina a Mota ta nazo to Broz d'ina amotar haya yake yawo idan ya shigo Nigeria.
Abun ma dariyawa ya bani don tunda nake ban tab'a jin ance wani yarima ya hau motar haya ba sai akanshi,Hanan tace kin ganni ko bayanan bai yarda wani ya kaini unguwa ba ko kuma da karu su biyo ni ba,wai saboda mudaina d'aukar kanmu wani abu ba .
Nace gaskiya kunada mutunci da mutunta mutane don wasu masu matsayin basa i'ya shigowa cikin talakawa don basu da halak'a mai kyau dasu shiyyasa wasu da sun fito sai kiga ana jifan su,Amman ku kam kunada son mutane da son talakawa.
Hanan tayo dariya sannan tace shiyyasa yau nayi basaja nasaka nik'ab da kikazo kusa dani na bud'e don kiga fuska ta,saboda da mutane sun ganni yanzu zakiga Ancika wajen nan saidai a karb'eni da k'er,Nayi dariya nace au kuwa gaskiya ne kam don mutane suna sonku.
Hanan tace mu shiga gidan mu ta gaida Umma ta don basu tab'a gaisawa ba,Nace to nan nayi mata jagora zuwa gidan mu amman azuciya ta har kunya nakeji don kada taga gidanmu amman dana tuna cewa gidan ubanane ba gidan haya ba kuma ko akan kashi muke zaune zan nuna gidanmu donni ko a makaranta bana nuna cewa ni y'ar gidan wasu ce duk da daka ganni zaka d'auka cewa mud'in masu kud'ine saboda hallitar da Allah yayimun kamar y'ar shugaban k'asa.
Muna shiga gidan na hango Ummana tana tuk'a tuwo,Hanan tayi Sallama Umma na ta jiyo muka k'arasa Hanan ta gaishe ta,Sannan na d'aukowa Hanan kujera ta zauna suna k'ara gaisawa.
Nace Umma kinsan wacece wannan kuwa?Umma tace A'ah bansan ta wacece?Nace Umma wannan gimbiya Hanzn kenan y'ar gidan sarki,Umma ta rik'e baki tana cewa oh Allah yau manyan mutanane agidan namu sannunki y'annan ya mutanen gidan?Hanan da tunda muka shigo gidan take ta kallon Ummana ko k'ifta idanu babu.
Tace Umma lafiya klau duk suna gaisheku daman nazo wajen Hanan ne k'awata ce amman a Chart muka had'u da'ita har tazama kusan aminiyata so shiyyasa har muka saba to nazo sau d'aya kafun su tashi muka gaisa.
Umma tace Allah sarki sai kuma kikaji sun tashi?Hanan tace wallahi kuwa Umma kuma naga baya hawa online kwata kwata kuma wayarta ma bata shiga shine nace ko lfy bari inzo inji?sai kuma akace mun sun tashi.
Umma tace wallahi kuwa y'arnan sun tashi amman Allah yasa lafiya dai wayarta bata shiga? Muka had'a baki wajen cewa Amin ya Rabbi.
Hanan tace Umma tunda muka shigo naga kina mun kama da Mahaifina mai marta ba?Umma tayi dariya tace ke y'annan mai marta ba dai saidai kama Umma ta fad'i hakan tana dariya.
Idan kunda d'a Comment sai zan k'ara tyiping.
*More Comments*✍🏻
*More tyiping*✍🏻
*Ummu Maher ce*
*Tyiping*🖌️
ABOUT MY WORK✍🏻
💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚
*NA*
*RABI'ATU.B.ABDULLAHI*
(Ummu Maher)Miss green💚📗
BABI NA 15&16📝
Hanan tace Allah Umma kinyi kama sosai da mai martaba sosai wallahi,don ni da naganki ba kiji yadda gabana yake fad'uwa ba wallahi don tunda nake ban tab'a ganin i'rin wannan kamar ba don ko mu da muke y'ay'anshi ba muyi kama da shi haka ba.
Dariya Umma ta kuma yi a karo na biyu don i'ta abunma dariya ya bata,tace Hanan kenan a'i ita kama haka take ba kiji ance babu wanda akayi kamanninshi shi kad'ai illa Manzon Allah(S.A.W)to bayan shi kuwa gaskiya ko wacce kama da y'sr uwarta,Amman nasha ganin mutanan da suke yi n kama sosai don wani ma in baki sani ba sai kice y'sn uwan juna ne.
Nan dai sukayi ta hira a junansu gwanin sha'awa daga k'arshe Hanan tayiwa Umma kyautar kud'i masu yawa Umma tayi ta godiya sannan na rako ta k'ofar gida ta hau motarta,ni kuma na koma gida ina jin dad'in yadda muka sha hira nida Hanan sai na tsinci kaina a mai tunanin Amal don bata bari na in zauna ni kad'ai ma ballan tana har inyi tunanin wani abu.
***************
A yau ne sakama kon jarrabarwamu ya fito na Waec&Neco don haka nayi saurin zuwa in dubo saka makona Alhmdh na ringa fad'i don jarrabawa ta tayi kyau sosai,Ina cikin murna na dawo gida don sanar da Umma cewa naci jarrabawa har nayi hanyar gida sai kuma na tuno da Malam wato mahaifina don in kai mishi yaga sakamakon jarrabawar don zan i'ya cewa Malam yafi Umma damuwa da karatuna.
Da murna ta na i'sa shagon ina zuwa na fad'a tare da Sallama alokacin yana gyara kaya akan trader d'inshi,ya juyo yace Mamana har kin dawo daga dubo jarrabawar?Nace eh Malam na dubo kuma sakamakona yayi kyau sosai,Malam yace Alhmdh Allah yayi miki Albarka Mamana kuma Allah yasa Albarka acikin A'ikin ki.
Nace Amin Malam nima ina godiya da ka sakani makaranta har nazamo yadda na zama yanzun Allah yasaka maka da Alkhairi yabarmu tare,Malam yace Amin amman fa ba nikad'aine nasha wahala wajen biyan kud'in makarantar kiba harda Alhaji Don shima ya taka gudummawa Arayuwarmu baki d'aya saidai muci gaba da yimishi Addu'ah ta samun nasara arayuwa.
Amin Malam kullum sai nayi tunaninsu ko wani hali suke ciki gashi ko number d'insu bamu dashi ballan tana in kirawo inji muryarsu,Malam yace A'i jiya yasaka wani ya kawomin wayarshi wai ya kawomun mugaisa.
Nace kai Malam shine baka kirawo niba mungaisa,Malam yace to A'i kinga wayar ba tawa bace shiyyasa amman yanzu zan sai waya sai mudinga gaisawa nace to shikkenan hakan ma yayi.
**************
Meema tace Murat kasan Allah bazaka ringa raina mun wayo ba kana cemun wai Har yanzu baka gama target d'in ba,abunda muka tsara shine kafun yayi wannan tafiyar tashi zamu A'ika ta komai don yana da kyau ace yanzu kasan inda yake maka ciwo ya mayar dakai kamar wani oganka sai abunda yace ka keyi wai shi gashi mai kud'i.
Murat yayi murmushi sannan yace Meema kenan kinsan nafiki hankali da kuma ilimi sannan na fiki Zak'uwa akan abunda zan A'ikata amman yana da kyau ace kasan yadda zaka tafiyar da tsarin A'ikin ka kinga kuwa dole saidai mubi a sannu har Allah ya cika mana burinmu.
Meema tace Hmm nifa kasan Allah Muta'z d'innan mugun haushi yake bani taurin kanshi da kuma jiji da kanshi yayi yawa,shifa ko kallon mata ba yayi ballan tana ma har ayi tunanin wani abu,nasha d'ana mai tarko ina tura masa mata gidanshi wai don suja hankalinshi amman duk abanza babu wani abu da ya cigaba.
Murat yayi dariya i'rin tasu mugaye yace Hmm A'i kuwa zaki dad'e kina ai kawa Muta'z karuwai don shifa yadda kika san ba Namiji ba haka Allah yayi shi kwata kwata baya koda sha'awar y'an mata ballan tana har asamu abunda akeso ta wannan hanyar.
Meema tayi dariya sannan ta tashi ta bud'e fridge ta d'auko wani swan mai sanyi ta kora shi sannan ta d'aukoshi a hannun ta tana tafiya tana yanga kamar zata fad'i don i'ta Meema i'rin matan nanne sirara k'ugun ta kamar zata karye saboda sirantar tata har tayi yawa.
Murat kuwa tuni ya kwalalo mata manyan eyes d'inshi yana kallon Meema dasu donshi Gaba d'aya idan yana ganin Meema baya i'ya komai saidai duk yadda yake jin ta aranshi bata kai Hanan ba don Hanan ji yake indai bai Aureta ba komai zai i'ya faruwa.
Baisan sanda Meema ta zauna ba sai jin muryarta yayi tana cewa Murat ka kwantar da hankalinka kaji Insha Allah Akwai wata hanya da zanbi wajen naga ba ruguza rayuwar Muta'z amman ba yanzu zan gaya maka ba don nasan halinku na maza sai kayi amfani dani wajen biyan buk'atarka daga ka gama kuma ka jefar dani kan titi inda ka kwaso ni😏.
Murat yayi dariya yace haba haba Meema ni na'isa in wulak'anta ki i'dan na wulak'anta ki in zauna dawa ki tuna fa duk abuna bazan tab'a mantawa dake ba don kinfimun duk sauran mata na duniyar nan.
Nanfa Meema taji dad'in wasa ta da Murat yayi taci gaba da shararomai zance tare da siyeshi da abubuwa kala kala i'rin nasu na y'an bariki shi kuma ya sakar maya hannun Aljihu ta d'ibi yadda take son kwasa.
*Wa nene Murat*
Murat dai shine asalin sunanshi wanda i'yayenshi suka saka mai,Mahaifinshi yakasance d'an asalin jihar Kano a unguwar Rijiyar lemo, Sunanshi ee'ro magini wanda babu inda baya zuwa acikin Nigeria don yin A'ikin gini kwararre ne sosai yayi Aurenshi da matarshi mai suna Maryam i'tama y'ar asalin jihar kano ce Unguwarsu d'aya da i'ta.
Sun dad'e Allah bai basu haihuwa ba saida sukayi shekara Goma da y'an watanni sannan ta haifi d'an ta Namiji suka saka mai suna Murat,Suna son Murat sosai.
Tashi d'aya Malam ya koma Bauchi don akwai wata ma'aikata ta masu gini don haka ya tattara iyalanshi suka tafi Bauchi,Kwanansu Hud'u da zuwa Bauchi aka kirawo ee'ro Aikin gini agidan sarauta Yaji dad'in Aikin sosai don ko babu komai yasan zasu samu kud'i sosai don haka yayi sallama da matarshi ya tafi.
Abu da ajali suna cikin Aiki bulo ya fad'o masa atake kuma rai yayi halinshi,don haka aka kai gawarshi hidanshi don a sallaceshi,Matarshi Maryam tayi kuka sosai kamar ranta zai fita alokacin Murat yana d'an shekara bakwai 7 amman duk da haka saida yagane mahaifinshi ya rasu.
Watan ee'ro biyu da rasuwa Maryam ma tabi mijin ta i'tama Allah yayi mata rasuwa,Shikkenan Murat ya dawo maraya babu uwa babu uba,don haka Aka kaishi gidan sarkidon a nemo y'sn uwan i'yayenshi.
Kwananshi hud'u da zuwa gidan sarki Sukayi sabo sosai da Muta'z wanda yakasance d'a tilo da sarki donko bacci Tare su keyi da Murat.
*Ummu Maher ce*✍🏻
Vote
share
And
Comments✍🏻💌📩
*Tyiping*🖌️
ABOUT MY WORK✍🏻
💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚
*NA*
*RABI'ATU.B.ABDULLAHI*
(Ummu Maher)Miss Green💚📗
بسم الله الرحمن الرحيم
_________________
______
🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚🖊
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa _
🏔🅙︎🅦︎🅐🏔
*BABI NA 17&18📝*
_____🖌️ Hakan da mai marta ya ganine ya sa yafi fita Murat sosai sonda yake yiwa d'an shi Mutaz sai ya shafi Murat saboda haka aka saka Murat makaranta i'ri d'aya da ta Muta'z, Hatta kaya tare ake musu komai dai i'ri d'aya sai suka zamo kamar y'an biyu.
Tunda Murat ya taso yaga son da I'yayen Muta'z suke yimai da yadda suke narkar mai da dukiya sai abun ya tsaya masa aranshi yake jin cewa kamar son DA suke nuna mai na k'arya ne Saboda gaba d'aya yaga i'rin dukiyar da suke nar karwa akan d'an nasu.
Don haka Murat ya rik'e cewa tabbas sai yaga bayan Muta'z sai dai ya rasa ta inda zai Fara A'ikata b'ar narsa,Har Allah ya kawo lokacin DA suka shiga jami'ah alokacin ne kuma rayuwar Murat ta k'ara samun ta waya,Saboda gaba ki d'aya Murat ya canza hali,ya kuma canza abokai musamman ma da yaga acikin turawa yake,A'ikuwa Ana cikin haka ya had'u da d'an wani attajiri a makarantar nan danan suka k'ullah abokan taka dashi ya Fara koya masa harkar bin Mata,Muta'z kuwa koda ya gane abunda Murat ya keyi ba k'aramun tashin hankali ya shiga ba saboda aduniya banda i'yayenshi da k'anwarshi babu mutumin da yake so irin Murat yake kuma fatan rayuwarshi tayi kyau sai gashi ya b'ata rayuwarshi tun kafun aje ko'ina.
Har kullum Muta'z fad'a yake yiwa abokinshi akan yaji tsoron Allah Amman sai ya nuna mishi cewa ya fishi tsoron Allah don haka Muta'z ya cigaba da yiwa abokinshi addu'ah akan Allah ya shirye shirin addinin islama🙏🏻.
Koda lokacin exam yazo Murat baiyi wani abun azzik'i ba don saka makonshi baiyi kyau ba Sam,Muta'z kuwa saka makonshi yayi kyau sosai da sosai,saidai daga lokacin da ya duba na Murat sai Murna ta koma ciki don ganin irin saka makon da abokin nashi ya samu.
Mai martaba yaji haushi sosai don duk abunda Murat ya keyi babu Wanda bai sani ba,saboda akwai masu kula da duk wani motsinsu sai dai su d'in basu sani ba don ya nemi kada su sani.
Allah ya taimaki Muta'z ya samu A'iki da gaggawa,shi kuwa Murat babu abun Arzik'i don haka Mai martaba ya d'aukeshi manager a company d'insu Amman lokaci d'aya Murat ya lalata Company ya zama gaba ki d'aya babu wani abu mai tsada cikin Company.
Hakan ne yasa Muta'z ya bud'ewa Murat Company na kanshi Wanda zai dun ga juya kud'inshi da kanshi I'dan ma ya cinye ruwanshi tunda Allah ya gani yayi mishi abunda yake ganin ya dace.
*Cigaban Labari*
Wani i'hu Mumtaz tayi tare da tsalle sai gata a tsakar gida,Umma tace ke Mumtaz wai meye yake damunki kina wani i'hu kamar zaki fasa mun Kai,Mumtaz tace Umma yanzu naji a radio Ana cewa Ana Neman masu son gurbi a jami'ah kuma harda ni acikin wad'an da aka suka samu gurbi a jami'ar.
Umma dariya ta Fara yi tana cewa Allah mun gode maka da ka amsa Addu'ar mu Allah ya taimaka,Allah ya baku sa'ah baki d'aya Allah ya sa i'dan kunyi karatun nan Allah yasa ku taimaki junanku Amin ya Rabbi.
Muna cikin murnar mu sai ga Mahaifina ya shigo shima ya ta yamu Murna sosai,Da daddare yace inzo muje kasuwa dashi,Bayan munje ya siyo min hija bai sun Kai biyar da ta kalmi da dogayen riguna masu kyau da kamala.
*Washe gari*
"Umma tace Kai Y'annan kinga yadda kika yi kyau kuwa cikin kayannan kinyi kyau sosai Wallahi,Dariya nayi lokacin da nake saka hijabina da yasha guga k'alk'al dashi gwanin ban sha'awa,simple make_up nayi ban shafa wani Jan baki ba hoda na shafa da lipstick na saka kwalli fuska ta tayi fayau nayi kyau gwanin ban sha'awa.
Rayuwar makaranta rayuwa ce mai dad'i kuma rayuwa ce mai sauk'i Amman idan ka d'au keta da sauk'i kuma idan baka nuna Kai d'an wani bane zaka zauna lafiya DA kowa,mutane da dama suna d'auka ta y'ar mai kud'i ceni saboda yadda lau nina yake,Nidai farace niba doguwa ba niba gajeriya ba ma'ana tsaka-tsaki.
I'na da dogon hanci Wanda ya k'aya ta fuska ta,ga d'an baki na k'arami mai kyau da tsari idanuna manyana masu wani i'rin launi mai kyau gwanin sha'awa,Hmm kyau da tsari saidai Wanda yaga Mumtaz.
Samari kuwa ta ko'ina zuwa suke wai suna sona Don takai i'dan naje makaranta bana fita daga class saboda yawan da samari suka yimun,A lokacin da nafara zuwa Makaranta na had'u da wata k'awata mai suna Zainab Bashir,Zainab mutuniyar kirki ce sosai don tana da d'abi'u masu kyau gata DA k'ok'ari sosai shiyyasa komai tare muke yi a cikin aji sai muka zamo abun sha'awa agun kowanni d'an ajinmu dama wad'an da ba y'an ajinmu ba .
Mun k'ulla k'awance mai k'arfi da Zainab,alokaci k'an k'ani y'an gidanmu suka Santa nima y'an gidansu suka sanni don kuwa watarana DA k'er muke rabuwa.
**********
Akwana a tashi asarar mai rai a yanzu muna lavel 3 inda muka k'ara dagewa a game da karatunmu na y'an jarida wato Mass Com,Allah yana bamu sa'ah a cikin karatunmu,Saidai ayanzu babu abunda yake da muna sai talaucin DA muke ciki nida i'yaye na.
Daman shagon da Baban su Amal ya bawa Babana shagon haya ne kuma asannu y'an unguwa suka karya mishi jarinshi da bashi don tsaba gen mugunta duk kud'in mutum sai kaji yace a bashi bashi toda i'rin wannan ne fa suka karyawa BABA na jari.
Shi kuma Mahaifina yana kunyar ya bugawa Alhaji waya ya sanar dashi halin da yake ciki,Saboda haka yaja bakinshi yayi shiru kuma ayanzu ya Fara Neman A'ikin da ya dace dashi Amman har yanzu Allah bai kawo ba.
Watarana ma haka nake tafiya makaranta ba tare da naci komai ba,Zainab kuwa kullum sai tazo da abinci makaranta duk saboda ni saboda tasan ni ba ma'abociyar cin abincin makaranta bace saboda haka take zuwa da abinci.
Duk itama Zainab ba kud'ine dasu ba Amman sun fimu rufin Asiri tunda Mahaifin ta yana A'ikin gwam nati sannan kuma yana da makarantar Islamiyya ta kanshi saboda haka yake samun kud'in da zai biyawa y'ay'anshi dukkanin buk'atunsu na yau da kullum.
Duk yadda Zainab za tayi Dani akan inci abincin da nazo dashi bana ci,don duk yadda muke dakai matuk'ar ba abincin mahaifiyata bane bana cinshi duk da d'inshi kuwa.
***********
Mai babban d'aki i'tace Mahaifiyar Mai martaba kyakkyawar tsohuwa mai farar Aniya,kamar kullum Muta'z da k'anwarshi sunzo gaishe da mai babban d'aki wacce suke Kira da Hajja,bayan sun gaishe ta suka zauna suna tsokanarta wai ta fiya cin goro gashi bakinta ya duk yayi ja.
Hajja kuwa tana jinsu ba tare da tace komai ba tayi dariya don ta shirya Rama i'ya shegen da suke yi mata,don haka ta kishin gid'a da filo Sannan ta k'ara gutsirar goronta ya bada k'araras sannan tace.
Hmm Ni kuwa Hanan i'na Saurayinki kuma yayanki Murat i'na yake?kwana biyu ban ganshi ba kada dai ace haryanzu bai daina rashin d'a Arshi ba?.
Sosa kai Hanan ta farayi tana cewa wallahi tsohu warnan matuk'ar mutum yazo wajen ki sai kin nemi b'ata mishi rai,yanzu meye laifinmu don munce kina cin goro A'i lafiyarki ake kare miki.
Hajja tayi dariya sannan ta kalli Muta'z tace Hmm wallahi Muta'z na kusa in gayawa ubanka ya nemo maka Mata kowa ya huta so kake kazama tuzuru agida KO to wallahi da Meemi Zan had'aka y'ar wajen Hajara wallahi kuwa kaji narantse daman irinku take so kyawawa.
Tuni Muta'z ya gimtse fuskarshi don yasan halin tsohuwarnan yanzu ta had'ashi da mai martaba,don duk abunda tace shi yake yi baya tab'a tsallake maganar Mahaifiyarshi Hajja.
Cikin Fushi Muta'z ya tashi zai fita don baya son hirar tasu tayi nisa don in akwai abunda ya tsana bai wuce zamcen Aure yanzu ba don babu yadda zai yi da Hajja ne shiyyasa,Karo yaci da wani Abu kamar mutum don haka ya d'ago kanshi don ganin waye?Meemi ya gani taci uban make-up tayi kamar y'ar tsana daman gata kamar zata karye,tsaki Muta'z yayi wuce warshi ba tare daya kalle ta,don haka Meemi ta juya tare DA cewa zaka sani yanzu Zan had'a maka muna finci kawai saita Fara kuka ta shiga wajen Hajja.
*Ummu Maher ce*
*Tyiping🖌️*
ABOUT MY WORK📚
💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
_*AKAN A'IKINA 2021*_
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚
*NA*
*RABI'ATU.B.ABDULLAHI*
(Ummu Maher)Miss green💚📗
بسم الله الرحمن الرحيم
_________________
______
🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚🖊
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa _
🏔🅙︎🅦︎🅐🏔
*BABI NA 19&20*📝
Hajja tace"Meemi me ya faru kike kuka gayamun Wanda ya bugeki yanzu in sab'a mishi?,Sai kuwa Meemy tace"Wallahi Hajja Yaya Muta'z ne ya ringa rankwashi na har saida wajen yayi ja saboda wai na biyo hanyar daya bi.
Hajja kuwa tace"Ni nasan daman wannan yaron yana da mugunta don kawai kinzo gidansu saiya nemi ya dinga takura miki toko ubanshi bai isa ya hanaki zuwa gidannan ba,ballan tana shi d'an yau.
Meemy kuwa da ta b'oye a bayan Hajja ta fito tana yiwa Muta'z gwalo alamun ta samu nasara,Muta'z "yace Haba Hajja wanman yarinyar muna fukace babu abunda ta iya sai dai ta ringa had'amu fad'a dake,Sai kuwa Hannan ma "tace wallahi Hajja kinfi son Meemi damu i'ta ko fad'a bakya yimata amman mu kullum cikin yimana fad'a kike ko kunyar Mai martaba bakyayi.
Hajja "tace inyee wato ma inji kunyar ubanku ko saboda shine ubana to ba ranji kunyar ba y'ar mara kunya,kuma Aure babu fashi indai ina raye Meemi Muta'z zata Aura ko yana so ko baya son hakan.
Cikin fushi Muta'z ya tashi ya fita,Hajja tayi kwafa tace kaji dashi dai Aure babu fashi,d'an nema kawai Hannan ma "tace Nifa Hajja kidaina had'ani da Murat saboda wallahi ni bana sonshi kwata kwata kinfi kowa sanin mugayen halayenshi amman kike cewa wai shi zan Aura to wallahi da in Aureshi gwara in mutu banyi Aure ba,tana fad'in hakan ta tashi ta fita tana maijin haushin kakar tata da take had'a ta da fasik'i mai neman mata tabbas tasan tana son Murat saboda babu macen da zaice Yana sonta tak'i amince mai saboda yana da kyau kud'i ga iya magana ga iya soyayya sai dai ba shida hali ko kad'an.
