IMTINAN Complet By Kulsoom Ismail Idris Mrs Baba Bello Abubakar
Bismillair Rahamanir Rahim
Da sunan Allah me Rahama mejin kai.
Yauma gani dauke da Littafi wanda na tabbatar zai nishadantar daku ya ilimantar daku ya fadakar daku. Ina fatan zaku dauki darussa da dama acikin sa Littafin ya kunshi abubuwa kamar haka.
Soyayya,tausayi,makirci,karka wulakanta dan adam duk yadda kake tunanin kafishi. Tare da wasu abubuwa da dama daban fade suba zaku jisu awannan Littafi.
Da wannan nake yiwa daukacin makaranta hausa Norvel ta'aziyyar babbar marubuciya Hadiza Salisu Sharif duniyar marubuta tayi rashi babba Allah yaji kanta ya jaddada Rahama agareta yabawa yayanta da iyayanta danganar rashinta.Allah ka haskaka makwancinta aikin Alkhairinta ya bita intamu tazo Allah yasa mucika da kalamr shahada.Ameen
💕💕IMTINAN💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Marubuciyar.
💕💕WA'AT Free book💕💕
💕💕 UNCLE J Free book💕💕
💕💕MA'ADANAR SIRRI paid book💕💕
💕💕And New book IMTINAN paid book.💕💕
Page 1&2
Cikin takun kasaita hade da izzah take taking steps wasu riga da wando ne ajikin ta sunyi masifar matseta cimgom ne abakinta sai tauna take kamar karya ta fenti fuskarta kamar yar tsana haka takoma,tunda ta fara sakkowa Ummee ta zuba mata ido cike da bacin rai Zuciyarta harwani tafarfasa takeyi idanunta cikowa yayi da kwallar takaici da bakin ciki sam IMTINAN kin kallon Ummee tai tasan kalar kallon da zata fuskanta daga gareta kai tsaye gefen Dad ta nufa ta zauna wanda tunda tafara sakkowa yake sakar mata murmushi.
Babu wata damuwa a tattare dashi na shigar datai kanta ko dan kwali babu sai dogon gashinta daya sakko har gadon baya.
Good morning My Momma na dan kallon sa tai kamar bazata tanka ba morning abunda tace kenan ta tsuke dan karamun bakinta Ummee jitake kamar tatashi ta rufesu da duka dagashi har ita morning Ummee tafada cikin sanyin muryarta ko kallontà Ummee bataiba ta mike daga