*MUMTAZ*
Mumtaz"tace wallahi Baba sun ce idan ban kawo da wuri ba zasu rufe Exam din da zamuyi yanzu itace ta k'arshe kuma zuwa jibi duk wanda bai kawo ba bazai zana Jarrabawar ba.
Mahaifina"yace babu komai uwata zan nemo kud'in yau Insha Allah kada ki damu Insha Allah sai burinki ya cika na zama y'ar jarida.
Dariya nayi "nace Allah ya amsa Baba,Mahaifina da Umma suka had'a bakinsu wajen cewa Amin Allah ya amsa,Tunda Babana ya fita tun safe sai yamma ya dawo yana cen yana ne marmin kud'in da zan samu shiga jarrabawa.
Umma ta kalle ni taga nayi ta gumi," tace haba Muta'z babu kyau ta gumi fa,Insha Allah Malam zai samo kud'innan kidaina damun kanki da tunani kinji"Nace to Umma...Ban gama rufe ba kina ba mukaga Malam ya shigo da sallamarsa muka amsa mishi,koda ba'ah gaya maka ba kasan babu nasara afitar da Malam yayi duk farar fatar Malam saida ta nuna alamun yasha wahala.
da sauri na tashi na d'au komai abincinshi da ruwan wanke hannu,ya kalle ni yace sannu Mamana Allah ubangiji yayi miki albarka nace Amin Baba.
Yace Mamana wallahi ban samu kud'innan ba andai samu rabi da k'er shima faskare nayi mai yawan gaske to anan nema na samu rabona,kuka na fashe dashi na tausayin Mahaifina hanna yenshi sunyi jajir abunka da farar fata,Malam yace haba Mumtaz kidaina kuka mana ko idan kika kai musu baza su amshi rabin bane?.
Da sauri na goge hawayena nace zasu amsa Baba amman don Allah kadaina wannan faskaren akaina jibi fa yadda hannayen ka fa sukayi jajir,Malam"yace babu komai ai Y'ay'a amanane a gurin iyayensu hakk'i ne akanmu mu kula dasu shiyyasa kika ina yin duk ai kin da zanyi don in kula daku.
*Washe gari*
tun sassafe na tashi nayi shirina na makaranta naci abinci,na fito na gashe dasu Malam sannan ya mik'omin kud'in yace gashi in kai makarantar ince za'ah ciko sauran kud'in,"Nace to Baba na gode Allah ubangiji ya k'ara bud'i Babana yace Amin ya Mamana Allah ubangiji ya baku sa'ah a jarrabawar nan"Nace Amin Baba na.
Ina zuwa makaranta na had'u da Zainab itama lokacin tazo makarantar,Muka gaisa take cemun in rakata Zata biya kud'i"Nace to muna tafiya muna hira har muka iso wajen muka ga gaida mutumin sai fara'ah yake mana yana kallona, bayan Zainab ta bada nata kud'in aka bata recief sannan nima na bashi nawa.
"Nace ga nawa amman rabi ne zan ciko sauran,Kallona yafara yi kamar yana nazarin wani abu a fuska ta cen yace,Amman yadda kike d'innan abun ya bani mamaki don duk wanda ya ganki zai d'auka wata y'ar gidan mai kud'in ce.
Shiru nayi ina kallonshi don ni gani na keyi rainin wayo ne ma idan bazai amsa ba yaga yamun mana amman sai yayi mun wulak'anci sannan zai amsa.
Kallo na yayi akaro na biyu sannan yace yanzu nawa zaki ciko,nace mishi dubu biyar ne," Yace oky babu komai zan bada kud'in kar kiji komai,Shiru nayi ina kallonshi da mamaki a fuska ta ina mamakin kud'in da yace ya cikamun saina jiyo Muryar Zainab tana"Cewa Mun gode Sir Allah yasaka da Alkhairi.
Ban sanda nima na fara yimai godiya ba,Muka fito daga Office d'in yana mai k'ara kallona Cikin zuciyarshi kuwa shi kad'ai yasan abunda yake shiryawa akan Mumtaz Shiru yayi yana tuno sanda ya tambaye ta sunanta tace Sunana Mumtaz,Ahankali yace Wow Nice Name ya fara juyi akan kujerar sa ta Alfarma.
Muna fitowa"Nace Zainab Wai don Allah me mutumin nan yake nufi dani ne daya ke cewa Ya d'auka ni y'ar Maikud'i ce?Shiru Zainab tayi sannan tace to wai ke Mumtaz baki gane ba ne?,nace kwarai kuwa ban gane me yake nufi ba sam.
Zainab"Tace Hmm wato Mumtaz ked'in ta da bance ke Wallahi saboda komai naki i'rin na y'ay'an sarakai ne ko Y'ay'an masu kud'i, Saboda Allah yayi miki wata irin baiwa.
Allah ya baki baiwar kyau da baiwar Ilimi da baiwar Hankali da nutsuwa kinga kuwa Babu Wanda zai samu wad'annan abubuwan ba tare da anyi sha'awarsa ba,Dariya nayi "Nace Hmm Zainab kenen kedai kawai kice kina wasa k'awarki kawai amman ni banga wani abu dana fi kowa ba,Dariya itama tayi sannan " Tace ni kuwa Wallahi naga abunda kika fi dubbun mutane,Nan dai muka cigaba da hirarmu ta k'awaye cikin Fasaha da fahimtar Juna.
**********
Mumtaz"Tace Malam Wallahi Wani Malamin mune ya biya mun sauran kud'in,Malam yace to Mamana wani Malamin ne? "Nace Wallahi a makarantar mu yake,Malam yace to Allah ya saka da Alkhairi ,Nace Amin Baba "Malam Yace Amman Mama na kuringa kula da Makaranta zaka had'u da Mutane kala kala wala d'alibai wala Malamai don haka ki kiyaye,Nace to Malam Insha Allah.
Mun fara jarrabawa cikin sa'ah har muka gama exam,cikin sa,ah yanzu kuma mun tafi hutun sati biyu.
Ina zaune a tsakar gida ina yanke farce na,Wani yaro ya shigo yana cewa wai ana sallama da Mumtaz inji wani a waje,Shiru nayi ina kallon Yaron sai naji Umma tace kaje gatanan zuwa.
*Gaskiya kun rage tyiping Fans"*
Yawan tyiping yawan comments
*Ummu Maher ce*
Vote
Share
And
Comments📝
*Tyiping*🖌️
ABOUT MY WORK✍🏻
💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚
*NA*
*RABI'ATU.B.ABDULLAHI*
(Ummu Maher)Miss green💚📗
بسم الله الرحمن الرحيم
_________________
______
🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚🖊
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa _
🏔🅙︎🅦︎🅐🏔
*BABI NA 21&22*📝
Nayi kamar banji abunda Umma ta fad'a ba don haka nayi shiru nak'i tashi Cikin zuciyata kuma tunani kawai na keyi wannan waye ya turo a kirawo ni?to koma dai waye ba zanje ba Don ni anawa tunanin bazan Fara zance ba har sai na gama makaranta sannan Zan Fara zance ,don ba Zan had'a makaranta da soyayya ba.
"Umma tace Mumtaz dake fa nake magana ki tashi kije waje kinyi bak'o," Nace to Umma Bari in k'ara sa yanke farce na"Umma tace to kiyi sauri dai ki tashi kije babu dad'i wulak'anci.
Wata kyakkyawar Mota na hango a k'ofar gidanmu irin mai bak'in glass d'innan,kuma ba'a hango mutumin da ke cikin motar,don haka a hankali na'isa wajen cikin murya ta mai dad'i"Nace Assalamu Alaikum,Wanda ke cikin motar ya amsa ba tare da ya fito ba.
Don haka nima sai naja na tsaya awajen ba tare Dana sake magana ba, Saboda ni arayuwata babu abunda na tsana aduniya sama da girman Kai,to idan ba girman Kai ba to menene?Nayi sallama ya amsa Amman bai fito ba nufinshi ni Zan bud'e motar in shiga kome?to A'i kuwa in dai haka ne zai dad'e don ni babu abunda na tsana irin zance a mota.
Cikin fushi nayi hanyar gidanmu saboda bazai yiyu yazo har k'ofar gidanmu ba sannan kuma yace zai raina mun wayo ba.
"Mumtaz don Allah ki tsaya kiji da abunda nazo miki da Alkhairi nazo miki,Muryarshi ce naji tazo mun a bazata koda ba'ah fad'amun ba nasan cewa Sir Mukhtar ne na makarantar mu,to meye ya kawoshi gidan mu kuma?.
Juyowa nayi Sannan "nace Sir sannu da zuwa ba tare da na had'a ido dashi ba,Saboda wani irin kwarjini da yayi mun ga wani irin kunyarshi da naji lokaci d'aya.
" Sannunki Mumtaz ya gida yasu Mama da Baba?"Nace duk suna lafiya Sir"Oky to Masha Allah wato Mumtaz nasan zakiyi mamakin zuwa na gidanku, Amman ba abun mamaki bane Saboda sone yaja Hakan.
"Mumtaz tun ranar da na Fara ganinki naji zuciyata ta aminta dake kuma zanso ki zamo Uwa awajen y'ay'a na,Ayanzu inada shekara 35 Amman tun ban Kai haka ba iyaye na suka damu inyi Aure,Saboda ni kad'ai ne d'ansu da suka mallaka arayuwarsu,don haka suke son inyi Aure suga Matata da Y'ay'ana.
Sai dai haryanzu banga matar da ta kwanta araina irinki ba ina sonki Ina k'aunarki Wallahi Mumtaz tun Ranar da na ganki naji Ina matuk'ar sonki so mai wuyar fassaruwa,Amman Ina fatan kema zaki Soni kamar yadda nake sonki?.
Shiru Nayi sa kama kon jin furucin Sir Mukhtar,Tabbas babu macen da zata ga Sir Mukhtar tace bata sonshi,Saboda yana da abubu wanda duk mace zata soshi,Yanada ilimi arabi da boko,yanada kyau,kud'i Da kuma hankali,kusan dai ya had'a dukkanin wani Abu Wanda mace zata soshi,Sai dai A i'nda gizo yake sak'a Shine kwata kwata ban shirya yin Aure yanzu ba Saboda inason inyi karatu in samu A'iki in taima kawa iyaye na,Sannan kuma bana son in had'a Soyayya da kuma karatu,don mafi akasarin y'an matanda suke biyewa Samari suyi ta soyayya k'arshe sai kiga babu abun arzik'in da suke shukawa A'cikin ajinsu.
"Mumtaz kina jina kuwa naji kinyi Shiru? kodai abunda nazo miki dashi ne ba kiyi a munna dashi ba?
DA k'er na bud'e bakina" Nace kayi hak'uri Sir Mukhtar bawai nak'i aminta da abunda kazo mun dashi bane A'ah kawai dai ni banason had'a Makaranta da Soyayya kawai shine matsala ta,kuma inason inyi karatu in samu Aiki don in taimakawa Iyaye na.
Sir Mukhtar "Yace babu komai Mumtaz kada ki damu indai kin amince Dani ni bazan zalin ceki ba,Ba kuma Zan ta kuraki ba Zan jira har lokacin da zaki gama karatunki sannan kuma in samo miki A'iki.
Kunya ce ta kama Mumtaz tayi saurin yin hanyar gidansu tana rufe fuska,tabbas tasan Son Sir Mukhtar ya Fara Kama ta don gashi tun daga yanzu ya Fara yi Mata kwarjini kuma ta Fara jin kunyarshi.
Shi kuwa Sir Mukhtar shafa kanshi ya Fara yi yana kallon Mumtaz cike daso da k'aunarta,ya shiga motar shi ya d'auko wasu kaya,sannan ya fito ya samu yaro yace ya kaiwa Mumtaz yana ganin yaron ya shiga saiya shiga motarshi ya tafi yana mai farinciki.
Mumtaz kuwa tana shigowa gida ta wuce d'akin ta da sauri tana fara'ah don bata kula da Umma dake tsakar gida ba tana yi Mata magana,Umma kuwa Murmushi tayi tabi Mumtaz da kallo Saboda idan kaga Budurwa tana farin ciki irin wannan to ta fad'a cikin soyayya,Umma bata gama rufe bakinta ba taji sallamar yaro,Yaron"Yace wai gashi inji wani a waje a bawa Mumtaz wannan.
Umma ta amsa tana cewa to An gode, Umma ta fara bud'e wani kwali kamar na wayar Hannu,ta bud'e shi me zata gani?wata dan k'areriyar waya ce mai kyau da tsari,Hannun Umma kuwa kakkarwa kawai ya keyi,sannan ta bud'e wata envelop ✉ kud'i masu yawa aciki ga wata zungureriyar ta karda aciki,da k'arfi Umma ta Fara kiran Mumtaz cike da tashin hankali.
Da sauri Mumtaz ta fito ta tsugunna"Tace Umma gani,Mumtaz waye wanda yazo gurinki yanzu? "Umma Sunanshi Sir Mukhtar Malamin mune a makaranta Shine wai yace yana sona.
Umma tayi shiru kamar baza tayi magana Cen kuma" Tace shikkenan tashi ki tafi Bari Malam ya dawo zamuyi magana dashi, a hankali Nace to Umma.
********
Meema ta kalli Farida"tace kinsan Allah Farida bazan fito bariki a banza ba in koma a banza,kina ganin Murat sai binshi na keyi ya Aureni Amman sai wulak'anci ya keyi mun Saboda yaci moriyar ganga yanzu saiya zubar Dani.
Farida"tace A'i ni wallahi mamaki ma kike bani da kika lik'ewa Murat meye amfanin son Wanda bai damu da Kai ba,Saboda haka kawai gwara ma ki hak'uri dashi kawai,ga maza nan y'an bariki sai binki su keyi kina wulak'an tasu ke kince sai Murat kuma har kina maganar ya Aure ki,kada ki manta fa kunyi bariki dashi koda kin Aureshi ba lallai bane kuzauna zaman aminci da kyau na ba.
Haba Farida meyasa kike fad'in haka Kinsan cewa matuk'ar ban Auri Murat ba komai zai iya faruwa dani,Nidai don Allah Farida ki samomin mafita don Allah.
Farida"tace Meema Zan baki wata y'ar shawara da kuma wata dabara irin tamu ta y'an bariki,Meema tayi y'ar fara'Ar da tunda suka Fara magana ba tayi ba,"Tace ina jinki Farida nasan ba zaki bani banzar shawara ba,Farida tayi dariya sannan "Tace A'i dole in baki shawara tunda Ina cin banza, don Meema idan ban baki shawara ba ma sai Allah ya tambayeni don duk kud'in da muke samowa tare muke cinye romon kinga kuwa dole ne in baki shawara don a cigaba da samo mana d'an abun b'atarwa.
Farida" tace Meema yanzu zamu Fara tun tub'ar Murat akan maganar Aurenki i'dan yak'i yarda saimu had'a mishi gadar zare Wanda ba zai i'ya tsallakewa ba.
Meema"tace k'awata wani i'rin gadar zare ne Wanda ban San dashi ba?Farida"tace Meema tambayar da nakeso inyi miki wani mutunne Murat yafi tsana aduniya saboda da haka ne zamu had'a mishi gadar zare.
Meema tayi shiru cen Kuma "tace kwarai akwai hallitar da Murat yafi tsana aduniya don kuwa ko zancen Muta'z kika yiwa Murat sai kunyi fad'a.
*Yawan Comments*
yawan tyiping✍🏻
*Ummu Maher ce*
*Vote*
*share*
And
*Comments*
*Tyiping*🖌️
💚🤍💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚🤍💚
ABOUT MY WORK👩🏻🏫
*NA*
*RABI'ATU.B.ABDULLAHI*
{{Ummu Maher}Miss green
💚}
*💅Shalelen Jarumai writers Ass💅*.
____________
Y'AR MUTAN NIGERIA🇳🇬💚🤍💚
*BABI NA 23&24📝*
Wata irin soyayya mai k'arfi ce ta shiga tsakanin Mumtaz da Sir Mukhtar,kuma ayanzu Umma ta gaya wa Malam Abinda Mumtaz ta fad'a mishi a ga me da Mukhtar,Babu b'ata lokaci Malam yayi bin cike a ga me da Mukhtar kuma Alhamdilillah ya samu shaida ta gari shi da Mahaifansa,don Asalin Familynsu FAmily ne na da mutunta duk wani d'an Adam,kuma sun samu shaida mai kyau don haka kowa ya ke ganin mutuncinsu,ga su suna da asali mai kyau shiyyasa kowa ya ke sha'awar zama dasu.
*Bayan wasu watanni*
Su Mumtaz na hango suna Celebration wato Murnar gama makaranta,Wanda Sir Mukhtar ya shirya wa Masoyiyarsa Mumtaz Tare da k'awayenta idan har kaga Mumtaz yanzu ba za ka gane taba Saboda yadda ta k'ara kyau ta k'ara wa yewa ta fuskar abun hannu kuma ma'ana kud'i shima Alhamdulillah,saboda a yanzu babu abinda za su cewa Sir Mukhtar don ya gama musu komai ta fannin Rayuwa.
*SIR MUKHTAR*
"Mumtaz kin yanzu Allah ya yadda kin gama makarantar ki KO?Kuma a yanzu babu abinda zamu ce sai dai mu yi wa Allah Godiya,tunda ga shi yanzu kin gama makaranta sai asha biki KO?.
Wata i'rin kunya ce ta ka ma Mumtaz kamar ta nitse a k'asa don tsabar kunya," Ta ce Malam ma ya yi mun wannan maganar da man jiran ta ba kin ka na ke jira sai ga shi kuma ka yi,Allah dai ya kad'e mana duk wata fitina.
"Amin my Mumtaz, ya fad'i hakan yana mai yiwa Mumtaz dariya tare da k'arajin wani son ta har cikin zuciyarsa,ya ji kamar ya janyo ranar Auransa da Mumtaz.
Nan dai suka cigaba da hirarsu tsakanin Mukhtar da Mumtaz.
*MU'TAZ*
" Yanzu don Allah Momi ba zaku bar maganar Auren nan ba yarinyar nan ba tada hankali KO kad'an In banda Hajju da rigima ta k'eleni mana in za b'a da Kai na mana, amman ta da meni da maganar wannan yarinyar da gaba ki d'ayanta goyon ka ka ce.
"Haba d'a na ka daina fad'in haka kaga wannan Alk'awarin Hajjo ne babu yadda zakayi dole sai hak'uri,ka ga Mahaifinka bai tab'a tsallake maganar Mahaifiyarsa ba kada kasa a wannan karan ya ba wa Mahaifiyarsa kunya akan Ta ce zata had'a Auren Zumunci tsakaninka da y'ar k'anwar Mahaifinka,kayi hak'uri don nima za ka janyomun zagi a wajen Hajjo.
" Cikin fushi Muta'z ya ta shi ya fad'a sa shensa ba tare da ya k'ara magana,saboda yadda ya tsani yarinyar nan abun ba'ah magana.
*SIR MUKHTAR*
"Hajiya kin San na dad'e i'na baki labarin Soyayyata da Mumtaz tsahon lokaci,to yanzu Iyayenta sun ce In turo Shine Na ce Bari in gaya miki,Saboda tun jiya na fad'awa Alhaji ya ce zai tura gidansu Mumtaz d'in,Shine Nace Bari in fad'a miki........
"Hajiya ce cikin fushi ta mik'e tsaye Ta ce Kai tsaya da wannan banzar maganar da ka ke yi ni kake fad'awa wai ka fad'awa Alhaji wai ya ce zai tura gidansu Mumtaz Ce wa za'ah tura gidansu, to Bari kaji bazan had'a Zuri'a ta y'ar talakawa ba.......
*Yawan sharhi*
*Yawan Rubutu*
don wallahi bakwa Sharhi.
*Kayi Sharhi*
sannan ka 👉🏻
*Ka tura*
*Miss green💚 ce*
*💅💃Shalelen Jarumai*
*🖊️Tyiping*
💚🤍💚🤍
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKI NA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚🤍💚🤍
Which means👇🏻
*ABOUT MY WORK*👩🎓
________✍🏻
*NA*
*RABI'ATU.B.ABDULLAHI*
{{Ummu Maher}}Miss green💚💚
Y'AR MUTAN KANAWAN NIGERIA🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
*Nabila dikko anda Nabiha Aminu uwayen d'aki ns gaisuwa ta ban girma gareku*
*Mominal Minal ban girma gare ki Marubucuyar Samiha y'ar mace*
da
*Momin shukura shugabar k'unguyar mu ban girma gareki Allah ya k'ara lfy*
*Na sa daukar da wannan shafin ga Y'an k'ungiya Baki d'aya*
wato
Jarumai Writer's Ass✍🏻
Da
Fans d'ina a duk inda suke, mussaman.
*KALTUM KANNA*
*AMIRA*
*BINTA SULAIMAN*
*MOM ARYAN*
*LUBABATU SULAIMAN*
da sauransu🤝🏻
🔔📚🔔
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
_{Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa}_
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=337435884671992&id=103920888023494&sfnsn=mo
*⚜️©J.A.W⚜️📚🖌️*
*Shafi na 25&26📝*
"Kai ko kunya ma baka ji ba zaka zo ka ce mun wai wannan y'ar matsiya tan ka ke son ka Auro mana gida,ba bu wanda bai san yadda tsiya ta yi musu k'a tutu ba,Shi ne ni zaka Auro mun Y'ar matsiya ta."
"Wallahi ba zai tab'a yi yuwa ba,saboda duk gidannan ba bu matsiyaci ballan tana matsiya ciya,don haka ka bud'e kunnu wan ka ka ji ni ba zaka Auri wannan yarinyar ba na za b'a maka matar da ta da ce da kai."
"Kuma ko tai makonsu ka k'ara yi Allah ya i'sa ban ya fe maka ba,don kud'inka ba a taimakon matsiya ta zai k'are ba don mu kullum ba ma son mu ragu sai dai kullum ar'zik'inmu ya yi ta k'a ruwa.
"Don haka sai su bi wani sarkin ni dai na hane ka da Auran y'ar matsiya ta jikan matsiya ta,Msssst kuma wallahi tallahi naji labarin ka fad'a wa Alhaji abin da ya faru ni da kai ne,sakarai kawai lusarin Namiji....."
Shiru Mukhtar ya yi kamar zai yi kuka,zuciyarsa na ta farfasa kamar zata fasa k'irjinsa ta fito,don yana yi wa Mumtaz son da bai tab'a yi wa wata d'iya mace ba.
Tun da ya ke bai tab'a soyayya da wata y'a mace ba ko kuma ya ce yana son ta ba,Tun y'an gidansu na yi mai magana har sun gaji sun k'e lesa saboda ko maganar mace ma ba ya so.
Sai ga shi lokaci d'aya ya sa ba da Muntaz ga wani mahaujacin son da ya ke mata,Kash!sai ga shi yanzu Mahaifiyarsa ta raba shi da abar son sa Mumtaz.
Wai me yasa iI'yaye su ke shisshigi a rayuwar y'ay'ansu wajen raba su da abin da ya ke so?,kuma ya ke muradin Rayuwa da i'ta har abada.
Tambayar da Mukhatar ya ke yi wa kansa? i'ta ce da wani i'do zai du bi Mumtaz kuma?Kuma da wani i'do zai du bi i'yayen Mumtaz da sunan ya dai na son Y'arsu.
Wasu hawaye ne suka fara zarya a idanunsa yana nemarwa kansa mafita,ya yanke shawarar Tafiyar da ya yu niyyar yi tun kafun su had'u da Mumtaz don k'ark karatunsa a England don haka yanzu ya zamar masa dole ya ta fi.
Saurin ta shi ya yi ya fita don fara shiri do a gobe ya ke son tafiya,Amman a daren nan zai je gidansu Mumtaz don ya ba ta sak'o y wuce ba ta re dasun had'u ba.
Cikin gaggawa ya d'auko bairo da ta kadda ya fara rubutu a ciki kamar haka.
_*Assalamu Alaikum*
" Amincin Allah ya tabbata akan ki Masoyiya ta Mumtaz.
Mumtaz Na so ki zama matata uwar y'ay'a na amman Allah bai yi ba,don wani mashi ya tsaya cak a cikin rayuwarmu ya hanamu rawar gaban hantsu.
Ban tab'a soyayya da wata y'a mace ba sai ke Muntaz,ballan tana ma har in samu daman Yaudarar wata y'a mace.
"Mumtaz inasonki kuma da sonki zan mutu,don Allah idan na mutu ki dinga yi mun Addu'ah kuma ki sakawa d'anki/y'arki su na na hakan zai sa koda na mutu inji dad'i.
Ki ya fe mun mumtaz don Allah,sannan ki ba wa Malam hak'uri a kan abinda ya faru.
" A k'ashe ina miki fatan Alkhairi Idan kin samu miji kiyi Aure.
Ki ya femun Mumtaz.
da ga
Sir Mumtaz_ ✍🏻.
____________________
Yana gama rubuta wa ya go ge hawayen da ya wanke masa fuskarsa yana Shesh shek'ar kuka kamar wani d'an yaro k'arami ko kuma yaron da aka hanashi Mama.
daga cen ne sa ya tsaya da motarsa ya samu yaro ys ba shi envelope d'in wato wasik'ar sannan ya bawa yaron wani Envelope k'ato sannan ya bawa yaron ya shiga gidan.
Sai da yaga yaron ya shiga gidam sannan ya shiga motarsa ya d'ora kan sa jikin sitiyarin motar yans kukan zuci,Sannan ya tafi zuciyarsa a da kushe.
K'arfe Hud'u na yamma jirginsu ya ta shi sai England yana hango ga jimari ya rufe idonsa yana kukan rabuwa da Mumtaz tare da Mahaifinsa,don Hajiyarsa ma murna ta ringa yi da tafiyar d'an na ta.
Alhaji kuwa ko da ya tambayi d'an nasa dalilin sa na k'in Auren Da ya ce a nemar mai k'in basa amsa ya yi k'arshe ma ya ta shi ya bar wajen yana kukan zuci.
Haka Alhaji ya samai ido yana taya d'an nasa addu'ar Allah ya kare mishi d'an Na sa a duk i'nda ya ke,ya kuma kawo masa mata ta gari shima ya huta da zaman gwaurancin da ya ke yi.
*************
Da gudu Mumtaz ta le k'a d'aki hannun ta yana kakkarwa ba kinta ma yana kak karwa idanunta kuwa ya yi jawur kamar garwashi.
"Um..um Umma kin ga wannan ta kaddar".
har lokacin bakin Mumtaz kak karwa ya ke yi.
Umma ta amsa cikin tsoro tana Ce wa.
" Mumtaz ta kaddar me ce ce wannan?ta fad'i hakan cikin ta shin hankali da furgici.
"Umma Sir Mukhatar ne ya aiko mun yanzu wai ya fasa neman Aure na idan na sa mu miji in yi Aure"....
*Ummu Maher ce*
*Vote*
*Share*
And
*Comments*
*🖊️Tyipin🖊️*
💚🤍💚🤍
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKI NA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚🤍💚🤍
Which means👇
*ABOUT MY WORK🧑🎓*
________✍🏻
*NA*
*RABI'ATU.B.ABDULLAHI*
{{Ummu Maher}}Miss green💚💚
Y'AR MUTAN KANAWAN NIGERIA🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
💫💫
*🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️*
https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl
_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_
*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*
*Shafi na 27&28📝*
______Wani k'u lulun ba k'in ciki ne ya tsaya wa Umma acikin ranta,wai Mukhtar ya fasa Auren y'arta Mumtaz to a k'an wani dalili?Zai Rabu da'ita menene laifin Y'arta Mumtaz?.
Kukan da Mumtaz ta Fara yi ne ya dawo da Umma daga cikin tunanin da ta ke yi,tayi saurin zuwa ta rufe bakin Mumtaz tana Cewa"Kiyi hak'uri Mumtaz komai ya yi farko yana da k'arshe Da man Allah ya yi Mukhtar ba mijin ki ba ne don haka ki fauwa lawa Allah komai shi zaiyi miki maganin komai Allah kuma ya ba ki miji nagari Wanda ya fishi.
Nan dai Umma ta ringa rarrashin Mumtaz tayi shiru sai dai ciwon kan da ya da me ta don har yanzu son Sir Mukhtar yana Nan a ranta,har yanzu tambayar da Mumtaz ta ke yi wa kanta shi ne ?wai me yasa Sir Mukhtar ya rabu da i'ta me ta yi mai da har zai d'auki wannan mummunan mata kin a kanta?.
To koma dai menene bai kamata ta rabu dashi ba,ya zama lallai ta nemi gidansu ta je ta sa mesa don ta ji Da hir abinda yasa Sir Mukhtar ya daina son ta.
Koda Malam ya dawo yaji abinda ya faru shima addu'ah ya din ga yiwa Mumtaz tare da yi Mata nasiha a kan rayuwa,Sannan Umma ta nuna wa Malam kud'in da Sir Mukhtar ya ba yar a bawa Mumtaz.
Shiru Malam ya yi sannan Ya ce"Shi Mumtaz d'in ne ya bayar a bawa Mumtaz d'in?
Umma "ta ce eh Malam shi ne ya ce a ba ta Amman Malam wannan kud'in ya yi yawa?.
" Kada Ku da mu Zan samu Mahaifinsa tunda na San gidansu Amman mu ba za mu amshi kud'in sa ba don munfi k'arfin a siye mu da kud'i."
*ENGLAND*
Sir Mukhtar Ya ce"Hello kana ji na I'na son ne ma Mata A'iki ne anan wajenku to i'nason ka turo mun number Shugabanku don muyi magana dashi don yarinyar tana da buri a Rayuwar ta na zama cikakkiyar y'ar jarida saboda ta kare mai gaskiya kuma yarinyar tana da jajir ce wa........
A hankali Sir Mukhtar ya ke maganar lokacin da wasu sa babbin hawaye suka zubo masa ya yi saurin go ge su,sannan ya ce"Rabi'u sai anjima ka turo mun da number.
Rabi'u ya ce"Ba b komai Mukhtar Insha Allah kada kaji komai Zan turo maka Nagode oga Allah ya ba da abinda a ke nema."
"Amin"
"Na gode"
"Rabi'u"
Suna gama wayar kuwa Rabi'u ya turowa Sir Mukhtar number,Mukhtar ya yi mai godiya Sannan ya kirawo ogansu Rabi'u.
Hamdala Mukhtar ya yi bayan sun gama wayar Sannan ya turawa Ogansu Rabi'u kud'i naira na gugan naira har dubu d'ari uku cuf Akan d'aukar Mumtaz da sukayi A'iki a gidan radio har Dana TV.
Sannan yaja musu kunne a kan kada su yadda su gaya Mata ce wa shine ya ne ma mata A'iki saboda ya San yanzu suna cikin fushi dashi sosai,shiyyasa ma ya fito da wannan hanyar don su rage zafin abinda ya yi wa Mumtaz.
Allah ya gani har yanzu yana son Mumtaz kuma bai fidda ran Auren ta ba,don gani ya ke yi matuk'ar bai Auri Mumtaz ba komai zai i'ya faruwa da shi.
*MUTA'Z*
"Haba Hajjo ke duk sanda nazo wajenki sai kin ne mi ki b'a ta min rai?Meye laifi na don Na ce ba za'ayi min Auren dole ba?Na ce miki ba na son Meemi wannan yarinyar mai d'an Karen si ranta kamar wata horo wallahi ba Zan Aure ta ba".
Hajjo ce ta rik'e baki tare da Ce wa"Inye lallai wannan yaron wato Kai yanzu ka girma KO?to wallahi baka i'sa ba kuma Wallahi baka i'sa ka Warware Alk'awarin Barkindo ba.
Wato Barkindo shi ne Mijin Hajjo tsohon sarki Wanda ya mutu ya barwa d'ansa tilo wato Mahaifin Muta'z.
"Kuma wallahi zanga uban na ka idan ma shi ne ya ke zugaka don kayi mun rashin ta i'do" tun bata I' da maganar da ta ke yi ba Muta'z ya yi tafiyarsa da ya ke Mumtaz akwai shi da zuciya sosai.
Hajjo ta harari bayan Muta'z Ta ce" d'an ne ma wato kai ma ka yo halin Barkindo na zuciyar masifa d'an a bu k'an k'ani sai ya haddasa Zuciya to yanzu me ye abin fad'a anan.
da sauri Meemi ta fito a wajen da ta lab'e saboda yanzu Muta'z ya kafa Mata dokar matuk'ar yana waje kada ta kuskura ta fito saboda idan ta fito sai ya b'ata Mata rai,i'ta kuma a duniya tana tsoron Muta'z don ta San halinsa da zuciya kamar kuturu.
"Haba Hajjo kina jin sa wai yana ce wa da siranta ta kamar horuwa Haba Hajjo gaskiya na gaji da cin mutuncin Hamma Muta'z kullum da wulak'ancin da zai yi mun saboda ya San Ina sonsa,gaskiya Hajjo idan baki Auramun Hamma ba mutuwa zanyi.
Nan dai Hajjo ta ba wa Meemi hak'uri akan Komai ya zo k'arshe ya zama dole mai babban suna ya Aure ki ja'iri kawai.
*MURAT*
"Ke! mima na gaji da wannan Alk'awarin na ki har yanzu lokacin d'aukar fansa ta baiyi ba don wallahi na rantse na kuma rantsewa sai na d'auki fansa A kan Muta'z".
🤔 To fa kunji mai sauraro wai sai ya d'auki fansa kan Muta'z kamar ya yi mishi wani Abu, duk taimakon da Muta'z ya yiwa Murat Amman ya manta shi so ya ke yi sai ya cuci shi don hassada.
y'an uwa na mudaina hassada domin hassada babban ciwo ne Allah ya tsare mu da hassada Amin🤲🏻.
Mima Ta ce "Come down Murat da d'i na da Kai ragon hak'uri Amman na fad'a maka akwai plan d'in da na ke shirya wa don haka kada ka da mu komai yazo End.
Nan fa Mima ta janyo Murat zuwa d'akin masha'arsu wai duk don ta lallab'ashi don i'ta kad'ai tasan abinda ta barwa zuciyarta kuma i'ta kad'ai tasan plan d'inta.
*Miss green ce💚💃*
*Share And Comments*✍🏻
*Tyiping🖌️*
💚🤍💚
🤵♀🤵♀🤵♀
*A KAN AI'KINA 2021*
🤵♀🤵♀🤵♀
💚🤍💚
Which means👆🏻
*A BOUT MY WORK🤵♀✍🏻*
Na
*Rabi'atu.B.Abdullahi*
(Ummu Maher)Miss green💚📗
💫💫
*🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️*
https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl
_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_
*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*
*Shafi na 30&31*
_______🖌️"Yanzu Mukhtar saboda na hana ka Auren wannan matsi ya ciyar yarinyar shi ne ka ke ga ba dani,saboda na ce to ka daga halaka shi ne ka ke ne man ka bijire mun to wallahi tallahi ko kaso ko kada kaso na ne mo maka matar da ta da ce da kai"...
Tun ka fun ya ce wani abu Hajiya ta kashe wayar ba tare da ta ji me zai ce ba,kallon wayar ya cigaba da yi da tunani fal acikin zuciyarsa.
Yana cikin wannan tunanin Musa ya kirawo shi a kan maganar Mumtaz don yanzu an gama komai har ta fara zuwa Aiki Amman ba da sanin Mukhatar ne ya ne mo mata Aikin ba.
Godiya Muktar ya shiga yi wa Musa sannan ya k'ara tura masa wasu kud'in,sannan ya ce ya cigaba da kula masa da Ajiyarsa wato Mumtaz don shi har yanzu bai fitar da ran Auren Mumtaz ba.
***
"kai Allah mun gode maka da ka kawowa Mumtaz wannan Aikin a wannan lokacin,Allah ya kare ki Mumtaz da karewar ubangiji da mala'ikunsa Allah ya baki ikon yin gaskiya aduk inda ki ke.
Malam ne ya ke ta shararowa Mumtaz Addu'ah da fatan samun da ce wa aduk inda ta ke.
Malam kenan akwai ilimi da sanin ya kamata y'ar d'aya tilo a duniya wato Mumtaz a kullum cikin Addu'ah ya ke mata Allah ya kare masa i'ta a duk inda ta ke.
Sai a san Nanne Mumtaz ta d'ago kanta Ta ce"Malam Na gode da addu'arka kuma Insha Allah Zanyi ki ya ye A kan AI'KINA zan yi k'ok'arin Kare duk wani hakkin Dana San ba nawa ba ne."
"Allah ya yi miki Albarka Mumtaz ya Albarkaci Rayuwarki Mamana".
" Amin Malam".
"Na gode".
******
Hajjo Ta ce"Ai wannan albishir da ka yi min ya yi mun da d'i Allah sanya Alkhairi ya ba su zaman lafiya".
Mai Martaba Mahaifin Muta'z Ya ce" Amin Hajjo ni zan ta fi."
Nan fa Hajjo ta fa ra shi mai Albarka tana jin da d'i da haka har ta raka sa tana k'ara shi mai Albarka don ya cika Alk'awarin Mahaifinsa.
Daga inda Mimee ta ke tana jiyo Hajjo wato kakarta tana murnar Aurensu da aka d'aura i'ta da Muta'z,tsalle ta daka a cikin d'akin ta fa d'a kan gadonta tana dariya da kukan da d'i.
Hajjo ta ce"ke kinji min y'a saboda an d'aura miki Aure da wannan mai murtu kekkiyar fuskar shi ne ki ke dariya harda tsalle,to kya yi kya gama indai wannan ne ni ka d'ai Ce agabansa.😀
Ni kuwa Ummu Maher na ce"oh Hajjo kin tsufa me Muta'z zaiyi da ke kykkyawan d'an gayu mai ji da ilimin addini likita_ likitan likitoci.
***
"Haba Fulani kina sane da Auren da mai maitaba ya d'aura mun da wannan ja kar yarinyar wai a matsayin matata."
"Yarinyar da kwata_kwata bata San mutuncin mutane ba ballan tana sanin darajar d'an Adam,yana maganar yana Jan numfashi don shi hayaniya ma bai i'ya taba Asalima shi ba ya son surutu sam ..."
"Haba Muta'z me ka ke so in ce akan wannan maganar kafi kowa sanin halin mahaifinka,ba'ah yi mishi ja yayya kuma me ye ai binsa don ya yi wa d'ansa Aure,kuma ya za b'a masa matar da ta da ce da kai."
"So ka ke yi in yi mishi musu don ya yi maka Aure ko me?to ba zan iya ba domin mijina shi ne Aljanna ta."
"Kuma Hajjo Mahaifiyarsa ce don haka ba by abinda za ta umarce sa ya k'i yi Mata shi matuk'ar bai sa b'awa Allah ba,kuma matuk'ar inason ya rabu da mahaifiyarsa lafiya to dole ne in ta ya sa ya rabu Mahaifiyarsa lafiya".
" Don haka nima Ina mai u martarka da ka yi hak'uri kabi zab'in da iyayenka suka yi maka ko ka sa mu da ce wa,kuma ka cigaba da yi wa iyayenka biyayya wataran sai labari".
Fulani tana kaiwa ta tashi ta koma b'an garenta tana tausayin d'anta abin k'aunarta a kullum.
Bayan kwana biyu aka fa ra bidirin biki A yi wannan a yi wan can Amman ba bu k'eyar ango don tun ranar ya koma sabon gidansa da ya Gina saboda hutawa.
Har gida Hanan ta kaiwa Mumtaz Invitation na biki,ranar ta da d'e i'ta da Umma suna hira ka fun daga bisa ni Mumtaz ta dawo daga wajen Aiki i'ta da wani abokin Aikin ta mai suna Mohd Lawan,jininsu ya had'u sosai don haka kullum sai ya rakota har gida bayan sun dawo daga Aiki.
Ko kafun Mumtaz ta dawo kallon Umma Hanan ta ringa yi tana hango fuskar mai martaba a kan fuskar Umma,don har Mumtaz. Ta dawo Hanan bata daina kallon Umma ba tana mamakin irin wannan kamanni ya yi ya wa.
Daga Alk'alamin
*Ummu Maher*
*Vote*
*Share*
*And*
*Comments*
*Typing🖌️*
💚🤍💚
🤵♀🤵♀🤵♀
*A KAN A'IKINA 2021*
🤵♀🤵♀🤵♀
💚🤍💚
Which Means👆🏻
*A BOUT MY WORK🤵♀✍🏻*
Na
*Rabi'atu Bashir Abdullahi*
(Ummu Maher)Miss green💚🍀.
💫💫
*🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️*
https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl
_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_
*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*
*Shafi na 32&31*
Sosai Mumtaz ta yi murna da zuwan k'awarta Gidan su Wato Hanan sunyi hira sosai sannan ta ke fad'a mata bikin Sweet brother d'in ta sannan ta bata gate pass d'in wajen.
Har bakin motar ta Mumtaz ta raka ta sannan ta dawo gida,har sai da Mumtaz ta shiga gida sannan Hanan ta ja motarta ta tafi,har zuciyarta tana jin k'aunar Mumtaz tana ji da ma Mumtaz ta zama y'ar uwarsu tana kwad'ai tawa a zuciyarta da ma matar Yayan ta ce da wannan tunanin ta fara driving zuwa gida.
*MUTA'Z*
"Yanzu don Allah Abinda ka ke yi Mu'taz ya da ce kenan ace tunda aka saka rana har yau da za'ayi dinner ba kaje kun dai dai ta da yarinyar nan ba."
"Fulani ki yi hak'uri duk yadda ki ke so haka za'ayi insha Allah idan na fita zan shiga wajen Hajjo insha Allah".
Da d'i ne ya kama Fulani don dama tasan d'an na ta mutun ne shi mai girmama iyayensa shiyyasa ma a kullum ta ke k'ara son d'an na ta.
*MUMTAZ*
" Kai Masha Allah Mumtaz kin ga kuwa yadda ki ka yi kyau kuwa?".
Dariya Mumtaz ta yi sannan ta kalli Ummanta ta ce "sai na fara zuwa Aiki don yau ni ce da duty zan d'auko wani Aiki sannan sai na biya wajen Dinner d'in".
" to Mumtaz ki kula da hanya Allah ya ki ya ye".
"Amin Umma".
*****
Sosai Mimee ta sha kwalliya ta alfarma sannan ta fito don su gana da Muta'z don kiranta kawai ya yi ya ce tazo ta same shi yana son yin magana da i'ta, haka kuwa a kayi yana zaune wajen shak'atawar Hajjo sai ga Mimee tazo.
Tun daga nesa ya hango ta yana sanye cikin shadda blue ya sanya hularsa zanna bukar ya yi kyau sosai shaddar sai walk'iya ta k'eyi da shek'i alamun shaddar mai tsada ce sai wane da wane zasu saka ta.
SLM
Kawai ta ce sannan ta samu waje ta zauna idonta k'uri akansa tana yi mishi kallon tsaf,ta da d'e tana son yayan nata sai yau ne Allah ya kawo mata ranar da za ta malleke sa a matsayin Mijinta don an Riga da an d'aura Aure tare wa kawai za tayi.
Shafa sajensa ya yi Wanda yasha gyara ya kwanta luf abin sha'awa da k'er ya fara juya lulu eyes d'insa zuwa fuskar Mimee.
Babu laifi Mimee kyakkyawa ce fara ce irin fau d'in nan k'irar jikinta kamar na silindium don tana da siranta sosai jikinta dai kamar irin ma asalin turawa.
" Yaya Muta'z gani an ce kana kira na,so ana yimun Make_up ne shiyyasa banzo ba"...
D'aga mata hannu ya yi alamun ta tsaya da maganarta sannan ya ce",daman nazo ne don in gaya miki bazan samu damar zuwa wajen dinner ba,idan ke za kije to ga hanya nan Amman ni bazan je ba,kuma kada ki kuskura ki fad'a wa rigimammiyar tsohuwar nan idan kika gaya mata in kika shigo hannu na ba zakiji da d'i ba,tunda ba tsohuwar ce za yi miki zaman Auren ba."
D'aukar glass d'insa ya yi irin me Skye d'innan yasa ka sannan ya yi wucewarsa yabarta da shak'ar dadda d'an k'amshin turarensa.
Bin bayan shi Mimee ta yi da kallo yana k'ara shiga ranta ji ta ke yi kamar ta janyo dare don ta ganta ga ta ga Yayan ta abin sonta.
Shi kuwa gogan bayan ya fito Gidan hutawarsa ya tafi don yaje ya huta kuma akwai wasu abubuwan da ya keso ya yi saboda haka ne yasa yazo Gidan don baya son hayaniya.
Saida ya yi sadaka sosai da kud'i,tsoffi sai addu'ah suke masa yana amsawa har ya shiga gidan.
Bai samu mai gadi a bakin gate d'in ba don haka da kanshi ya fito ya bud'e gate d'in sannan ya shiga,don yana tunanin ko yana ban d'aki ne.
Koda ya shiga gidan numfarfashi ya dinga ji acikin gidan yana bin lungu da sak'o na gidan yana dubawa.
Abinda ya gani ne yasa shi k'amewa awajen saboda abinda ya gane wa idanunshi.
*MURAT*
"Murat Aiki ya kan kama an gama komai yanzu burinka ya kusa cika ko kuma in ce ya cika ma."
Juyowa ta yi rik'e da wayarta a hannu tana dariya kamar mahaukaciya,sannan ta ce"babu abinda bana ganin bayanshi idan ya ce zai shiga rayuwata don haka mutane suke tsoro na.
Mima ce ta ke fad'in haka ya yin da ta kewayo da hannu ta kan sajen Murat cikin kissa da kisisina."
Janyo hannunta ya yi da k'arfi sannan ya ce"My Mima kin gama min komai dole ne ki zama ta hannun da ma na,dariya ta yi sannan ta d'auki glass cup tana shan lemo,tana jin zak'in lemon har can cikin zuciyarta sai da ta yi kurb'a biyu sannan ta ajje cup d'in ta d'auki wayar ta tana Neman wata number.
*__MUMTAZ___*
"Mohd yaushe zamu tashi ne saboda inason zuwa wata dinner ne?".
Ya bud'e bakinsa zaiyi magana wayar sa ta kama ruri,da sauri ya d'auki wayar yana cewa" hello waye.
Murmushi Mima ta yi sannan ta saita muryarta ta ce"Assalamu Alaikum. "
"Don Allah kutaimaka kuje gidan Muta'z Abubakar yarima Wanda ya ke titin gidan Radio d'inku,mun ganshi ya d'auki wata yarinya da gudu aka yasaka ta acikin motarsa Amman yanzu don Allah kuje kada ya cutar da i'ta."
"Hhh hhh hhh"
Dariya Mima ta yi sannan ta cire sim d'in ta saka shi a kwandon shara,Murat shima dariyar ya ke yi Sannan afili Ya ce".
*_MUTA'Z THE LIFE IS🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥_*
*Real Ummu Maher ce✍🏻*
Vote
Share
&
Comments✍🏻
*Typing*🖌️
💚🤍💚
🤵🏻♀🤵♀🤵🏻♀
*AKAN AIKI NA 2021*
🤵🏻♀🤵♀🤵🏻♀
💚🤍💚
Which Means👆🏻
ABOUT MY WORK🤵🏻♀✍🏻
Na
🌹Rabi'atu B/ Abdullahi🌹Ummu Maher
(Miss green)💚☘️
💫💫
*🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️*
https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl
_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_
*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*
*Shafi na 33&34*
Dariya Murat ya yi sosai irin dariyar basawa d'innan,sannan ya janyo Mima jikinsa i'ta kuwa ta kanne mishi ido d'aya alamun nasarar da ta samu na shiga tsakanin aminan juna Murat da kuma Muta'z.
*Muta'z*
Kuka ya ke yi kamar k'ara min yaro yana mai kallon yarinyar da aka b'atawa rayuwarta yarinyar da bata wuce shekara takwas zuwa Tara.
Da sauri Mumtaz ta fad'a d'akin tana d'aukar rahoto da sauri Muta'z ya juyo don ganin mai d'aukarsa hoto domin ya hango hasken camera.
Ido hud'u sukayi da Mumtaz a dai dai lokacin da Mohd ya shigo gidan,shak'a Muta'z ya kaiwa Mumtaz Wanda sai da taji ajikinta sannan ya fara magana da kakkausar murya Ya ce".
"wallahi kika sake kika yad'a wannan abin to na lahira sai ya fiki jin da d'i,muguwa masharanciya kawai dai dai lokacin shi kuma Mohd yana k'ara d'aukar rahoto.
Alokacin kuma y'an sanda sukayi wa gidan k'awayenya,har lokacin Muta'z bai saki Mumtaz ba ya shak'eta sosai don Muta'z ya fita daga hayyacinsa gaba ki d'aya.
Mohd kuwa yana ta k'ok'arin kwatar Mumtaz yayinda Muta'z ya saki Mumtaz ya wancakalar sa i'ta gefe ya koma kan Mohd.
Tunda Mumtaz ta ke ba'ah tab'a yi mata makamanciyar wannan shak'ar ba.
Saboda yadda iyayenta suke sonta da k'aunarta kuma ga ta yarinya mai biyayya basu tab'a dukanta ba,sai yau gashi wani abanza ya shak'eta AKAN AIKINTA.
Da k'er aka b'an_b'are Mohd daga jikin Muta'z don Muta'z k'arfi ne dashi kamar na doki.
Ankwa y'an sandan suka mak'alawa Muta'z yana ji yana gani suka tafi dashi Office i'ta kuma yarinyar su Mumtaz suka kaita asibiti don duba lafiyar yarinyar don ba k'aramar wahala Tasha ba don har yanzu a sume ta ke.
*****
Labarai Fulani da mai Martaba suke yayinda gidan ma acike ya ke da y'an uwa saboda bikin d'an gata Muta'z.
Da sauri Fulani da Mai Martaba suka tashi hannun su dafe da k'irjinsu suna kallon Muta'z yadda y'an sanda suka yiwa d'ansu jina jina da duka,don har ga Allah basu San Muta'z d'an sarki bane saboda shi bai fiya shiga Media bama ballanta na har a ganeshi.
Salati suke suna sallallami ya yinda kowannensu ya rasa sukuni nan da nan Suka fita a mota don zuwa ganin d'an nasu Hanan ma kuka ta ke yi kamar ranta zai fita don ganin yadda a kayi wa d'an uwanta tilo rauni.
Sara masa y'an sanda suka shiga yi har sai da ya shiga babbar headquarters d'in,ranshi a b'ace ya zauna gaban babban Inspector y'an sanda.
Ran Mai Martaba ta gama b'aci kuma har lokacin ya kasa bayani,sai Fulani ce ta fara bayanin tana kuka"Akan wani daliline zaku kama mana d'an mu kuyi mishi wannan babbar illar"?
Sai asannan ne inspetor ya gane wa take nufi domin ya hango kamar da Yaron da suka kama d'azun Akan hukuncin fyed'e.
Sunkuyar da kai Inspector ya yi domin har ga Allah kunya ce ta kamasa,saboda bai San d'ansa bane Amman koma menene a dokar k'asa hakan shine dai_dai.
Nan fa Inspector ya fara yi musu bayani Akan abinda ya faru.
Alokacin kuma Inspector ya saka aka fito da Muta'z kuma alokacin Iyayen Fiddausi suka zo wato yarinyar da aka yi wa fyed'e.
Kuka suke sosai kamar ransu a game da lalatawa y'arsu rayuwa da a kayi suna tsinewa Muta'z tare da aibata shi,don tun jiya da'aka turata talla ba'ah sake ganin ta ba.
Kan Muta'z a sunkuye yana zubar da kwallar bak'in ciki a game da wannan jarabtar da ta same sa,ko kuma ya ce sharrin da aka yi mai.
Iyayen Muta'z sun san halin d'an su tun daga girmansa har yarintarshi don haka basu yadda d'an su ne ya Aikata haka ba.
Cikin Kakkausar Murya Mai Martaba ya kirawo sunan d'an nashi Ya ce"Muta'z ka fad'a min gaskiya duk da nasan kai mai gaskiya ne"Waye ya yiwa yarinyar nan fyed'e"?.
Kallon iyayen yarinyar Muta'z ya yi sannan ya fashe da kuka cikin kuka Ya ce Ka gafarceni Mai Martaba Wallahi Ni ne".
*Real Ummu Maher ce✍🏻*
💚🤍💚
🤵🏻♀🤵♀🤵🏻♀
*AKAN AIKI NA 2021*
🤵🏻♀🤵♀🤵🏻♀
💚🤍💚
Which means👇🏻👇🏻
*ABOUT MY WORK✍🏻*
Na
*🌹Rabi'atu B/Abdullahi*
(Ummu Maher)Miss green💚☘️
*_💫📚JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION💪🏻_*
*MURAT FANS*
Yana godiya bisa bashi hadin kai da kuka yi Fans😩🥲
*MUMTAZ FANS*
Tana godiya bisa yadda kuka bata hadin kai wajen d'aukar hoto da kuma rahoto📸📲📲.
*MUTA'Z FANS*
Yana bak'in cikin yadda kuka bawa Murat da Mumtaz goyon baya.😭😭
__,,,,,
Shafi na 38&39
Wani wawan Mari Mai Martaba ya kaiwa d'ansa Yarima,hannunsa yana kakkarwa ya nuna sa da yatsansa sannan ya ce"Muta'z sakayyar da zaka nuna min kenan?"na tarbiyyar da na yi maka,to daga yau na cireka daga cikin y'ay'ana kuma daga kar ka k'ara kirana a matsayin ubanka".
Inspector ga shinan duk wani hukunci da ya kamata a yi mishi a yi mai,tunda duk tsun_tsun da yaja ruwa shi ruwa kan duka.
Fulani kuwa kuka kawai ta ke yi tana Ce wa"Muta'z kada ka d'orawa kanka abinda kasan ba Kaine ka yi shi ba,don Allah ka fad'i gaskiya."?
"Fulani idan ki ka k'ara yi wa wannan yaron magana to sai dai a kulle Ku tare babu ruwana".
Da k'er Fulani ta fita tana kuka tana me Amman tana ji tana gani aka Tisa k'eyar Muta'z zuwa d'akin ajje masu laifi.
Koda suka i'sa gida kowa da abin da ya ke sak'awa acikin zuciyarsa Mai Martaba kuwa k'arfin hali kawai ya ke yi don babu yadda zaiyi ne shiyyasa ya d'orawa d'ansa laifi son gudun zagin talakawa,don yasan Muta'z bazai tab'a aikata hakan ba.
To wanene ya yi wa Yarima Muta'z sharri haka"? Koma wanene nan ba da dad'ewa ba Allah zai tuna asirinsa don Allah baya basin zalunci a doron k'asa.
*******
Mumtaz
" wai me ye yake damunki tunda kika dawo kin k'i cin abincin na ki gashi kuma yau kun dad'e."?
Shiru Mumtaz ta yi don sarai ta San dole sai ummanta ta yi mata wannan tambayar don tunda ta shiga d'aki bata fito ba sai yanzu don ta tsorata sa ganin abinda ya faru.
Sai ta samu damar ce wa umman nata"Wallahi babu komai kawai sai na gaji ne Aiki ya yi yawa,kuma kinga ban samu Damar zuwa bikin gidansu Hanan ba saboda Aiki."
Umman ta ce
"Ayya Allah sarki Allah ya bada abinda ake nema".
" Amin Umma"waini har yanzu banga Malam ya dawo ba".?
Dariya Umma ta yi sannan ta ce"Ai d'azu ya dawo ba kyanan Malam ya je k'auye saboda an yi musu rasuwa."
Allah yajik'an rai na ce sannan na koma d'aki na kwanta ina tunanin irin wannan rayuwa, har yaushe ne za'ah daina yi wa y'an mata da yara fyed'e a k'asar Hausa.?ki dubi yadda aka lalatawa wannan yarinyar rayuwa,Amman koma menene iyayenta sune da laifi.
Don rashin kulawa sa yaranmu yana saka irin wannan abin ya faru dasu.
******
Babu yadda Fulani bata yi ba akan mai Martaba yasaka baki akan asaki d'ansu Amman ya k'i dolen doliyarta ta hakuri,kuma gashi tana gadon asibiti saboda tunanin d'anta,shima Mai Martaban kawai dauriya ya ke yi shi kad'ai yasan yadda ya ke ji.
Mimee da Hajjo sunsha kuka har sun hak'ura gashi yanzu an d'aura Auren su.
A b'angaren Murat kuwa yaje sau biyu ya duba aminin nashi,agaban Muta'z ya nuna ya damu dashi yana fitowa kuma ya fara dariyar mugunta saboda ya hango nasara k'arara a game da abinda yasa a gaba.
An yan kewa Muta'z hukuncin zama na shekara sha hud'u14 tare da yanke mishi tara mai yawa.
Fulani da Mimee da Hajjo suna zuwa duba Mutaz akai akai Duk sanda sukazo sai sun tasa Mutaz suyi ta kuka,abin tausayi Mimee kuwa akwai sanda ta suma bayan sunje,Mutaz yana tausayawa Mimee yadda zata dad'e da Aurensa akanta don Hajjo ta ce babu wanda ya isa ya raba Auren matukar tana raye.
*******
"Kai Gaye gaskiya nifa zanje in Tina abinda ya faru saboda ko yanzu idan muka mutu sai Allah ya tambaye mu don mun cuci bawan Allah".
By
*Real Ummu Maher ce*
💚🤍💚
🤵🏻♀🤵♀🤵🏻♀
*AKAN AIKI NA 2021*
🤵🏻♀🤵♀🤵🏻♀
💚🤍💚
Which means👇🏻👇🏻
ABOUT MY WORK✍🏻
NA
*🌹Râbî'âtû ß/ Âbdûllahî*
(Úmmú Máhèr)Míss gréén💚☘️.
💫💫
*_🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION_📚🖊️*
https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl
_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_
*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*
*Shafi na 40&41*
Gaye ya ce"kai Morris ba ka da hankali ne zaka je ka tona mana asiri to karka soma wallahi don ni fyed'ewa yara yanzu na fara,kai kanka kasan idan Aure muka ce za muyi ina Mike da kud'in Auren?"Aure ya zama tamkar wani ciniki ka ga ai gwara mu more sosai kafin mu samu kud'in Auren tunda ga yaran nan ana sakinsu kamar wasu dabbobi.
"Kai Morris wallahi jiya Dana je wata unguwa naga yara mata suna ta wasansu a unguwa wasu da wando basu kuma babu wallahi baka ji yadda naji tausayin yaranba shin iyayensu kuwa suna sonsu kuwa?" Gaskiya ni dai bazan bar y'ay'ana a titi ba Wallahi,kuma indai iyaye basu daina barin y'ay'ansu saka_saka ba ba za'ah daina yi musu fyed'e ba"ya fad'i hakan yana kunna sugari yana zuk'arta kamar ya samu wata alewa.
Dai dai nan ya gama d'aukar video din su sannan ya yi gidan yayansa don kai mai rahoton wad'anda suka yi wa y'ar yayan nasa fyed'e.
"Innalillahi wa inna Ilaihi Raji'un"
"Yanzu daman ba yaron nan ne ya aikata wannan fyed'en ba?kai Amman mun cuce shi kuma sai Allah ya saka mishi."
Mahaifin Fiddausi ne ya ke fad'ar hakan yarinyar da aka yiwa fyed'e.
Shamsu wato k'anin Mahaifin Fiddausi ya ce"wallahi Yaya Allah ne ya toni asirinsu na taho zan tafi Aiki na hangosu a kusa da wani kango,daman kuma da ta mu dasu saboda mu y'an cumity da y'an Daba bama shiri so shiyyasa na taho don ganin abinda ke faruwa don ansha kawo mana k'ararsu i'sa ta ke da wuya na ji suna irin wannan maganar babu b'ata alokaci na fara yi musu video."
"kai Masha Allah yanzu saimu d'unguma muje police station don mu gudanar da wannan hujjar shima a sakesa a kama wad'annan azzaluman muna fukai masu
"Kai masha Allah" Allah ya k'ara tsare mana yaranmu".
Amin.
★<><><>★
"Haba Fulani wannan wani irin kuka ne da ya zama na kullum kada ki k'ara jawa kanki wata matsalar fa"?.
Shiru Fulani ta yi tana kallon mai Martaba ba tare da ta ce komai ba ta tashi ta koma d'akinta sannan ta cigaba da kuka yanzu sai d'anta ya yi shekara sha hud'u a gidan yari bai mori k'uruciyarsa ba?kai ko wanene ya yi wa d'anta sharri Allah ya Toni asirinsa da gaggawa.
Mai Martaba kuwa kallon Fulani ya yi sanda ta tashi ta koma d'akinta,Hawaye ne ya fito a idanun Mai Martaba ya goge idanunshi harga Allah shi yasan abinda ya ke damunsa akan wannan abin Ya Allah ya bayyana duk Wanda ya yi wa d'ansa Sharri har saukar Alqur'ani mai girma yasa a ke yi wa Yarima akan Allah ya toni asirin ko su wanene suka yi wa d'ansa sharri,tunda aka kulle Yarima Mai Martaba baya bacci saboda tunanin d'ansa.
Ya kalli gefensa ya tuno sanda gidansu yana cike Ga Hanan ga Muta'z sun saka Mai Martaba a tsakiya ga kuma Fulani da Mahaifiyarsa Hajjo kullum farlon cike ya ke da Iyalai, amman yau babu kowa,yana cikin wannan tunanin yaga kiran wayarsa yasa hannu da k'er ya d'auka.
"Iye..iye..iye to gani nan yanzu zanzo Allah na gode maka ganinan zuwa yanzu kuwa".
Da k'er Mai Martaba ya gama wayar yana had'a kalamai da k'er,kirawo Fulani ya yi awaya ya shaida mata abinda ya faru da gudu Fulani ta fito har tana had'a hanya da karun gidan suna ta kallon ta suna tunanin me yasa Fulani gudu haka Amman koma menene abin babba ne.
<><>,>,
Muta'z ya rasa farin ciki ya ke ko bak'in ciki Allah ya wanke shi cikin ruwan sanyi,da gudu ya rungume Fulani da Mai Martaba yana kuka,Fulani ta kalli d'an nata yau wata d'aya kenan da faruwar lamarin Amman gaba ki d'aya d'an nata ya canza gashin kansa duk ya cukur_kud'e abin tausayi.
An kamo su Gaye da Morris tambayar duniya suka cw ba wani ne ya saka suba sune suka aikata hakan da Kansu,Ai kuwa aka k'ulle su Suna Nadamar abinda suka Aikata.
Ban hak'uri Iyayen Fiddausi suka rink'a yiwa Mai Martaba duk da Basusan Muta'z d'an sarki bane sai yanzu,nan fa suka ringa yabawa Mai Martaba k'ok'arin shi na sakawa a kulle d'an shi duk da kud'in da ya ke dashi.
Nan fa y'an jarida suka cika wajen kafin ka ce me harda su Mumtaz a wajen suna mamakin yadda abin ya faru,Mumtaz ta yi k'asak'e tana kallon Muta'z duk daman kowa ya fad'i irin halin shi Mai kyau.
Ko wanni d'an Jarida ya saka lasi fik'arsa wajen bakin Muta'z don jin abinda zaice,Kawai sai kallonshi Ya kai kan Mumtaz wacce ta fara yad'a labarin Fyed'en da aka ce ya yi wa wata yarinya.
Kallon Banza Muta'z ya aikawa Mumtaz sannan ya zari lasifik'ar hannunta da k'arfin gaske Wanda har ciwo sai da ya jiwa Mumtaz, abinka da farar fata sai ga wajen ya yi jajir harda jini.
Sai da ya k'ara yi mata kallon banza kallon alamar zamu had'u sannan ya fara magana kamar haka..........."
Kash! naso inji abinda zai faru Amman idan na ga ruwan sharhi gobe zan k'ara Rubuta.
Daga
Ak'alamin
Ummu Maher
Vote
Share &Comments
*🪦✨AKAN AIKI NA✨🪦*
Book 2 sabon salo📖✍🏻
Na
_*Rêãl🌹 Oum Maher*_
(Mîss gréén💚)
*MATAR BASH💎*
📲MINAL MULTIMEDIA
https://youtu.be/NCrdsZmuh6E
Dan Allah kushiga ku danna Mana subscribe
_*📚JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION*✍🏻_
42/43
Jikin Mumtaz ne ya yi wani irin sanyi ganin kallon da Muta'z ya ke yi mata.
Harya gama jawabinsa bata k'ara sanin me ake tattaunawa ita dai taji tashin motoci,sai da kowa ya watse sannan taja k'afafunta da k'er ta bar wajen.
Har taje gida bata daina tunanin irin kallon da Muta'z ya ke yi mata shin d'aukar jawabin da ta ke yi ya zama laifi? Ko kuwa d'aukar jawabin da ta yi ne alokacin da a ka kirawo su zuwa gidanshi shine laifi?
"Ke Mumtaz lafiyarki kuwa ki ka zauna kina tunani haka?kuma me ya samu hannun ki harda jini?".
" Wallahi Umma bugewa na yi to shine wajen ya ke yi min zafi Amman yanzu zanje chemist d'in Sale ya yi min treatment d'in waje babu komai kada ki damu Umma wajen ya yi sauk'i".
Ta fad'i hakan ne don ganin yadda Umman ta damu sosai don tafi kowa sanin halin da iyayenta suke shiga a duk sanda suka ga wani Abu yana damunta.
★<><>★
Wani sabon biki a ka k'ara yi agidan mai Martaba don dawowar Shalelen d'ansa kuma Magajinsa,Murat kuwa yak'e kawai ya ke yi don yadda ya ke jin zuciyarsa kamar zata fashe duk shirinsa akan Muta'z ya war_ware to waye ya lalata mishi shirinsa yasan dai Morris da gaye Mimaa ce ta had'a su akan ce wa Suyi mishi sharrin da za'ah d'auresa har igiya ta yi rara Mimaa ce ta shirya duk wani shirin da aka yi shidai na shi taimakon kawai nuna b'oyayyen gidan Muta'z Wanda ya ke hutawa a ciki sannan ya sace mukullin gidan ba tare da ya gani ba.
Har aka gama shahararren bikin na Muta'z da Mimee,Murat bai iya ce wa k'ala ba daga baya ma sai ya sulale ya bar wajen tsabar bak'in ciki.
Shi kuwa Muta'z a yanzu nunawa Mimee so ya ke kamar me don ya yi matuk'ar tausaya wa yarinyar alokacin da aka kulleshi don da k'er Hajjo ta ke lallab'asa su ta fi gida don yadda ta ke matuk'ar rike cewa Hajjo wataran ma har suma ta ke yi.
Ita kuwa Mimee koda taga yadda Muta'z ya ke nuna mata sai ta dinga wani karai Raye kamar wata Kifi,shi kuwa har dariya ya ke mata don yadda ta ke siririya kamar wata silindium yadda kasan ba ta cin Abinci.
*Bayan buki*
Ko irin kunyar nan Mimee ba ta ji ba ta zage ta ringa yi wa Muta'z soyayya kamar ba Amarya ba kuma ranar farko,Shi kuwa kallon ta kawai sai ya fara tausayinta don matuk'ar ta shigo hannunsa ba za ta ji da d'i ba.
Hakan ce kuwa ta faru don a ranar Muta'z ya nuna mata ba maza bane kuma ba d'aya suke ba a fannin k'arfi da nuna Iko kiran sunan Hajjo kuwa ta yishi babu adadi shi kuwa ko a jikinsa don ita ce ta kawo kanta.
Duk da yadda tasha wuya bai hana ta k'ara son Yayan nata ba don yadda ya iya da ma ce babu dama zaka rantse da Allah daman ya saba harkar Amman ba haka bane kawai dai hallitarsa ce haka.
Koda safiya ta yi Mimee ba ta ga Yaya Muta'z ba koda ta kira wayarsa ma bata same sa ba,ta tashi daga ita sai rigar bacci ta lek'a ta Window ta hango fitar Motarshi daga gidan, kamar taje ta tsayar da motar Amman ya Riga da ya fita haka ta hak'ura ta nufa fridge don nemawa cikinta abin tab'a wa ba tare da ko Sallah ta yi ba ballanta na wankan Tsarki.
★<><>★
Sai da Muta'z ya zauna a Office d'insa sannan ya d'auki wayarsa rai a b'ace ya fara kiran wata number.
"Atiku wai har yanzu bata fito daga gidan bane don wallahi idan wata matsala ta faru akan harkar nan to Ku kuka sa kanku".
Ya fad'i hakan cikin tsawa" Oga ka d'an k'ara jira yanzu ne lokacin fito warta daga gida don haka kad'an k'ara jira.
Cikin fushi ya kashe wayar domin ya shirya komai a lokacin da ya shirya amman suna son b'ata mishi lokaci,Don ya shirya nuna wa Mumtaz kuskurenta na yad'a abinda bata da masaniya akai.
Mumtaz kuwa baiwar Allah tana cen bata San what going on ba.
"Kai Uwata kinga yadda kuwa Abayarnan ta yi miki Kyau kamar wata Balarabiyar Asali".
Malam ne ya ke fad'in hakan ya yinda ya ke kai k'osai bakinsa Ita kuwa Umma tana k'ara sa sakin K'osan.
Dariya Mumtaz ta yi Wanda ya ke k'ara fito da ita, ya yinda ta ke jin fad'uwar gaba sosai aranta ta ce"Malam Amman yau da wuri zan dawo don Aikin babu yawa."
"To uwata Akula da hanya Allah ya bada sa'ah".
" Amin Malam sai na dawo" ta fad'i hakan tana d'aukar k'osai guda d'aya tana ci,Mumtaz kenan akwai zuciyar kula da iyaye d'aukar Albashinta 4 kenan yanzu,da k'er Mlm ya ke tilasta mata don ta siya sutura saboda sutura itace mutum babu yadda za ta yi dole ta ke siya don itama ta yarda sutura ita ce mutum. kuma tana siya musu kayan abinci sosai harda mai da magi Lipton madara kai harda au kwai.
Ni kuwa Ummu Maher na ce muma Allah ya bamu y'ay'a masu son mu Amin👏🏻👏🏻.
Tana fitowa daga gidan ta kalli hannun dama da hagu sai ta hango wani d'an adaidata da alama tafiya zaiyi,da Sauri ta tsayar dashi ta alama da baki.
Tsayawa ya yi sannan ta shiga ta fad'a mishi inda zata je.
Sunyi nisa sosai a cikin tafiyarsu kawai sai taga ya juyo ya shek'a mata Abu a hancinta tun daga nan bata k'ara sanin inda kanta ya ke ba.
*Oum Maher ce*
_*don Allah ku ta yani da Addu'ah akwai wani Abu da ya ke damuna na keson in samu,Allah ya bamu duk abinda muke nema na Alkhairi Amin.*_
*_✨AKAN AIKI NA_ ✨*
✍🏻Ummu Maher(Miss green)💚
44/45
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION*
Tunda Mumtaz ta tashi daga dogon baccin da ta yi sai taji gaba ki d'aya an d'aure ta akan kujera,ko iya motsi ba ta yi, gashi d'akin gaba ki d'aya duhu ne,ko hannunka ba zaka iya gani ba hankalin Mumtaz ya kai matuk'a a tashi saboda batasan ko ina aka kawota ba.
Ta dad'e acikin wannan hali sannan taji k'arar bud'e k'ofar d'akin,wani k'amshi ya daki hancinta wanda ta ke tunanin ta tab'a jinshi amman bata san a inda ta sanshi ba.
Tsoronta ne ya k'aru a lokacin da taji mutumin yana takowa har zuwa inda ta ke,amman kafin yazo Wani irin haske mai wuyar gani ya haske d'akin,da d'ewar da na yi acikin duhu sai yasa idanu na suka zama kamar na makauniya,na rintse idanuwa naji gaba ki d'aya so nake in bud'e idona inga a i'na na ke,wata kakkausar Murya na ji,muryar namiji wadda itama na ke tunanin kamar na tab'a jin irin muryar,da k'er na bud'e idona don in ga waye wannan.
"İnna lillahi wa İnna İlaihi Raji'un."
"Na san za ki yi mamakin ganina ko?to ba abin mamaki bane don kinga haka ta faru da ke,kuma ki daina mamaki domin yanzu zaki gane tsakanin aya da tsakuwa."
Wasu hawaye ne masu zafi suka fara ambaliya a kyakkyawar fuskata murya ta na rawa Na ce"Don Allah kada ka cutar dani saboda nasan ahalin yanzu iyaye na suna cen suna nema na,don Allah kada ka lalatamin rayuwata kamar yadda ka lalata rayuwar yarinyar.........
Wani ruwan sanyu me kamar k'ank'ara Muta'z ya watsamin har cikin bakina,abinda ban k'arasa maganar kenan ba,wani numfashi mai wahala na furzar sannan na fasa wanu irin kuka.
"A'i ba ki yi kuka ba har yanzu domin kuwa keda farin ciki har abadan abadan,sabida baki isa ki shiga rayuwata ki gurb'ata min ita ba sannan ki ce zaki zauna lafiya".
" Zan cen iyayenki kuma kada ki damu domin inason in d'an d'ana musu yadda nawa iyayen suka ji alokacin da sukuma na ki iyayen suke cikin farin ciki,kinga kuwa dole kema yanzu na ki iyayen suji a jikinsu."
Ya fad'i hakan yana mai janyo dogon gashina da ya warware ya fad'o a gadon baya na,K'ara jan gashin nawa ya yi da k'arfin gaske yana magana da kakkausar murya.
"Kinyi gangancin shigowa rayuwata har ki ke ganin ce wa ya kamata ki yi min sharri,to wallahi tallahi sai na koya miki hankali ta inda ba zaki yi tunanin k'ara yi min sharri ba nonsence kawai".
Ya saki gashin na wa sannan ya fita daga d'akin ya kashe hasken, da k'arfin gaske ya rufo k'ofar ji ka ke gammmmmm....tsabar rufe k'ofar da a ka yi da k'arfi sai da na kusan sakin fitsari a wando.
Sai da na kwana a zaune babu ci babu sha,har lokacin sallar asuba ya yi ban yi bacci ba,tsanar Muta'z na ji a raina da kuma mummunan halayensa,na shiga tsinemai ina magana da k'arfi don so na ke yi ya ji,don duk muguntar da zaiyi min na saka azuciyata baki na bazai tab'a rufuwa ba.
A b'an garen su Mlm kuwa sunyi neman duniya amman ba suga Mumtaz ba, har wajen Aikinsu sai da Mlm ya je amman babu wata maganar da aka samu akan Mumtaz,hankalin Mlm da Umma ya yi matuk'ar tashi sosai,yadda suka ga dare haka suka ga safiya Mlm na kuka Umma na kuka,haka suka kwana suna Sallah suna kaiwa Allah kukansu Akan b'atan y'arsu Mumtaz.
Har Police station Mlm ya je ya kai report amman shiru ka ke ji abin har mamaki ya ke bawa Su Mlm yadda y'ar tasu ta b'ata kamar b'atan d'an mutum ba.
Tun asuba Umma da Mlm suka k'ara fita yawon neman y'ar tasu Hamma har yamma har dare babu labari,Akan dole suka hak'ura zuciyoyinsu kamar zasu fashe don tsabar bak'in ciki,amman da ya ke masu tawakkali ne sai suka fauwalawa Allah tare da rok'onsa akan ya bayyana musu y'arsu abar sonsu wato Mumtaz.
Sai da yamma ta yi alokacin na fara gajiya har na suma tsabar yunwa,na ji an watsamin ruwa, gaba ki d'aya kayana suka jik'e sharkaf ni kuwa sai haki na ke ina kiran sunan Allah.
Haske ya k'ara kunnawa a d'akim wnda yasa na fara tunanin ko a lahira na ke,saboda abin ya yi min yawa ga ruwa ga idanuna da suka koma kamar na makauniya.
Kallona ya shiga yi yana dariya,acikon zuciyarshi kuwa kawai tausayani ya ke ji na d'auko yarinya har gidansu,ganin irin tuanin da ya fara zuwa zuciyarsa kawai sai ya yi saurin ba sarwa,sannan yazo ya kin ceni daga mugun k'ullin da na sha.
Gaba ki d'aya na fad'o jikinsa yarab,tsabar galabaitar da na yi,wani yamm ya ji ajikinsa tsigar jikinsa ta fara ta shi,da sauri ya saki mumtaz ta fad'i ajikin bango,na fara wani irin nishi mai wahalarwa..
_Kuyi manage saboda jikin nawa da sai a hankali._
*Ummu Maher ce*
*AKAN AIKI NA*
Book 3
Ummu Maher(miss green)
46/47
Yanzu Mlm haka zamu saka idanu muna kalllon Y'ar ta b'ata an rasa gane wad'anda suka d'auke mana y'armu,gaskiya yau har Gidan radionsu saina koma don su naga kamar basu damu ba,Umma CE ke ta sababinta tana yi tana share hawaye da gefen zaninta,Malam kuwa yana gefe ya saka handkacif yana goge hawayenda suka zamar masa sabo.
Iya wahala Mumtaz tana Shanta awajen Muta'z Wanda yake jin har yanzu baiyi ramuwar da yake son yi ba,don haka yau ya shirya muguntar da zaiyi mata Wanda baza ta tab'a manta irin muguntar da ya yi mata ba har ta mutu.
Yau ma kamar kullum da kanshi ya kawo mata abinci,Mumtaz ta d'aga idonta da k'er wad'anda suka yi mata nauyi tsabar wahala ta Kalli abincin sai dai duk da yunwar da ta ke ji ba zata iya cin abincin ba saboda wani mugun yaji da Ake zubawa acikin abincin don sai ka kusa zuba fitsari saboda azabar yaji.
Cikin tsawa ya fara yi mata magana "d'auki abincin kici ko kuwa yanzu na gana miki mummunar azaba Y'ar jaridar k'arya mai d'orawa mutane sharri, yau sai kinyi Dana sanin had'a min sharri domin muguntar yau tafi ta kullum.
Tun kafin ya gama maganarsa Mumtaz ta fara cin abincin tana kwallah don sai taga yajin ma yafi na kullum,kai Muta'z ya karanci tsabar mugunta,har ta gama ci yana kallon fuskarta tare da k'ara tsanarta tunda ta kunya tashi a idon duniya dole ne shima ya kunyata ta.
Bata Ankara ba ya fizge kwanan tare da turo mata ruwa nan ta d'aga ta fara kwankwad'a sai da ta shanye sannan ta ajje jarkar a nan ta fara wani bacci mai wahala,shi kuwa Muta'z wani mummunan kallo ya bita da shi tare da yin wata mik'a kamar zai yi aikin k'arfi.
Mumtaz kuwa baiwar Allah sai baccinta ta ke yi a d'akin baccin wahala,shed'an yafara bugawa Muta'z ganga nan fa ya fara aiwatarwa da Mumtaz mummunan k'udurinsa akanta.
Cikin baccin wahala ta fara jiyo wani bak'on lamari yayinda ta fara jiyo wata irin azaba a k'asanta,wani yunk'uri ta yi don ta tashi taga menene?
Abun da ta gani ne yasa gabanta wani mummunan fad'uwa tana rintsa idanunta jin kamar zata mutu saboda azaba,wani irin kuka ta saki mai ban tausayi tana son tashi Amman ta kasa,Muta'z kuwa baima son aduniyar da yake ba don yayi nisa baya jin kira,don tunda yake bai tab'a zuwa wannan duniya mai matuk'ar dad'i ba.
Kuka Mumtaz ta ke tana tausayin kanta dana iyayenta,tun tana k'arama suke kula da ita tare da bata tarbiyya dai_dai gqargwado Amman yau gashi wani abanza ya lalata mata rayuwarta wajen amfani da kud'in da ya ke dashi wajen yi mata fyed'e.
Sai da ya gama ne ya fara kuka da idanuwansa don tunda yake bai tab'a zina ba,yayi zama cikin turawa Amman bai saka ya watsar da tarbiyyar da iyayensa suka yi masa, yana fita daga d'akin ya kirawo wata number tare da bada umarni,shi kuma gaba Ki d'aya ya fita daga Gidan,da k'er ya kawo kansa gidansa yana had'a hanya kamar Wanda yasha wani Abu.
Taji sanda aka bud'e k'ofa Amman bata san ko waye ba don ko d'aga idonta bata iyayi tsabar kukan da taji gashi ko tafiya ba zata iyayi ba saboda azaba.
Wani Abu suka busa mata kamar ranar da suka d'auko ta har suka kawota k'ofar gidansu bata San anzo ba.
Alokacin kusan k'arfe 8na dare ne,suka ajje ta a hankali a soron gidansu,suka taho a hankali cikin sand'a suka shiga mota,alokacin Malam ya dawo daga Sallah ya hango fitowarsu daga Gidan tun kafin ya iso wajen suka shiga motar suka jata da k'arfi suka fita daga layin baki d'aya.
Salati Malam ya saka bayan ya haska soron ya ce"Mumtaz ke ce me suka yi miki,Innalillahi Wa inna Ilaihi Raji'un."
Ummu Maher ce.
*AKAN AIKI NA*
_Ummu Maher (Miss green)_
48&49
Tsananin tashin hankali ranar Mlm ya yi shi,don ganin y'arsa tilo a k'asa kamar gawa baisan yanada wani k'arfi ba, sai yau don gaba ki d'aya ya d'auki Mumtaz ya yi cikin Gidan da ita yana kwallawa Umma kira,da gudu itama ta fito har tana tuntub'e jin ya ambaci sunan Y'arsu Mumtaz,Tayashi rik'e Mumtaz ta yi tana cike da tsoro don ganin y'ar tasu kamar gawa a d'akinta ta kwantar da ita tana faman yayyafa mata ruwa Mlm kuwa yarasa tudun dafawa ga y'arsu Amman tana cikin wani hali Wanda basai an gaya maka irin wahalar da tasha ba,ta rame ta k'anjame abun tausayi wata kwallah Malam ya share yana k'ara kallon fuskar Mumtaz wadda ta ke cikin wani hali na wahala.
Wata irin ajiyar zuciya Mumtaz ta saki a hankali jin hannun Ummanta ajikinta don koda bata bud'e idonta ba tasan waye don bazata tab'a manta sanyin jikin Mahaifiyar taba,da sauri ta rungume Umman tana k'ara sautin kukanta,Malam ma cike da tausayi ya ke kallonsu.
"Don Allah Umma kada kuga laifina Wallahi d'auke ni a kayi aka kaini wani gida aka yi ta azabtar dani AKAN AIKI NA,wallahi Umma kodon samun kwanciyar hankalinku daga yau nabar Aikin Jarida don samuwar kwanciyar hankulanku keda Mlm,sai ta k'ara rungume Umma d'in tana k'ara sakin wani irin marayan kuka na tausayin kanta dana iyayenta.
Likita Malam ya kirawo ya duba Mumtaz d'in tare da yi mata allurai nan da nan sai kuwa bacci ya d'auke ta awajen,Malam yasan Mumtaz zata iya tashi tana jin yunwa don haka ya siyo mata Shayi da baredi hakan kuwa a ka yi tana tashi daga bacci cikin dare Umma ta bata shayin da buredi ta cinye tas kamar mayunwaciya,Umma kuwa tana zaune tana kallon y'ar ta cike da tausayi,koda ta gama kwanciya ta k'ara ba ita ce ta tashi daga wannan baccin ba sai k'arfe 9na safe,tana tashi Umma ta gama dafa mata ruwan zafi,ai kuwa taji dad'in ruwan zafin don ta gasa jikinta don haryanzu tana jin azaba dauriya kawai ta ke yi.
Umman ta kula da haka shiyyasa ma kafin ta fito daga wankan har ta had'a mata abin karyawa tare da ajje mata magani har ma da kayan canzawa,Mumtaz kuwa ta ji dad'in ruwan zafin don ta gasa jikinta sosai kuma Alhmdh ta fara jin dad'in jikinta don har tafiyarta ta fara dawowa dai_dai abinci ta ci sosai nanmq kamar mayunwaciya Umma kuwa tana ta kallonta har dai ta kasa hak'uri tare da cewa"İn ce dai basa baku abinci Mumtaz don daga yadda ki ke cin abinci ya isa ka tabbatar ballanta na duk wanda yaga ramarki yasan dole kinsha wuya".
"Ruwan fiyowata ta k'urba mai d'an sanyi tana jin bugun zuciyarta na k'aruwa na tsoro tare kuma da tausayin iyayenta dama ita kanta," kinyi shiru Mumtaz don wallahi ni nasan wad'annan mutanen koma su waye to basu da imani,an mayar da talaka tamkar wani banza ayi ta cutarsa ana zaluntarsa don an san babu mao tsaya masa,to Ai akwai Allah shi zai shige mana gaba,kuma koda baki fad'a ba Mumtaz daga yau kin daina aikin nan tunda abin ya soma da haka,kai duniya da mutum ya ce zaiyi gaskiya shikkenan ya zama nama awajen mutane,Allah dai ya shige mana gaba."
Har Umma ta gama maganarta bance da ita k'ala ba don ni kad'ai nasan halinda zuciyata ta ke ciki,araina kuwa ina k'ara jaddada rashin tausayi irin na Muta'z baya tunanin shima zai haihu?koma dai ba haka ba ai yana da k'annai me ya ke tunanin zai faru idan hakan ta faru y'an uwansa tabbas tasan hakan sai ta faru ko ba yauba wanda ya yi da kyau ma ya ya k'arke ballan tana wanda bai yi da kyau.
Ni kuwa Ummu Maher na ce Allah ya shiryar samu cikin shiriya madai_ daiciya Amin.
*GERMANY*
Shiri ya ke sosai na komawa gida don ba k'aramar murna ya yi ba jin Hajiyarsa ba ta k'ara yi masa magana Akan Auren da ta ce za ta yi masa ba,gefe d'aya kuma na zuciyarsa yana k'ara jin dad'i don ayau zai had'u da sanyin idaniyarsa,duk da Rabonsa da ya yi waya Manager na wajensu Mumtaz har ya manta don Aiki daya sha masa kai.
Baba megadi yana lek'owa ya hango ubangidansa wato Mukhtar ya washe baki yana jin dad'in ganinsa,sannu da dawowa ya yi mai sannan suka gaisa cikin mutuntawa don yana matuk'ar ganib darajar Megadib don mutamin arzik'ine,haka shima Baba megadin yana matuk'ar ganin darajar Mukhtar don mutumin kirki ne tsabanin Hajiyarsa da igiyar kud'i ke janta don ko gaisuwarsa bata fiye amsawa ba.
Da murna ya shigo gidan nasu don rabonsa da ganin mahaifansa da k'annansa har ya manta,shiyyasa ya ke Allah² da ya gansu sannan ya tafi wajen sanyin idaniyarsa.
Yana shiga main farlon gidan nasu ma'ana babban farlonsu ya hango Hajiyarsa cikin kwalliyar wani tsadaddan leshi mai matuk'ar kyau da tsada sam bai kula da wanda ke wajanba ya taho da sauri yana mai jin matuk'ar jin kewar Hajiyarsa ta sa,Sakinat ce ta shi haushi da bak'in ciki da suka gama cika mata zuciya don ganin ko kallonta Mijin nata baiyi ba,duk da shi har yanzu bai san da cewa Anyi masa Aure ba,Tsananin zafin da Sakinat taji ne yasa ta buga uwar k'ara don taka ta d'in da Sir Mukhatar ya yi wanda shi ba da gayya yayi ba don bai ganta ba harga Allah.
*Ummu Maher ce✍🏻.............*
*AKAN AIKI NA*
_Ummu Maher(Miss green)_
50&51
Juyowa Mukhtar ya yi da sauri don jin ihu a bayansa,sai a sannan ya kula da Sakinat y'ar Gidan k'anin Babansa da ke Abuja.
"Sakinat yaushe ki kazo gari ?haushi da b'acin rai suka taru suka yi wa Sakinat yawa don haka sai ta yi shigewarta d'akin Hajiyar Mukhtar,Y'ar dariya Hajiya ta yi sannan tabi bayan Sakinat don tana son Sakinat Sosai don ita da uwar Sakina Aminai suke tun kafin su Auri y'an gida d'aya.
Sororo Mukhatar ya d'aga kafad'a alamar ko a jiki na ya yi sannan ya wuce dining ya fara bud'e kulolin abincin tuni ya zauna ya cika tumbinsa sannan ya shiga d'akin Hajiya,Sakinat tana zaune kusa da Hajiy a ta cika fam kamar zata yi kuka.
Nuna masa waje Hajiya ta yi Sannan ta ce ina son ka nitsu kaji abinda zan gaya maka,Tun yanzu zan fad'a maka duk d'an da baya farantawa iyayensa sunansa matacce don yana Raye ne Amman kuma matacce ne.
Yanzu zamuje sama Alhaji yana nan daman don yana wani aiki ne daka dawo ban CE ka shiga ba Amman yanzu zamuje,haka Mukhtar ya din ga bin Mahaifiyarsa har zuwa sashen Babansa.
Gaishesa Mukhtar ya fara yi sannan ya tambayesa ya aikinsa ya ce komai Alhmdh,Nan dai Abba ya fara nasiha da jawabi sannan ya wuce kai tsaye ya gaya masa Auren da sukayi masa ba tare da ya Sani ba,tunda Abban ya fara magana kansa A k'asa yana jin kansa kamar zai tsage,koda Abban ya ga haka sai ya cewa Hajiya su tafi,bayan sun tafi ne Abban ya cigaba da yi masa nasiha tare da yi masa albishir d'in duk Wanda ya keso ya kawo masa ita shi kuma in dai mutuniyar kirki ce zai Aura masa,Amman sai ya kula da hakkin k'anwarsa kuma matarsa,Sannan Abba ya ce mai zai fara zama Anan Gidan kafin suga yadda zaman zai kasance,Don gidansu yana cen komai an zuva da kuma masu kula da Gidan kafin a tare.
Koda Sir Mukhtar ya fuskanci Abbansa a zuciyarsa ya CE indai zaka yadda da zab'ina Mumtaz to nima zanso Sakinat kuma zan sota tare da yi mata adalci.
Hajiya kuwa shirya y'arta ta yi sosai,suna yi Sakinat tana mita Hajiya ta mik'o mata wani turare wai ta fesa,ta amsa tana k'un k'uni Hajiya ta ce.
"Yanzu Sakinat a haka zaki mallaki mijin kina sakarci?" To bari kiji matuk'ar kinason Mukhtar ya soki to sai kin koyi abubuwa da dama don janyo hankalinsa ya soki.
Haka Hajiya ta ringa yiwa Sakinat nasiha har ta d'auka tana yiwa Hajiyar godiya,don Sakinat yarinyace shekararta19 don haka Hajiya ta bada k'aimi wajen saito ta kan Hanya,don Hajiya akwai ilimin zama da miji,kissa kisisina da dai sauransu.
*MUTA'Z*
Yana zaune idonshi Alumshe kamar yana bacci Amman ba bacci ya ke yi ba,yana tunanin yadda har ya iya rashin imani wajen ketawa yarinya haddin ta,Shin yanzu idan K'anwata a kayi wa haka yaya zanji?wani Abu ne ya tokare masa k'irjinsa tsantsar tausayin yarinyar ya ke ji Sosai,a haka har Mimee ta sameshi tana kallon yadda ya zurfafa a tunani,ko kusa Mimee irin matan Nanne da idan miji yana wani hali ta kansu kawai suke ko ya mutu ko yayi rai,Apple d'inta ta d'auka tana ci tana lumshe ido don yanzu ta zama Miss Apple.
*MUMTAZ*
Ta warware sosai ta yi Y'ar k'iba don yanzu Baba yana sana'ah Babansu Amal ya turo mai kud'i masu kauri ya tada shagonsa damk'am da kaya yana sa'ah,kuma su Amal d'in ma sun kusa dawowa.
Tunda abinnan ya faru tsakanin Muta'z da Mumtaz shikkenan ta fara zazzab'in dare ta rasa na menene ga wani uban kwad'ayi.
*MISS GREEN CE........*✍🏼
*AKAN AIKINA*
_*Ummu Maher*_
(Miss green🌱)
52&53
......Umma ta ce"yanzu Mumtaz haka zaki yi ta zama kina kwad'ayi ba zakici abinci ba sai kwad'ayi?"Umma wallahi kwad'ayi kawai na keji ki barni in samu inci faten nan don Allah,taliyarce mutum gajiya ya ke yi da ita.
"To gashi je ki siyo kifi ki saka ciki nasan zaifi dad'i,da fara'ata na amsa ina godiya ina cewa Umma ta zama Hajjaju,dariya ta yi sannan ta ce" Allah yasa Y'ar nan don maka akwai dad'i,ina dariya na saka hijab d'ina sabo Wanda Mlm ya siyomin sabo ne ruwan kalar kwanduwar kwai,kasamcewa ta ma d'an hasken fata sai nayi kyau sosai,gashi Hijab d'in irin mai facemask ne,sai yayi min kyau kamar nayi roling da man wando irin bujennan sai nayi kamar matashiyar Ba indiya.
Wani irin fad'uwa gaba na ya yi ganin Sir Mukhtar a k'ofar gidanmu yana jikin window d'in motarsa yana face d'in k'ofar gidanmu cikin wata tsadaddiyar motarsa jip mai kyau kalar bak'a.
Fara'ata na rage sannan na wuce shi sai dai harga Allah nima banji dad'in wuceshi d'in da na yi ba,don ko babu komai Sir Mukhtar bai cancanci haka agareni ba bisa yadda ya yi namijin k'ok'ari wajen kula dani da iyaye na.
Da k'er ya fara magana har muryarsa tana sark'ewa kamar wani mai jin tsorona.
"Mu.."
"Mu.."
"Mumtaz"
Juyowa na yi ya yinda na hard'e hannayena saman k'irjina sannan Na ce.
"Na'am"
Cikin siririyar voice d'ina mai matuk'ar da d'i,kallonsa kawai na ke yi yadda ya canza ya zama fari ga k'ibar da ya k'ara,da ka ganshi kasan kud'i sun zauna ajikinsa.
"Don Allah don Annabi Mumtaz ki yi hak'uri ki ya feni nasan na yi matuk'ar yi miki laifi,da abinda na aikata miki Amman wallahi hakan ba zai k'ara faruwa ba wancen ma tsautsayi ne please".
Ya had'a hannayensa kamar zaiyi kuka,ni kuwa na waskata bakina gefe tare da fari da idanu kuma har yanzu hannayena suna k'irjina.
To sak'anin Masoya babu mai shiga don matuk'ar ka shiga ma Kaine zaka ji Kunya.
To hakan CE kuwa ta faru tsakanin Mukhtar da Mumtaz biyo bayan hak'uri da Sir d'inta ya dinga bata sai ga Mumtaz har tana wangale baki,hakan kuwa ba k'ara min sanyaya zuciyar Mukhtar yayi ba duk burinsa bai wuce yaga Mumtaz da iyayenta suna cikin farin ciki ba.
Da sauri Mumtaz ta shiga gida don gayawa mata Sir Mukhtar ya dawo yana waje,yanzu zai shigo su gaisa,Umman ma ta yi farinciki sai dai har yanzu bata daina d'ar_d'ar da al'amarin Mukhtar d'in ba.
Kud'i ya ajjewa Umma sannan yayi mata albishir da zai turo magabatansa a satinnan,Umma ta yi farinciki sosai tare da sanyawa Mukhtar d'in albarka.
......Hajiyar Mukhtar taja dogon numfashi Sannan ta kalli Maman Sakina ta ce"kinga abinda nake gaya miki ko?yarinyar da ita da Matsiyatan Iyayenta sun gama da Mukhtar.
Hajiyan Sakina ta ce"kinga tunda har ya dad'e bai fito daga cikin gidanba me zai hana mutafi koma me zamu yanke idan munje Gidan ma yanke.
_*Ummu Maher ce👌🏻*_
*_Ummu Maher_*
*AKAN AIKI NA*
54&55
.........Wani wawan Mari Hajiyar Mukhtar ta wanka wa d'an nata sannan ta nuna shi da manuniyarta ta ce.
"Sha_sha"
Mara sanin darajar iyayenka wato Mukhtar har yanzu daman baka daina kula wannan matsiyaciyar yarinyar ba,y'ar matsiyata jikan matsiyata,har yaushe ne aka d'aura maka Aure da zaka dinga bibiyar wannan munafukar yarinyar,shiyyasa Dana ga ka fita na bika don ni yanzu har tsoro kake bani.
"To wallahi kaji narantse ka sake ka k'ara komawa wajen wannan tsinanniyar yarinyar saina Tsine maka!Saina tsine maka!!
Wani jiri Mukhtar ya fara ji da k'er ya kai kansa d'akinsa yana kuka wiwi kamar yaro.
Mumtaz kuwa washegari tana ta zuba idanu koda zata ga Sir Mukhtar shiru haka kawai gabanta ya dinga fad'uwa,dauriya kawai ta ke yi Amman gaba ki d'aya bata jin dad'in jikinta.
Da daddaren ta daure ta tafi Asibiti,sai dai tayi matuk'ar Dana sanin zuwanta asibiti domin kuwa an shaida Mata tana d'auke da ciki har na wata biyu.
Ihu Mumtaz ta saka a asibitin da k'er wata nurse mai suna NAWWARA ta cikin Doctor nawwara na Ummu Maher, hak'uri ta dinga bata sannan Mumtaz ta bata lbrn abinda ya faru da ita bayan wata 2da suka wuce na saceta din da akayi,sai dai bata fad'a mata kowa Nene ba.
Bayan ta dawo daga asibiti ta shige d'akinta tana tunanin rayuwarta, Umma CE ta shigo mata da indomie.
" Maza ta shi Kici abinci shiyyasa ma na dafa miki ita nasan zaki ji dad'inta.
Tausayin iyayenta ne ya kama ta kamar ta yi musu kuka.
Ciwo fa ya sako Mumtaz a gaba yau ciwo gobe lfy, Umma kuwa ta ringa zabga mata magungunan musamman na shawara don ta ce Shawara ce da ita.
Har darbejiya da lemon tsami ake mutsika mata ta sha Abu dai sai gaba ya ke yi,gashi Babu Mukhtar babu dalilinsa,abun duniya yayi wa Mumtaz yawa,a kullum kwanan duniya sai ta tsinewa Muta'z a bisa cutar rayuwarta da yayi don yana matsayin d'an mekud'i.
Sand'a_sand'a Mumtaz ke yi har ta fito waje alokacin Mlm bai dawoba,cen ta fita wani chemist da ke bayan unguwarsu.
Sallama ta yiwa likitan sannan ta amsa ta shigo ciki,Maganin ciwon ciki ta CE ta bata,ta d'auko mata sannan ta bata kud'in ta fito.
Tana shigowa Gidan Umma na fito wa daga d'akinta.
"Mumtaz!ina kika ne na lek'o ban ganki ba?"
"Eh wallahi"
Na je na siyo paracetamol na lek'o kin fara bacci shiyyasa,ta fad'i hakan tana bud'e randa don shan maganin.
D'aki ta koma ta fara bacci,Mlm yana shigowa ya rufe musu gida,sannan yayi musu albishir su Amal,zasu dawo gobe murna sosai sukayi suna addu'ar Allah ya kawo su lfy.
*Washegari*
Mumtaz ta fito daga wanka kenan taji an rufe mata idanu,koda ba,ah gaya mata ba tasan k'awarta ce Amal,juyowa tayi suka rungume junansu har kuka sai da sukayi.
Umma ta fito ta shimfid'awa Amal ta barma ana ta hirar yaushe gamo,Mumtaz tana ta kallonsu cikin so da k'auna.
Ranar dai ansha hira Mumtaz tana tunanin gayawa Amal halinda take ciki har dare yayi kowa ya kwanta.
Da daddare Mumtaz ta sake komawa chemist aka had'o mata gabje gabje waidon duk ta samu sauk'i.
Tun cikin dare mararta ke mata ciwo Amman ta kasa ta yarda kowa agidan gudun kada ta katse musu baccinsu.
Da k'er baccin wahala ya kwasheta sai k'arfe 8na safe na tashi,da k'er na d'auki buta zan shiga ban d'aki,ban lura da randar dake kusa dani ba kawai na fad'a kan randar,Salati na ke jiyowa a samana ga wani Abu yana bina a k'afafuna kamar jini.
Wannan shine Labarin Mumtaz da Tun farkon littafin muka fara da labarinta.
*Miss green CE✍🏻*
💞💞💞💞💞💞💞
*AKAN AIKI NA*
(Book 4)
WRITING BY.
UMMU MAHER.
(MISS GREEN💚🌱)
WATTPAD NAME
RABIATU222.
*DEDICATED TO AKAN AIKI NA FANS &UMMU MAHER PALACE.*
No.56to60
......Sai da na yi kwana biyar a asibiti sannan na warware har yanzu bana iya had'a idanu da su Mlm saboda har yanzu ina matuk'ar jin kunyarsu akan abin da na janyo musu Wanda nima k'addara ta ce hakan.
Amal ma tazo ita da Mamansu Amal har kuka ta yi da jin abinda ya faru munyi kuka nida ita kamar babu gobe a haka har muka bawa zuviyoyinmu hak'uri,Allah ma daya taimakeni cikin ya fita da yaya zanyi da d'an shege,wannan abin shine ya ke sakawa in k'ara godewa ubangiji tare da tsinewa Muta'z kullum.
Abinda Mumtaz bata Sani ba bayan tafiyarsu asibiti yazo Muta'z yazo gidansu yafi sau babu adadi abin ba k'ara min tada hankalin Muta'z ya yi ba,kada dai ace yarinyar nan sun tashi ta yaya za'ayi ya nemi yafiyarta son yasan ba k'aramin aik aika ya yi mata ba,kuma yasan idan har bai nemi yafiyarta ba Allah bazai tab'a yafe masa ba kuma shima wataran sai anyiwa y'ay'ansa haka.
Amal ta dawo daga asibiti don d'aukarwa Mumtaz kaya tana cikin bud'e Gidan taji muryar namiji a bayanta,saurin juyowa ta yi sai taga mutum kamar balarabe a gabanta shagala ta fara yi da kallonsa,har sai da ya fuskanci hakan sannan ya yi gyaran murya yana ce wa.
"Am Nanne gidansu Mumtaz,y'ar jarida?."
"Eh nan ne lfy Mlm?"
"Daman yau kwanana biyar ina zuwa Gidan a kulle Allah dai yasa lfy?"
"Wallahi bata da lfy ne tana hospital Amman da sauk'i".
Gabansa ne ya yi wani mummunan tashi cikin in ina ya CE.
" Me.Me me."
"Me ya sameta?"
D'an Jim Amal ta yi sannan ta ce.
"Zazzab'ine".
Oky Allah ya sauwak'e muje in dubata motar Muta'z suka shiga sannan suka tafi asibitin,suna zuwa Gaban Muta'z ya ringa fad'uwa don harga Allah tsoron had'uwarsa da Mumtaz ya ke yi,kallon sunan asibitin ya yi sannan ya yi murmushi suka shiga.
Cak Muta'z ya tsaya sannan ya ce wa Amal idan ta je ta kirawo mai Baban Muta'z, hakan kuwa a ka yi tana shiga ta fad'awa Mlm ya fito gaisawa suka fara yi sannan Muta'z ya fara yi wa Mlm bayani ce wa shine Yarima mai jiran gado,ba k'aramar murna Mlm ya yi ba wai yau shine Agaban Yarima.
" Baba da man nazo ne Neman wata alfarma daman naga y'arku Mumtaz tun bayan wata 1 da ya wuce kuma naji ta kwantamin to shine na keso Ku bani Auren ta!.
Das gaban Mlm ya yanke ya fad'i,Gaskiya ne da aka CE Mahak'urci mawadaci wai yau Yarima ne ya ke son y'ar sa Mumtaz tabbas yana jin lbrnsa mutumin kirki ne sosai,kuma ya ji lbrn wannan asibitin ma nq shine n karan kanshi.
Amman sai dai kash!Mumtaz An lalata mata rayuwarta ta yadda ba za'ah iya b'oye abinda ya faru da ita ba.
*MISS GREEN CE✍🏻...💔for life*
*✨ _AKAN AIKI NA_ ✨*
By
Ummu Maher (Miss green)
_🙏🏻never put the key to your happiness in some e'lse pocket😭_
No.54&55
.......__D'akin Mlm ya yiwa Muta'z jagora suka shiga,Mumtaz tana zaune tana shan shayin da Amal ta had'a mata kawai sai taga Muta'z yana bayan Mlm ya yi kyau cikin farin yadi k'al kamar audiga,sajensa sai walk'iya ya ke kamar hasken Zerhra sai dai ya rame sosai kana ganin sa zakaga hakan,gaban Mumtaz ne yayi mugun fad'uwa ta zabura zata tashi tana nuna sa da manuniyarta sai dai kome ta tuno kuma ta koma ta zauna tana rik'e da kanta daya kusa rabewa gida biyu.
Mlm ya fuskanci akwai wani Abu don haka ya ce"Mumtaz wannan sunansa Muta'z yazo ya duba kine!"Muta'z kuwa bakinsa na rawa ya CE"sannu Mumtaz, Allah ya sauwak'e ya baki lfy ".Amin Amal ta amsa mishi yana fad'in hakan yayi sauri ya fita yana kukan zuci yana tausayin abinda ya aikatawa Mumtaz baiwar Allah.lallai babu Wanda ya cancanci ya Auri Mumtaz saishi domin kuwa ko babu komai shine ya lalata mata martabarta na y'a mace Wanda ko wacce mace indai budurwa CE ta ke lallab'ashi tare da alkintasa ko don tsira da mutuncinta.
Yana fita ya kirawo wani yaronsa mai suna Musa ya yi mai bayanin komai nidai Ummu Maher bansan komenene ba Amman naji ana zancen gini,A sati 1,da Mumtaz ta yi a asibiti har Muta'z ya sa anfara ginin Gidan su Mumtaz gadan_gadan abunka da kud'i sai gashi gini har an kusa gamawa duk da ba iya Gidan su bane,har wani kango na kusa da Gidan su Mumtaz d'in ya had'a ya siya sai gashi gida ya fito d'od'ar yayi kuma girma.
Duk abinda ke faru wa Mlm ya Sani Umma CE kawai bata Sani ba hatta Amal ta Sani,Muta'z ya nemi alfarmar a k'ara wa su Mumtaz sati d'aya akan Wanda ta yi sannan ya ware kud'i masu yawa don akaita d'akin Hutu,koda Umma ta samu Mlm da maganar jikin Muta'z yayi sauk'i kuma gashi har yanzu babu zancen Sallama,sai Mlm ya ce mata eh ai sun fad'a masa sai ta k'ara sati d'aya,daga haka Umma bata kara magana ba ta cigaba da kula da y'arta Mumtaz, don halin da ta ke ciki tana buk'atar kulawa sosai.
Har yanzu tsoron Muta'z Allah dai yasa Mumtaz bata fad'awa iyayenta abinda ya faru tsakaninsa da ita ba,sai dai har yanzu mamaki ya ke yi da yaji babu Wanda yayi masa magana koda kuwa a fuskane don kullum sai sun had'u da Mlm kuma kullum Muta'z cikin yiwa Mumtaz hidima ya ke yi kamar Wanda baisan zafin kud'i ba.gefe d'aya kuma yana k'ara son Mumtaz da ta rufa masa asiri ba tare da ta tuna masa ba.
*MURAT*
Ayanzu fa Murat da Meema abin duniya ya ishesu gashi yanzu komai ya dagule musu don har yanzu basa shiri tun akan abinda ya faru,don shi Murat gani ya ke yi laifin Meema ne ita kuma Meema tana ganin laifin Murat,tofa wannan ne ya had'a musu wata gagarumar matsala don tsakanin Murat da Meema an samu matsala,don ayanzu Murat ya koma kula wata aminiyar Meema suna lalacewarsu,don Meema ta tab'a ganin su awani hotel inda hankalinta ya tashi sosai,har ta yiwa Murat barazanar nunawa duniya vedion sharrin da a kayiwa Muta'z, hankalin Murat ya tashi sosai ya dinga Neman su shirya da Meema ita kuma Meema ta CE Indai yana son su shirya sai dai ya Aure ta,domin kuwa ta gaji da yawon duniya babu shiri Murat ya amin cewa Meema Amman zuciyarsa bata so hakan ba don dai babu abinda zai iyayine,don baiso Auren irinsu Meema yafi son ya Auri Y'ar Gidan mutunci.
*MUTA'Z*
Alhmdulillah ayanzu an kammala ginin Gidan su Mumtaz komai na more rayuwa anzuba musu d'akin Mumtaz kuwa kamar d'akin matar gwamna saboda kyau gaban mirror kuwa kayan shafa ne kala_kala,ga kayan kwalliya turare da dai sauransu gida dai masha Allah.
Mota guda Muta'z ya bada da driver don tuk'a iyayen Mumtaz da ita kanta sarauniyar Mumtaz,wadda har yanzu bata San wainar da ake toyawa ba.koda aka d'akosu daga asibiti Mumtaz kallon motar kawai ta ke yi saboda kyau da tsarinta ga A/C mai dad'i aciki,koda ta shiga motar sai da taja dogon numfashi don motar k'arshe CE ta had'u sosai.da sosai.
Mamaki da rud'a nine suka ziyarci Mumtaz ganin Gidan su ya koma kamar a k'asar waje,Salati ta farayi a fili tana kallon Umma da Mlm tana cewa"Umma kalli gidamu?wani azzalumin ya karbe ya gine mana shi don rashin tausayi.
Notice!zaku ga na bar GRP kuyi hak'uri laifin ogane don baya so,Amman zan cigaba da tyiping insha Allah nagode!nagode!dafatan kun fahimce ni🙏🏻ina missing dinku mussaman Amira da Bilkisu da Kaltum khanna masoyan littafin Akan Aikina na gode na gode,Mumtaz tana gaisheku,duk Maison magana dani sai ya turomin sak'onsa ta private domin bana cikin GRP.🙏🏻🥰
*ILOVE U ALL MY PANS🥰🙏🏻😭*
*Ummu Maher CE*
_*✨AKAN AIKI NA*✨_
By
Ummu Maher (miss green)
Ina gaida masoyan wannan littafi na akan Aikina aduk inda kuke,Akan Aikina fans GRP ina gaisheku ban manta daku ba duk da bana cikin GRP.
No.56&57
Umma ma mamaki ne kwance fal fuskarta ta kalli Mlm tana son k'arin bayani,"Muje Mlm ya CE wa Su Umma sannan ya bud'e get d'in Gidan suka shiga,Mumtaz da Umma bin Mlm kawai sukeyi kamar rak'umi da akala har suka shigo babban farlon Gidan,Mlm ne ya yi musu alamar su zauna cikin kujerun da ke farlon,a d'arare Umma da Mumtaz suka zauna suna ta faman mamaki kujerun ma kad'ai abin kallo ne.
A nitse Mlm ya fara basu labari tunda ga farko har k'arshe ya k'are maganar yana kuka,don tunda ya ke bai tab'a tunanin ko irin wannan Gidan zai shiga da aunan aiki ba,ballan tana ya zama gidansa,babu abinda zai cewa Muta'z sai dai Allah ya saka mishi da alkhairi,don da Mlm ya so yayi taurin kai wajen amsar Gidan Amman kuma daga baya yaji babu dad'i mayar da hannun kyauta baya.
Wani Abu ne ya tsaya wa Mumtaz azuciyarta wai yau Wanda ta tsana arayuwarta wai shine ya Gina musu gida irin wannan?ta kalli Mlm tana matuk'ar jin tausayin iyayenta don tasan basu San munanan halayensa ba da basu amshi wannan Gidan da ya yi musu ba amatsayin rufe musu baki sai dai tasan Mlm bashi da kwad'ayi ko kad'an kawai dai ya amsa ne don ko babu komai yasan filin Gidan sane kuma bayan hakan tasan Mlm baya maida hannun kyauta baya.
Umma ma ta yi murna sosai tana ta saka mishi da alkhairi,Mlm ne ya raka Mumtaz d'akinta a saman bene Wanda ya gaji da had'uwa don irin benen nanne mai rawn kafin ka isa saman,bata gama mamaki ba sai da ta shiga d'akin nata,d'akin ya gaji da had'uwa ta CE"wow so nice"Amman da sauri ta rufe bakinta tuno da cewa Muta'z ne ya saka mata komai ba d'akin sai taji duk bak'in ciki ya kewaye ta.koda ta bud'e sip d'in da ke manne acikin d'akin taga kaya sun kai set hamsin a shirye a goge acikin Sip d'in masu matuk'ar kyau Riga da siket dogayen riguna da k'anan kaya maau kyau da tsari,ga gaban madubi kayan shafa kala_kala.
Da daddare suna zaune kan Dining suna cin abinci suka ji nocking, Mlm ne ya CE Mumtaz ta je ta duba,a hankali ta tashi ta bud'e k'ofar farlon,gabanta ne ya yi wani irin bugawa ganin Muta'z a tsaye yana kallon ta da rinannun idanunsa,yana sanye da wata d'anyar shadda coffee, kasan cewarsa mai haske ba k'ara min kyau suka yi masa ba.
Murmushi ya sakarmin sannan ya rab'a ta gefe na ya wuce ni kuma na rufe k'ofar ina binsa da wani mummunan kallo,aduk sanda naga Muta'z sai naji wata muguwar tsanarsa acikin raina don bana manta sanda ya yi amfani da k'arfinsa a matsayinsa na d'a namiji ya yi min fyed'e,har yau ban San me yake damuna ba da nake b'oyewa iyaye na abinda ya aikata min,tsoronsa?ko me na keji da na kasa fad'awa iyaye na.
Haye wa sama na yi ina sharar kwalla acikin akan kyakkyawar face d'ita,da kwallan tausayi Muta'z ya Bini har na shige d'akina na haye lumtsumemen gadona ina kuka mai cin rai,Muta'z ya cuce ni yanzu idan nayi Aure me zance da mijina matuk'ar ya Gane ni ba budurwa ba CE? Wannan tambayar kullum na ke yiwa kaina Amman na kasa samun amsa,sai dai amsa d'aya na ke bawa kaina Muta'z ya cuceni.
Tun daga ranar sai Muta'z yazo gidanmu da daddare sunyi hira da Mlm kuma ayanzu ya samowa Mlm aikin wani company d'aya daga cikin company Mai Martaba wato Mahaifin Muta'z.
Alhmdh don ko ayanzu munyi ban kwana da talauci,awani yammaci ne Mlm ya sameni a d'akina ina karanta wani novels mai suna ASANADIN ABAYAR SALLAH,na marubuciya Ummu Maher, na ji dad'in littafin sosai ina cikin karatunne Mlm ya shigo,na yi saurin sakkowa daga kan gadon ina gaishesa,ya samu waje ya zauna ni kuma ina k'asa azaune na sunkuyar da kaina,gabana sai fad'uwa ya ke yi,na jiyo muryar Mlm yana cewa.
"Mamana magana na keson yi da ke ta fahimta don nasan halin Mamana idan abin bai miki ba ki fito ki gaya min?don ba zan miki dole ba sai dai ,a irin wannan rayuwar da muke ciki Abu ne mai wahalar gaske samun namiji mai addini,nutsuwa da kuma kamala, wannan yaron Muta'z ne ya ke sonki kuma harya turo magabatansa don ayi mishi iso don ya fara zuwa zance".
Da sauri na tashi tsaye dafe da k'irjina Wanda ya ke sama da k'asa tsabar tashin hankali,Na CE" Baba bazan iya Auren saba saboda bashida hali mai kyau.....
Ummu Maher CE.
Vote
Share
And
Comments.
*_💚💘AKAN AIKI NA💘💚_*
Book 4 last
Na
Ummu Maher(Miss green🍀💚)
58&59
Ina kaiwa nan na koma d'aki da gudun gaske ina kuka,matuk'ar aka takuramin akan Auren Muta'z to babu makawa nasan mutuwa zanyi don ba zan iya rayuwa da azzalumi ba,mak'iyi na,macuci,mazinaci.
Mlm ya kalli Umma sannan ya ce"Bazan tab'a yiwa Mumtaz auren dole ba,ina ganin wannan yaron da mutunci fiye da yadda kike zato,don kafin in sanarwa Mumtaz sai da na yi bincike sosai akan yaron don,yaron d'an manya ne Babanshi ayanzu haka shine sarkin da ke mulkalmu,sarki me adalci da sanin yakamata,zanso Mumtaz ta Auri Wannan yaron badon kud'insu ko wani abuba,A'ah sai don tarbiyyarsa da nagartarsa."
"Ki rarrashi Mumtaz bazan tab'a yi mata zab'en tumun dare ba a matsayina na mahaifinta,kuma nasan wataran itama za tayi alfahari da wannan Auren,don na hango so da kuma tausayin Mumtaz a cikin kwayar idanunsa,don haka zan cigaba da addu'ar Allah ya tabbatar da alkhairi Amin.
Kullum sai Muta'z yazo gidanmu amman bai tab'a ganina ba,don da naji k'arar motarsa na ke guduwa don ayanzu ba wai son ganinsa ne ba nayi ba,a'ah kawai da naganshi sai inji gabana ya yi muguwar fad'uwa.
Ga Amal kullum tana gidanmu muna shan hira,ita ma hirarta a kullum bai wuce in Auri Yarima Muta'z ba,don a cewarta munyi matuk'ar dacewa da juna,don kullum idan yazo suna shan hira shida Amal,kuma kullum baya gajiya da bawa Amal sak'o ta kawomin,har waya sabuwa dal ya kawomin.
***
Ranar wata asabar ina zaune ina shan iska a farfajiyar gidanmu,ina sanye cikin riga da siket ns atamfa holand na tufke gashina,na siraro d'an kwalin ta tsakiya gashina ina shan iska,sai naji ajikina kamar ana kallona,saurin juyowa na yi sai da gabana ya fad'i na daburce har na yarda d'ankwalina a k'asa,na yi saurin duk'awa don d'auko d'ankwalin,sai na ji hannun mutun dab dani na sunkuya shima ya sunkuya tare muka d'auko d'ankwalin hannayenmu na gogar na juna,babu abin da na tsana irin had'a idanu da Yarima Muta'z, don wani abu na ke hangowa acikinsu wanda ya ke sakawai gaba kid'aya inji kwarjininsa ya bai bayeni,don duk tsiwar dana d'auko zanyi mai sai naji ta tafi.
Cikin voice d'insa mai dad'i ya ce
"ykk My pricess"
Saurin d'ago kaina na yi sannan na tashi zan tafi,ya ruk'o hannuna gaba d'aya naji na fad'a kan k'akk'arfan k'irjinsa,muka had'a ido ban san sanda na tashi da sauri na shiga gida ba,gaba na yana dukan³,shi kuwa shafar gashin kansa kawai ya yi yana jin kansa kamar wani sabon ango.
MURAT
______
***
"Meema wallahi kin cuceni,kin cuci aminina da kika k'ara bani kwarin guiwa wajen cutarsa da kuma cin amanarsa,Allah bazai tab'a barin mu ba,matuk'ar hakkin Muta'z yana kanmu,kuma ki sani Meema bazan tab'a auren wulak'an tacciyar mace irinki ba,wacce ta gaji da duniya,duniya ta gaji da ita......
" kai Murat sai ta zancen ka wallahi tallahi daman kai can Azzalumine macuci,don haka kada ka sake cewa wai ni ce na saka kan hanya?"kuma ka ke tatsuniyar cewa ba zaka Aureni ba,kasan abinda ma bazai tab'a yiyuwa bane?"ko kana so?ko baka so?dole sai na Aureka,domin kuwa a lokacin daka rabu dani to fa awannan lokacinne zan toni asirinka kowa yasan waye kai".
Wani kyakkyawan mari Murat ya kifawa Meema sannan ya nuna ta da yatsar sa ya ce"Wallahi Meema kinyi k'arya ki gama lalacewarki sannan ki ce wai yanzu in Aureki,bazan tab'a Auren Karuwa,fasik'a irinki ba,don haka ki nemi me Aurenki Amman ba ni ba.
Wata shewa Meema ta yi sannan ta ciro wani fefen vedio ta ce"wannan vedion Murat shine rayuwarka kuma shine Ajalinka bazan tab'a bari wannan vedion ya kufcemin ba,domin ina da irinsa yafi 100,kuma ka duba wayarka ka gani.
Kuyi hak'uri anyi min rasuwa ne shiyyasa na yi tyiping kad'an.
Taku har kullum Ummu Maher💔
Miss grèèn💚.
kunga yanzu bana grp so duk masuyin comments yana isomin.
Ku yad'a
Sannan
Kuyi comments✍️
*_AKAN AIKI NA_*
By Ummu Maher
Miss green🍀
60
....wallahi Fulani ina masifar son yarinyar tare da tausayinta,Amman kinsan wani abin mamaki?
Fulani ta girgiza kai alamar a,ah.
"Amman yarinyar nan ko ganina bata San yi bansan ko me na yi mata ba,don Allah Fulani kije gidansu ki farauto min zuciyarta ko Allah zaisa ta so ni.
Shiru Fulani tayi har ya gama maganar sa,tana mamakin Yarima Muta'z ko yaushe ya yi Auren oho?har ya ke son k'ara wani Auren Amman sai ta daure ta ce" ni kuwa wannan wata yarinya ce mai sa,ah irin wannan Yarima kamar kai a ce an samu yarinyar da zata k'i ka?ko dai wani Abu ka yi mata da bata sonka?ni dai nasan babu macen da zata had'u da kai ta ce bata sonka,don komai kana da shi na nagarta ilimi,addini,tarbiyya,kyau,nasaba,hak'uri,da kuma yiwa iyayenka biyayya.
Don haka irinku mata suke so,don haka na yi maka Alk'awarin nemo maka Aurenta kuma Insha Allah komai yazo k'arshe.
Rungume Fulani Yayi sannan ya manna mata kiss a kumatunta,don bashi da tamkar Mahaifiyarsa.
"Hajjo in zo ki rakani wajen Fulani ta damamin wannan furar ta ta,mai dad'i ke Idan mutun yazo gurinki saiki cikani da wasu magarya alhalin ba k'oshi zanyi ba,"to uwar masifa muje kisha gero ma ba fura ba".
Suna shiga sashen Fulani suka ga Murat yana zaune suna ta hira da Fulani,Mimee ta sunkuya ta gaishe da Fulani cikin shagwab'a tace"don Allah Mama ki dama min fura insha wallahi indai bansha fura ba sai inga kamar cikin jikina zai zube wallahi."
"Ah ai kuwa yanzu Muta'z ya gama shan nasa,bari akawo miki yanzu kinji y'ata,ba a b'ata lokaci ba Mimee ta shiga shan furar ta babu k'akkutawa,don tunda ta samu ciki yau kusan wata 7 kenan take masifar shan furaDon fura tana d'aya daga cikin abinda take masifar son sha tunda ta samu ciki.
....tun safe Umma da Mlm suke shiri don Muta'z ya gaya musu zuwan Mahaifiyarsa,Amman Mumtaz tana cikin d'akinta ko lek'owa bata yi ba,don wani azabar zazzab'i da ciwon kai ta ke ji.
"Mumtaz!Mumtaz!!INA kika Shiga ne tun safe kina d'aki don mugun halinki da ki ka koya to wallahi maza maza ki sakko tun safe nake aiki kina.....
Maganar ta ce ta tsaya jin Takun shigowarsu Muta'z da Mahaifiyarsa,rasa inda zata sakasu ta yi Mahaifiyar Muta'z kawai ta tsaya tana kallonta tana yi mata wani irin kallo.,.
To Ku biyoni anan gava don jin wani irin kallo Mahaifiyar Muta'z ta ke yi wa Umma,Mahaifiyar Mumtaz?shin me ya janyo wannan kallon?.
*Ummu Maher CE*
Share&cmnt.
[11/22, 15:19] 🥰Ummu Maher🏕️⛱️: *_AKAN AIKI NA_*
By
_Ummu Maher_
_*Miss green*_
Wattpad
Rabiatu222
64&65
.....Da sauri Fulani ta rungume Umma sannan ta CE"Jamila daman kina raye tun kina jaririya aka yarda ke aka nemeki aka rasa,Allah mungode maka da Bayyanarki don babu tantama Jamila ke ce don kamarku da mai Martaba har ta b'aci wallahi".
Mamaki da firgici ne suka kama Umma sosai don ita dai tunda ta taso a rayuwarta bata San kowa ba sai Mlm da Iyayenshi sai dai basu b'oye mata komai na rayuwarta ba,sun gaya mata cewa tsintarta a ka yi a gefen hanya.
Da sauri Fulani ta d'auko wayarta ta kira Hajja don ta shaida mata.
"Wai wani jarababben ne ya ke damuna awaya ne?idan na ce kada a siyomin waya sai an siyomin to nidai babu ruwana wallahi da munafinci"...
Maganarta ce ta tsaya cak,jin abinda Fulani ta ke fad'a hannu na rawa Hajjo ta saki wayar ta fad'i k'asa wan war, Meema ce da ke kwance saman kujerarta tana shan fura ta hango Hajjo zata fad'i k'asada k'er ta tashi don taro kakar ta.
Hajjo kuwa da kanta taje wajen
[11/22, 20:15] 🥰Ummu Maher🏕️⛱️: Mai Martaba don shaida masa abinda ke faruwa don hankalinta ya tashi sosai da jin wannan maganar,shima cikin tashin hankali ya biyo Hajjo suka fito dogarai suka biyosu don bud'e musu k'ofa,cikin sauri Mai Martaba ya fara tuk'a motar cikin gaggawa,rabonda ya yi tuk'i kusan shekara 20 kenan.
Da kwatancen Fulani Allah ya kawo su Hajjo lfy harma da Meema,kai tsaye suka shiga cikin Gidan,hankalinsu gaba ki d'aya ya karkata ga maganar Momi.
"Inna lillahi wa inna ilaihi Raji'un"
Muryar Hajjo ce ta karad'e d'akin sannan ta tafi da saurinta ta rungume Umma tana mai godewa Allah da yasa taga y'arta tun kafin ta mutu don a kullum addu'arta taga y'arta don duk duniya tana son ta tunda kuma ta haifeta aka ga irin son da ta ke yi mata shikkenan aka tsani yarinyar har sai da aka had'a baki da wata baiwa aka yardar mata da y'a,sai da aka gane kuma Allah ya Toni asirinta ta fad'i gaskiya sun had'a baki da kishiyar Hajjo don ita bata da y'ay'a,Mahaifiyar Meema ita ce ta biyu sai Kuma Mahaifiyar Mumtaz Auta kenan wadda ta b'ata tun tana k'arama.
Ko da Mlm ya ce su Hajjo su bada wata shaidar bayan kama da Umma ta ke yi da Mai Martaba,nan ta ke Hajjo ta tashi ta ce Umma ta ja hannun rigarta akwai tawadar Allah,haka kuwa a kayi tana bud'ewa kuwa sai ga tawadar Allah.
Da sauri Umma ta tashi ta k'ara rungume Hajjo tana mai jin dad'in ganin Mahaifiyarta duk da bata Santa ba sai yanzu,Addu'ah Mai Martaba ya fara yi sannan aka fara hira gwanin ban sha'awa,Muta'z ma yazo nan ya dinga jin wani farin ciki a cikin zuciyarsa don daman tun ranar da ya fara ganin Mumtaz yasan cewa jininsa ce don yadda ya ke sonta kamar rai.
Yawan maganar da akeyi ne ya tasheni daga dogon baccin Dana samu,ina tashi naji ciwon kan gaba kid'aya babu shi, daga ni sai wata doguwar rigar bacci pink colour tana da siririn hannu,gashin kaina ya bazo baya duk ya warwatse alamun daga bacci na tashi,na fara sakkowa saga upstar ahankali cike da nutsuwa na fara kiran Umma!Umma!!.
Tunda na fara sakkowa mutanen wajen hankalinsu ya dawo kaina kowa yana jinjina wannan halittar mai kyau da tsaruwa,Fulani kuwa cewa ta yi Lallai dole Muta'z d'inta ya gigice don duk yadda ya kai da kyau to fa wannan yarinyar k'arshe ce.
Ita kuwa Meema tun kafin ma tasan wacece taji tana wani matsanancin kishi da Mumtaz, don Meema da taga hankalin Muta'z duk yana wajen Kallon Mumtaz ai takanas ta taso ta zauna kusa da Muta'z Amman bai san Meema tana wani Abu wai shi kishi ba.
Ummu Maher ce
*Vote*
*share*
Comments👌🏻
*_AKAN AIKI NA_*
By
_Ummu Maher(Miss green🍀)_
Littafaina
Uwar gidana
Auren dole
Ruhi d'aya
Inayatullah
Farouk
Kaddarar rayuwa ce
Asanadin Abayar Sallah
Akan Aikina
Jameeler
Doctor Nawwara
_gaskiya ina jin dad'in yadda kuke nuna min k'auna mussam duk masu yimin post.
*Kaltum Khanna*
*Dr Amira*
*Nabiha Aminu*
*Rukayya gawata*
*Hjr L Sadiq*
*mmn teddy*
*Momin Shukura*
*Nana M sha'aban*
*Fauziyya d s*
*Autar Mama*
*Ummu najma*
*koise baby*
*Bilkisu*
Da duk masoya na wad'anda ban samu damar ambato sunansu ba.
Please nayi mistake tun a baya na page maimakon in saka 70 na saka 65har sau biyu yanzu zan tashi a 70.
70
Da sauri Hajjo ta taso ta rungumeni tana cewa"Allah Sarki jikata gakinan kamar Ku d'aya da Muta'z."
Gaba d'aya ban gane inda zancen nasu ya dosa ba sai da Mlm yayi mata bayanin komai sannan na tashi da Sauri na rungume Hajjo harda Mai Marta ba ina kuka Ashe Mahaifiyata tana da gatanta haka ta zauna cikin talauci da k'uncin rayuwa sannan ta zauna ba tare da tasan danginta ba ko kuma ta nemesu ba, sai yanzu da Allah ya kawo k'arshen komai.
Ai aranar Hajjo a gidan ta kwana ana ta hira ni kuwa kaina na kan cinyar Hajjo a haka har bacci ya d'aukeni Umma kuwa suna ta bada labarin yadda aka yi aka yarda Umma na a bola.
Ban San ya akayi Hajjo tasan abinda ke tsakanina da Muta'z ba,ai kuwa Hajjo cewa ta yi a satinnan za'ayi Auren don hankalin Muta'z ya kwanta shikkenan ya had'a Auren y'an uwan juna.
Ranar kamar in Zane tsohuwar nayi don na lura fitinanniyar tsohuwa CE,Mai Martaba kuwa ya ce Ummana ta dawo Gidan sarauta kusa dashi yana ganinta hankalinsa zai fi kwanciya,Umma ta CE yayi hak'uri soon zata dawo.
Yau kusan sati 1 kenan Muta'z baya gari,don ya kwana biyu baizo gidanmu ba,nima ban damu ba don kwata kwata baya gabana har yau idan naganshi wani irin mugun haushinshi na keji sai dai kwata kwata bana iya had'a idanu dashi don tsoron I'danunsa na keji.
Fulani kuwa sai Jana a jiki ta ke yi,na rasa me yasa nake son matar don tana burgeni sosai.
***
Duniya fa ta juyawa Murar sosai don Meema ta rikita lissafinsa don ta ce matuk'ar tana numfashi dole ne ya Aureta,a yanzu kuwa har ya kai kud'i harda sarana babu Wanda ya Sani,saboda tsabar zubar da aji Meema da kanta ta amshi kud'inta harda na sadaki kuma an saka sati2masu zuwa asha biki,bak'in ciki kuwa Murat yasha sa wannan wani Irin Aure zaiyi babu albarka manya ko kad'an a ciki,gashi don tsabar abin kunya wai amarya CE ta ke amsar kud'in Aurenta da kanta.
A yanzu kuwa wasan b'uya suke yi da Muta'z don besan abinda zai CE masa idan sun had'u ba,ayanzu yayi nadamar duk abinda ya yiwa Amininsa kuma d'an uwansa Muta'z yasan Allah bazai tab'a barin hakkin Muta'z akansa ba,ya zama dole ya nemi yafiyarsa ko Allah zai dubesa,don yasan Auren Meema k'addararsa ce don Bai tab'a tunanin zai Auri mace Y'ar duniya kuma fasik'a ba.
A duk duniyar nan babu yarinyar da ya ke so, kuma yake k'auna kamar Hanan ita kad'ai ya ke so ya mallaka a matsayin matarsa uwar y'ay'an sa sai dai yasan Hanan ta yi mishi nisa Nisan da bazai iya kamota ba,don fasik'i baya Auren wadda ba fasik'a ba,yafi kowa sanin halin Hanan yarinya ce mai ilimi,tarbiyya,da kuma biyayya,uwa uba addini,ada kafin Hanan tasan halinshi tana matuk'ar yi mai biyayya a matsayinta na k'anwarsa har Allah yasa suka fara soyayya sai gashi ya b'ata rawarsa da tsalle akaran banza,don babu wata mace mai mutunci da zata so ta Auri mazinaci ,dumu² Hanan ta kamashi shida Meemi suna aikata masha'a da Allah ya Toni asirinsa ranar Aikenta Muta'z yayi wajensa Allah yasa tayi mummunan gamo tun daga ranar Hanan ta tsani Murat kamar ta caka mai wuk'a ta kashe shi.
***
Rana bata k'arya sai dai uwar d'iya taji kunya,yau CE ranar da aka kawo kud'i na baiko da kud'in saka ranar Muta'z da Mumtaz,ranar Mumtaz tasha kuka kamar ranta zai fita,don ma sauk'inta har yanzu bata ganin Muta'z har yanzu bai dawo ba da sai ta tona mishi asiri kowa yasan halinsa,ita kanta bata San yadda za ayi ta yi rayuwar Aure da Muta'z ba,mutumin da ya b'ata mata rayuwarta ya yi mata fyed'e harda kullin cikin shege,idan ta tuno da wannan abin yana matuk'ar b'ata mata rai sosai, kuma tana tunanin tona mai asiri zumuncin da ke tsakanin iyayensu ya lalaci ga Hajjo da ta shige gaba akan komai,matuk'ar ta Sani to wallahi sai ta tsani Muta'z tsana mai tsanani.
Wata biyu aka saka alokacin Meemi ta haihu,kuma har yanzu bata San halin da ake ciki ba na maganar k'arin Auren mijinta,Hajjo ta CE a k'eleta da kanta zata fad'a mata har sai ta haihu sannan za'a fad'a mata.
Ni kuwa kallonsu kawai na ke yi don abinda Muta'z ya min sai na rama Wanda yafi nashi ma,Amman ni kad'ai na barwa zuciyata don sai ya gane nima macece.
*Ummu Maher CE*
*_AKAN AIKI NA_*
By
_Ummu Maher(Miss green)🍀_
Ina gaishe Ku y'an GRP dafatan duk kuna lfy👏🏼daga Ummu Maher dinku.
Pg 71&72
....yau aka kawo lefena akwatina set12 mak'ota da y'an uwa sai tururuwar shigowa suke yi ganin lefena,kowa kuma da abinda ya ke fad'a wasu da basu San alk'armu da su Muta'z ba cewa suke munbi son zuciya munbi kud'i sauran aje a siyar damu.
Ni kuwa basu San da za'a janye Aure na da Muta'z to da tabbas da nafi kowa jin dad'i don ban San me yasa ba ?koda shigowa gidanmu yayi b'oyewa na keyi don bana son in kalli kwayar idonsa don abubuwa da yawa nake gani acikinsu.
****
Cikin dare Mimee ta fara nak'uda dak'er taje d'akin Muta'z ta tashe shi alokacin ta fara fita daga hayyacinta,suna isa emergency aka karb'esu da gaggawa aka shiga da ita.
Da sauri Muta'z ya zaro wayarsa ya kira Fulani harma da Me Martaba don ya sanar musu halin da ake ciki,Har Mumtaz ya kira sai da tayi ringing 5 sannan ta d'aga yaji muryar Mumtaz kamar sarewa don dad'i,don haka yayi gaggawar sanar mata halin da suke ciki.
Duk da k'iyayyar da ta kewa Muta'z Amman tayi matuk'ar tausaya mishi don tasan halinda maza suke shiga idan matansu suna labour.
Da sauri na sakko k'asa na sanarwa Hajjo da Umma halin da ake ciki,cikin rud'ewa Hajjo ta d'auko hijabinta mu ma muka shirya sai Hospital.
Har mukaje bata haihu ba hankalin kowa ya tashi har ana tunanin ko ayi Mata operation, sai Allah ya sauke ta lfy ta haifi Y'arta mace Ku Kakkyawa me kama da Mahaifinta,nan da nan asibitin ya kaure da murna,Amman duk da halin da Mimee ta ke ciki kallon banza ta dinga bina dashi,ina ganin haka nayi tahowa ta gida,INA fitowa daga asibitin naji an janyo hijabina ina juyawa naga Muta'z a tsaye yana murmushi,had'e raina nayi na juya amman bai bani dama ba kawai sai ya rungumeni a k'irjinsa,ban San me yasa ba na kasa hanashi saima wani irin dad'in k'amshin jikinsa da na keji abin sha'awa don tunda na ke ban tab'a jin dad'in turare haka ba.
Muna cikin wannan halin ne naji muryar shi dai dai kunne na ya ce.
"I love u"
Har cikin b'argon jiki na naji wannan dad'in Amman da nayi wani tunani da sauri na wuce parking space,da sauri ya wuce ta gaba na ya janyo hannuna ya ajjeni a kusa dashi ya figi motar sai gida.
Kallona kawai ya ke yi yana tuk'i ya kasa cemin komai saboda miskilanci don na lura Muta'z miskili ne,nima ban ce mai komai ba na juya ina kallon window sai naji yana cewa.
"Mumtaz na Sani ni me babban lefe ne awajenki to ina Neman alfarma a wajenki ki bani dama in gyara lefina don Allah", ya fad'i hakan cikin rarrashi.
Ko kallon shi banyi ba har muka iso wani tafkeken gida me rantsattsan kyau,mamaki ne ya kamani na juya zanyi magana kawai sai naga ya bud'e min murfin k'ofar motar alamar in fito.
Ko kallon sa banyi ba na fito na tsaye a waje,kawai sai naga ya tsugunna a gabana yana cewa" don Allah Mumtaz ki yi hak'uri ki yafe min nayi alk'awarin insha Allah zan gyara lefina please ya had'a hannayensa alamun ban hak'uri.
Ban sanda na had'a hannaye na da nasa ba inq cewa na hak'ura ka tashi mu tafi gida Allah ya yafe mana baki 1.
To tun daga wannan ranar ne Muta'z ya k'ara shigemin kuma ko agaban waye sai ya nuna min soyayyarsa a fili,Amal ta kan CE min na yi dacen miji me sona,kawai kallon ta na ke yi don ni kad'ai nasan me Ya yi min Amman Allah da kansa muna yi mishi lefi ya yafe mana don haka na yafewa Muta'z lefinsa Amman dole sai na gumq masa idan mukayi Aure wannan sirri na barwa zuciyata.
Ummu Maher ce
*_AKAN AIKI NA_*
Rubuta wa✍🏻
_(Ummu Maher)Miss Green_
Pg 74&75
.....ko da naje barkan Meemi ko kallona ba ta yi ba k'arshe ma ta tashi ta barmin wajen,Allah yasa Fulani tana Gidan ta amshi kayan barkan da na kawo sannan ta ringa yiwa Meemi fad'a akan wulak'an ta d'an Adam ko don ina a matsayin y'ar uwarta mafi kusanci.
Ni kuwa daman nasan hakan zai faru don ba kowacce mace ba ce ta ke da b'oye Kishin ta don haka kuwa dole ne ta yi,Amman ni dai har zuciyata bana jin haushin ta ko kad'an don ni shi kanshi mijin ba sonshi na ke yi ba ballan tana inyi kishinsa don haka tuni daga shi har ita na tattarasu na watsar.
Umma ce kad'ai ta je ranar suna Amman babu yadda ba ta yi dani inje ba Amman na k'i k'arshe ma na lafe a gado na ce ba ni da lfy.
Ina kwance a kan gadona daga ni sai wata rigar bacci Red color gashin kaina duk ya barbazu akan gadon kamar wata ba India,k'arar shigowar mota naji Amman sai ban tashi ba don nasan Mlm ne ya dawo kuma watak'il wani abin zai d'auka don haka naci gaba da bacci na.
A cikin bacci na naji wani irin k'amshin turare Wanda k'amshinsa ba ya gushewa a cikin hancina da gangar jiki na baki 1,saurin ta shi na yi don tsabar tsoro gabana ne ya yi wani irin mugun tashi ganin Muta'z a kaina yana yimin wani irin mayen kallo kamar zai cinye ni.
Da Sauri na fara Neman blanket d'ina Amman baya kan gadon,kunya ta bi ta isheni kawai sai naga ya k'araso har inda nake ya lullub'amin a jiki na sannan ya yi min wata signal ya bi hanyar fita,tsayawa naga ya yi a bakin k'ofar sannan ya ce min"ki fito Hanan ta zo ganin ki don jiya ta dawo daga mkrnt......
Ai ban Bari ya k'ara sa ba na d'auko hijab d'ina na saka na wuce ta gabansa da Sauri don zumud'in ganin Hanan,shi kuwa tsayawa yayi a bakin k'ofar yana shak'ar daddad'an k'amshin da Mumtaz ta barmai,har zuciyarsa ya ke jin wani irin tsagwaran son Mumtaz har cikin zuciyar sa so na tsakani da Allah.
A farlo ya samesu sun rungume juna suna ta zuba surutu,ya watsowa Hanan wani kallo sannan ya ce"ke Hanan ki iya bakin ki don Da amarya ta ki ke magana ehee".
Dariya Hanan ta yi sannan ta ce"Kai gaskiya Yaya ka iya zab'e fa gata k'anwarka ga ta matarka kaga shikkenan ka had'a k'annenka a matsayin Matanka".
Nan dai Hanan ta ringa bani labari,shi kuwa Muta'z sai kallo na ya ke yi kamar zai cinye ni da naga ya matsamin sai na rik'e hannun Hanan na ce muje kitchen mu d'ora girki,sannan na juyo Amman na kasa kallon kwayar idonsa na ce"ka koma gida kaga yau suna zamuyi girki."
Zama naga ya k'ara yi sannan ya CE"Wow shikkenan kinga sai inci girkin amaryata".ya fad'i hakan ya na mannemin ido alamar yaji dad'in hakan.
Hanan sai dariya ta ke tana cewa Romio da Juliet kawai,ni kuwa naja hannunta muka shiga kitchen muka fara aikin mu gadan gadan,tunda suka fara girkin Muta'z yake kallon farlon kamar ya bisu ga wani k'amshi da ya faraji Wanda ya gama cika farlon.
Naman kai muka dafa Wanda ya gaji da k'amshi ,sai jallop d'in taliya Wanda Tasha green beans, da hanta,da kayan k'amshi sai coconut&pine apple jus.
Hanan ce ta fara jerawa a dining ni kuma ina gyara wajen da muka b'ata sai da na gama gyarawa tsab sannan nafito,na d'auka gaba d'aya ya tafi baya farlon Ashe yana nan ya hard'e k'afa 1 kan 1,kallo na ya ringa yi har na fara hawa kan step a hankali kamar me tausayin tsep d'in, Muta'z kuwa kamar wani soko sai kallo na ya ke yi Hanan ta kula da hakan sai dariya ta ke yi shi kuwa gogan besan ma meke faruwa.
Yana ganin Mumtaz ta hau sama ya fara cika cikinsa da d'a amun yana santi kamar wani yaro sai da yaci ya more sannan ya tashi yana masha Allah kace na more da amarya me iya girki.
A hankali na fara sakkowa akan step d'in ina sanye da wata doguwar Riga Arabian gown blue black kasan cewa ta fara sai ta haska ni sosai na nad'a belt d'in a kaina na saka plat show me kyau, ina danna wayata har na k'ara so Amman Muta'z besan na k'ara so ba don wani mugun kallo da ya ke bina dashi kamar zai cinye ni,ni kuwa na basar dashi na zauna ina cewa Hanan idan ta gama cin abincin zamuje gidansu Amal don su gaisa.
Saurin tashi Muta'z ya yi wai zai kaimu,Amman na ce mishi ya barshi ga gidansu nan kusa da namu Amman fafur ya CE wallahi sai ya rakani.
Haka kuwa akayi har gidansu Amal ya rakamu sai da yaga mun shiga sannan ya tsaya acikin motar ya ce mu shiga zai jiramu,ina matuk'ar mamakin kishin Muta'z kamar Wanda za'a saceni.
Amal ta yi matuk'ar jin dad'in zuwanmu,Mamansu ma sai nannan ta ke damu don yanzu sona ta ke kamar za ta goyani,ni kuwa a zuciyata oh Ashe dubiyarnan sai kana dashi a ke damawa da kai.
.....Fulani da kanta ta d'auko me yimin dilka da gyaran jiki ciki da waje,ai kuwa matar tasan abinda ta ke yi don irin matan sudawan nanne don haka ta zage awajen gyarani ciki da waje,gabana kuwa ko d'an yatsa bazai shiga ba tsabar gyara kuma an hana Muta'z zuwa gidanmu don har sai an kaini Gidan shi sannan zai ganni don haka Bak'aramun kwaruwa Muta'z ya yi ba don har ciwo sai da yayi,don Ni da kaina na tsara wannan don yadda na ke ada ma Muta'z yana k'ok'arin tab'a jikina ballan tana yanzu da komai nawa ya canza Wanda ya sanni ada yanzu ba zai gane ni ba.
Please kuyi hak'uri abubuwa ne suke yimin yawa shiyyasa bana tyiping da wuri✍🏻.
Ummu Maher CE
Vote
Share
And
Comments.
*_AKAN AIKI NA_*
Rubuta wa✍🏻
_(Ummu Maher)Miss green🍀_
_*Please don Allah kuyi hak'uri fans bana samun kawo muku labarin Jamila abubuwa ne suka yi yawa*_
_(The Wedding)_
💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼
To fa ranar muke jira yau gata tazooo,ranar bikin Muta'z da Mumtaz.
Page 76&77
Wani irin kyau me had'e da sirrika kala² Mumtaz ta yi kamar ka d'auke ta gaba d'aya,tun jiya na ke kuka don idan na tuna ayanzu haka na zama Matar Mumtaz ba k'ara min tashi hankali na ya ke yi ba,don gaba d'aya yanzu tsoron Mumtaz na ke yi don na dad'e da sanin ba k'ara min mugu bane.
Tun k'arfe 4 y'an d'aukar amarya suka zo muna ta kuka nida Amal,don tun safe muke kukan rabuwa ni da aminiyata Hajjo kuwa sai masifa ta ke Wai min isheta da kuka kamar wad'anda za'a yanka kukan ya yi yawa.
Hajjo CE ta shiryani da kanta da wata had'addiyar tamfa super me Golding ta yi kyau sosai sannan aka d'oramin wata lafiyayyiyar Lifaya fara Sol sai ratsin gold ajikinta aka fesheni da turare exsense ne k'amshin gaske.
Har aka gama shirin kuka na ke yi aka shigar dani babban farlon Mlm ya yi min nasiha sosai me ratsa jiki nan fa kuka na ya k'ara k'aruwa da k'er Mlm ya rarrasheni don shima kukan zuci ya ke yi.
Wata sabuwar mota muka shiga wadda Muta'z ya yimin kyautarta yau bayan d'aurin Aure motar sai k'elli ta ke yi.
Muna shiga Gidan Sarauta ya d'auka a ko ina bakajin komai sai tashin kid'a da tambura ta ko ina,Muta'z kuwa yana d'akinshi shida abokansa suna ta yimai tsiya Mijin Meemi da Mumtaz abin shi kanshi burgesa ya ke yi sosai.
Meemi kuwa tana sashenta lokacin da aka shigo da Mumtaz ji ta ke kamar ta kashe kanta tsabar kishi,Baby kuwa sai kuka ta ke yi baiwar Allah Amman tak'i kulata da ta dame ta ma har dungure mata kai ta yi ai kuwa ta ringa tsala kuka.
"Don ubanki ba ubanki bane ya janyomin wannan fitanar ba ina zaman zamana yarinya ta lik'ewa mijina ai kuwa duk sai sun gane kurensu don wallahi bazan yarda wacce mace ta had'a shimfid'a da mijina ba.
B'angaren Fulani aka fara kaini ta karb'eni hannu bibbiyu sannan ta kaimu b'angaren mai martaba shima ya yimin nasiha sosai ta zaman hak'uri agidan miji,sannan ya mik'omin wasu mukulli na kyautar wani Gidan shak'atawarsa Har kuka saida Hajjo ta yi na ganin irin kyautar da Mai Martaba ya yiwa jikarta ta dinga saka mai albarka.
Sashen Meemi aka nufa dani Amman muna zuwa Masu yi mata hidama wato bayinta suka CE mana ta fita,Hajjo kuwa cewa ta yi "Uban ta fita ba bata fita ba🥴wallahi sai tadawo munanan muna jiranta ko in shigo d'akin tafito ja'ira,da k'er aka bata hak'uri ta hak'ura ammanfa tana ta sababi.
Sashena aka kaini aka ce in shiga da bismillah,ai kuwa na shiga da addu'oi a bakina gwanin sha'awa,sai da na CE alhmdh don wani dad'i da nishad'i na dinga ji sosai.
Akan faffad'an gadona aka ajjeni Amal ta rungumeni tana ta kuka y'an kai Amarya suka fara watsewa daga ni sai Amal sai Hanan ita kuwa sai murna ta ke yi ta samu k'awa ni kuwa kaina yana cikin had'addiyar lifaya sai k'amshi na ke zubawa ana cikin haka mukaji ana bud'e k'ofa.
Da sauri Amal ta tashi tana share hawayenta,Muta'z ne shi kad'ai yasha wata d'anyar shadda fara Sol abin sha'awa kyaunsa da nutsuwarsa da haibarsa duka sun fito gwanin ban sha'awa.
Gyaran murya ya yi Amal da Hanan suka gaishesa sukayi mana sai da safe,anan naji hanjin ciki na sun kad'a K'uuuu tsabar tsoron Muta'z, shima ya fuskanci haka don haka ya zauna abakin gadon yana me godewa Allah akan kyautar mata da yayi masa.
Matsowa ya farayi ni kuma ina ja da baya don kunyarsa na ke ji ba kad'anba kawai sai naji ya kamo hannuna cikin nasa,yana shafawa ahankali da sauri na janye hannuna ina Jan zuciya.
Dariya ya yi sannan yace ina yiwa Allah godiya da ya kawo mu wannan rana Dana mallakeki a matsayin matata,sosai na juyo numfashinsa gab dani ya yaye min mayafina a hankali sannan ya CE"Masha Allah ina yiwa Allah godiya da ya bani wannan babbar kyau ta,Mumtaz da ban Aureki ban San yadda rayuwata zata zama ba sonki Allah ne ya d'arsa min shi a cikin zuciyata,ki bani dama in koya miki sona kuma in shayar dake dad'in da baki tab'a ji ba arayuwarki.
Ummu Maher CE
Vote
Share
And
Comments
*_AKAN AIKI NA_*
Rubutawa✍🏻₹₹₹₹₹
*_(Ûmmu Mâhér)Míss gréén☘️_*
Wannan shafin naku ne masoyana Allah yabarmu tare.
*Mmn Teddy*
*Y'ar Kaka*
*Nabila Dikko*
*Nabiha Aminu*
*Ruky Gawata(My suruka)*
*Hadiza Barau Gidan Iko*
*Amina M Baso*
*Ummu najma*
*Dr Amira*
*Khaltum Khanna*
*Zahra'uu Naseer Aliyu*
*Nersmer*
*Momin Shukura*
Page 78&79
Shiru na yi ina tunanin wannan wani irin farin ciki ya ke so ya saka ni,ni dai nasan babu wani farin cikin da zai iya saka ni saboda shi azzalumi ne mutumin da ya yi min fyed'e ta k'arfi Da yaji shine yanzu zai CE zai saka ni cikin farin ciki,ina cikin wannan tunanin na ji ya rik'e hannu na kamar zaiyi kuka ya Ce"Mumtaz ki yadda zan shayar da ke farin ciki Mara misaltuwa don haka yanzu ki tashi muyi sallah mu godewa Allah bisa wannan ni'ima da ya yi mana.
Addu'ah Yarima Muta'z ya dinga kwararuwa har mamaki ya bani daman ya iya addu'ah irin haka ban Sani ba,Ya kama goshina ya yi min addu'a.
Da kanshi yadinga shayar dani fresh milk tare da d'awisu wadda ta gasu da kyau k'amshi ya bad'e ko ina,ban San ina jin yunwa ba sai da naga abinda naci da yawa sosai.
"To ni baza a shayar dani ba a samu lada"?.
Maganar sa naji kamar a dodon kunnena don haka naji tsigar jiki na ta tashi sai na tsinci kaina a mai yimai murmushi na cuko hannuna da lomar D'awisu na saka mishi a baki,a kunya CE na fara ciyar dashi yana lumshe ido.
Zan saka mishi lumar k'arshe ya rik'e hannuna naga idanunsa gaba ki d'aya sun juye,ya rungumo ni kamar y'ar k'aramar yarinya sai bathroom,kunya da nadamar saurin saukowata daga dokin fushi ya dame ni,don kafin in farga ya rabani da komai nawa ya saka ni a komar wanka shima ya shugo.
Tunda nake ban tab'a jin Abu me dad'i irin Wanda Yarima Muta'z ya ke min ba,Lallai Allah ya yi gaskiya da ya CE muddin mace da namiji suka had'u to namijin su shaid'anne,kuma koma menene Aure dai ni'ima ne,don da zina CE ba zata yi armashi haka ba.
Gaba d'aya ya sake rungunoni zuwa kan faffad'an gadonmu Wanda ya gaji da had'uwa ya fara kawomin wasu zafafan kiss a cibiyata ban San sanda na manta da hanyar garinmu ba na saki jiki kamar y'ar hannu ina kawo wuta.
Ni kuwa Ummu Maher na rufo musu k'ofa na CE Yarima asha angonci lfy.
Sai da komai ya lafa sannan ya rungomin yana saka min albarka tare da fad'amin maganganun da sai da naji kunyarsu don tuni na manta da wani Abu da Muta'z ya yimin a baya kuma daga wannan Daren na gane Muta'z so ya ke yimin domin Allah ba don wani Abu ba.
Ranar kuwa Uwargida Meemi ko runtsawa ba tayi ba,don yadda ta kejin zuciyarta bata tunanin ayanzu Muta'z zai ko kalleta don yadda ya ke nan²da Mumtaz ga ta mai kyau, da koma ta CE ta fita komai don ta tsorata ita kanta da yadda Mumtaz ta yi kyau kamar ka d'auketa duk namijin da yasa ido akanta ba zai iya d'aukewa ba saboda ta tafi da ko wani irin sirrin kyau.
Kuka babu irin Wanda Meemi ba ta yi ba,Baby ma ta tashi jin uwarta na kuka ita ma ta fara ta ya ta,Amman da Ta ishe uwar da kuka Zane ta tayi don dole Baby ta yi kuka tana Jan zuciya,ta kalli yarinyar komai nata irin na mahaifinta sai taji gaba ki d'aya yarinyar tana bata mugun haushi.
Da kanshi ya gasa Mumtaz tana ta rufe ido saboda kunya,shi kuwa jinshi ya ke kamar wani sabo don yadda ya kejinshi cikin nishad'i da annushuwa.
"My Baby in k'ara round2 wallahi ban k'oshi ba?".
Da Sauri Mumtaz ta shammaceshi ta d'auki tawul d'inta ta fito da gudu suka fara y'ar tsere daga k'arshe dai suka fad'a kan gado suna mayarda numfashi a tsakaninsu,Muta'z ya kalli Mumtaz ya CE" My baby ina matuk'ar sonki da k'aunarki don Allah kada ki gujeni duk rintsi duk wuya",Mumtaz nasan kina sona duk da abinda na aikata miki Amman baki tona min asiri ba,kika rufamin asiri kinga kuwa ya zama dole in soki don ke matar rufin asiri CE.
Daga nan Muta'z ya k'ara yiwa Mumtaz,wayo suka fad'a duniyar maji dad'i.
Tare suka tashi daga bacci sukayi wanka suka shirya cikin shadda dark blue me kyau,yadda sukayi kyau kamar ka sacesu suka fito farlo a tare,angama jera musu komai akan dining,har Muta'z ya zauna sai kuma ya tashi ya CE"My love bari in dubo Uwar gida ina zuwa",da kallo na bishi ya yinda naji zuciya ta babu dad'i amman babu yadda za ta yi tunda matar sa CE.
Yana shiga sashen Meemi ya hango Baby a k'asa kan tile tana bacci ga shi idonta ya kumbura da alamu ma tashi kuka abinta.
Mamaki ne ya cika Muta'z yazo da Sauri ya rungumeta a k'irjinsa da alama d'umin ta keso ta kuma lafewa a jikinsa tare da sheshshak'ar kuka alamun ta dad'e tana kuka daga baya bacci ya d'auketa.
Ko kallonshi Meemi ba ta yi ba ta cigaba da Ku kanta kamar k'aramar yarinya ta kaici ne ya cika Muta'z, y CE"Ashe baki da hankali Meemi yanzu Y'ar tawa kika ajje a k'asan tiles,kin fi kowa sanin cewa ko magen gidanmu bata kwana akan tiles ballan tana y'ata ta cikina,How comes ki CE wai kishi kike,ko hauka?saboda yafi kama da hauka Amman ba laifinki bane ki yi komai a sannu".
yana kaiwa nan ya d'auki Baby ya fita da ita yana Jan tsaki kamar zai tashi sama,abinda yasa Meemi ta yiwa Muta'z haka saboda yana da masifar son y'ay'ansa shiyyasa ta yi masa haka,I ta kuwa yana fita ta saka mayafinta ta fita.
*Ummu Maher CE*
*_AKAN AIKI NA_*
Rubutawa✍🏻ঁঁঁঁঁঁঁঁঁঁঁঁঁঁ
_*(Ummu Mâhér)Miss gréén*☘️_
🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚
Pg 80
Tun daga wannan ranar ruk'on Baby ya dawo hannuna yarinyar ta saba dani sosai don ko bacci tare muke da Baby Uban ya yi ta fad'a mussaman idan yana Son harka in yi ta mai dariya da kansa zai d'auketa ya kaita d'akin ta.
Sannan an kawo min Barori har guda uku masu taya ni aiki,harma da Jakadiya aka kawo min, don babu yadda zanyi ne Amman kwata² masu AIKI basa cikin tsari na.
Tunda Meemi ta bar Gidan nan bata dawo ba,Ashe wajen Me Martaba takai k'ararshi Wai baya kwatanta mata adalci a tsakaninmu,lokacin da Me Martaba yaji ya kirawo Muta'z ya shaida masa duk abubuwan da Meemi ta fad'a mishi.
Sosai Muta'z ya ji haushin Meemi don ya tsani kai k'ara Amman babu yadda zaiyi Dole ya bawa Me Martaba hak'uri don a zauna lfy.
Ko da ta dawo Ma tashin hankali na yau daban na jib'i daban Amman duk da haka Muta'z baya shiga harkarta don ko yana b'angaren ta sai taga damar yimai magana,shi kuwa ya shigewarsa d'aki ya barta cikin zullumi,kuma har yau bata tambayi Baby ba don daman madara ake bata watanta uku ta daina bawa yarinyar nono Wai kada Nonon ta ya lalace shiyyasa ta daina ba ta,shima Muta'z ko zancen Baby baiyi mata ba ya saka mata ido kurum don shi zaman Baby awajan Mumtaz ya fiye mishi akan zama a wajen Meemi.
**** *** ****
"Wallahi tallahi Murat baka isa ka ce sai da ka aureni yanzu kuma zaka sakeni ba matuk'ar ka sakeni to tabbas asirinka zai tonu don bazan yarda ka cuceni ka CE kuma kai zaka zauna lfy ba ehe".
Meema bata San tun tuni Murat ya kwashe wannan CD d'in ba lokacin da ta saki jikinta dashi shi kuma a lokacin ya kwashesu duka ya k'una.
Shiru Murat ya yi yana kallon Meema sannan ya CE Meema ba zaki k'ara kwana a Gidan nan ba Meema kin cuceni kinci amanata duk kud'in Dana mallaka kin kwashesu saboda son zuciyarki Amman yanzu kina fad'a min kada in rabu dake saboda tonuwar asiri na,don haka na sakeki Saki 3.
Wani wawan ihu Meema ta yi ta zabura zata shak'e Murat ya yi kukan kura ya hankad'ata sannan ya nuna ta da yatsar sa ya CE" ki fitarmin agida tun kafin in saka ayi waje dake".
Ko da ta nemi ta yi mai gaddama don haka da kansa ya dinga janta har sai da fidda ta tak'arfi da yaji tana kuka tana ihu, don a rayuwarta tana matuk'ar son Murat.
Yana shigowa ya rufe get d'in ya zauna a farfajiyar Gidan yana jin zuciyarta tana yi masa zafi tabbas alhakin Muta'z ke bibiyarsa kuma tabbas bazai samu sukuni ba har sai ya nemi yafiyarsa,hak'ik'a hassada ga mai rabo taki CE,be yarda da wannan Karin maganar ba sai akanshi don Muta'z bai tab'a yimai Hassada ba Amman gashi kullum yana cigaba shi kuma yana dakushewa ya zamanto duk abinda yasa hannu to sai ya lalace.
Yana cikin wannan tunanin yaji horn d'in mota da sauri ya kallo bakin get d'in don yasan wannan tabbas horn d'in Muta'z ne.
Da sauri ya tashi ya bud'e mai yana me Matuk'ar jin kunyar kallon Muta'z don gani ya ke yi kamar Muta'z ya gane duk wani Abu da ya yi mai.
"Haba Murat yanzu ko ban nemaka ba kai ba zaka neme ni ba?".
Da sauri Murat ya rungume Muta'z yana kuka yana cewa" Muta'z ka yafemin don Allah idan baka yafemin ba bazan samu sa'ida ba har awajen Allah.
"Murat na yafe maka duniya da lahira,kuma bana son inji lefin da ka yi min na yafe maka Allah ya yafe mana baki d'aya.
Sosai Murat ya dad'a ganin girman Muta'z saboda lallai Muta'z ya cika mutum na gaskiya me yafewa magautansa.
Hira sosai suka shiga yi har Murat yana bashi labarin sakin da ya yi wa Meema da duk abinda ta yi mai babu Wanda ya b'oyewa Muta'z.
Daman Muta'z yasan za'a yi haka saboda yadda aka shirya Auren,dole Allah ya d'ebewa abin albarka.
*After 5 years*
..,....
Mumtaz na hango tana zaune da k'aton cikin ta haihuwa ko yau ko gobe,ta k'ara cika da kyau kana ganinta kasan Hutu ya zaunu ajikinta.
Wasu yara ne Twins wad'anda ba zasu wuce shekara uku ba mace da na miji sai kuma yayarsu Baby ta ruk'osu gwanin sha'awa.
Suka fad'o kanta suna mata sannu da gida. *After 5 years*
..,....
Mumtaz na hango tana zaune da k'aton cikin ta haihuwa ko yau ko gobe,ta k'ara cika da kyau kana ganinta kasan Hutu ya zaunu ajikinta.
Wasu yara ne Twins wad'anda ba zasu wuce shekara uku ba mace da na miji sai kuma yayarsu Baby ta ruk'osu gwanin sha'awa.
Suka fad'o kanta suna mata sannu da gida."Wash haba Murat kai kafi kowa rashin hankali so kake ka illata ni?".
" Haba Mmn Murat ayi hak'uri mun tuba".
Muta'z ne ya fad'i hakan lokacin da ya ke shigowa cikin farlon yasha kayan sarauta irin Wanda Y'ay'an Sarauta suke sakawa musamman y'ay'an gata.
"Har kun dawo daga hawan ne"?
" Eh madam mun dawo ya gida"?.
Nan muka cigaba da a tsakaninmu akwai shak'uwa sosai kuma bazaka tab'a cewa ba ni CE na haifi Baby ba,na d'auketa kamar Twins Murat da Meema asalin sunanta Khadija, sunan Meema wadda Allah ya yiwa rasuwa shekara 1,A sanadiyyar Haihuwa Allah ya yi mata rasuwa da d'an cikinta.
Kafin Meemi ta rasu mun zama 1 ni da ita domin duk wata k'iyayya ta daina da taga bana kula ta,shiyyasa muka zauna lfy.
Umma da Mlm sun dawo Gidan Sarauta,Hanan ta Auri Murat biyo bayan ruguntsumin da akayi don Da k'er Hanan ta Auri Murat,Amman a yanzu komai ya zama tarihi y'ar su 1 me Suna Mumtaz, takwara ta Hajjo ma tana nan tare damu Alhmdh ayanzu babu abinda zance da Allah sai godiya don ayanzu bani da wata matsala sai wadda ba arasa ba ita ma kuma ta zama dole kodon Allah ya jarraba ka.
Amal ta Auri wani abokin Muta'z shima likita ne kwararre Wanda a yanzu suna K'asar England ita da mijinta me suna Ahmad.
Meema ma ta yi Aure ta Auri wani me suna Alhaji K'asim matansa 4,Wanda a farko taji dad'in Aurensa Amman daga baya ya zamar da ita kamar jaka,zagi da wulak'anci yanzu ansallami ko wani me aiki agidan ita ta ke yi,Wanda tuni ta nemi yafiyar Muta'z duk da bata fad'a mai lefinta ba Amman ya yafe mata,ta nemi yafiyar Murat ma shima ya yafe mata.
Mumtaz ta sauka lfy ya yinda ta haifi d'a namiji me kamada Mutaz.
Hajiyan Mukhtar har gida tazo ta bawa Mumtaz hak'uri akan duk abubuwan da ta yi mata,don tun yanzu ta gane Illar Auren had'in da ta yiwa d'anta Mukhtar don yanzu Sakina da Uwarta ba k'aramin wahalar da Hajiya suke ba.
Duniya kenan shiyyasa aka ce makashinka yana tare da kai.
*TAMMAT BI HAMDULLAH/....*
*SUBHANAKHALLAHUMMA WABI HAMDI ASH'HADU ALLA ILAHA ILLA ANTA ASTAGHFIRUKA WA'ATUBU ILAIKA*
Anan na kawo k'arshen wannan littafi nawa me Suna AKAN AIKI NA,ina fatan y'an uwana zakuyi amfani da abinda muka karanta,saboda yana da kyau muringa karanta littafi badon soyayya ko wani Abu ba,a'ah mu ringa katantashi saboda d'auka darasi na rayuwa.
Wanda idan kun lura wannan labarin yana fad'akar damu akan illar Hassada da kuma cin amana.Sannan kuma yana nuna mana cewa yadda da k'addara Imani ne,kamar yadda mahaifin Mumtaz ya yarda dashi gashi daga baya ya yi arzik'i.
Masha Allah ina gaida masoyan wannan littafin baki d'aya musamman.
*KHALTUM KHANNA*
*DR AMIRA*
*MAMAN HUMAIRA*
*LUBABATU SULAIMAN*
Da dukkanin masoyanana Allah yabar zmnci Amin.
Taku har kullum Ummu Maher Miss green👌🏻££££չչչঊঊঊঊঈঈঈঐঔঔ
Masu jin yaran india su fassara🤣🤣🥴🥴✍🏻.
Sai kun jini a sabonLittafina me Suna
RAYUWARMU AYAU
&
0 Comments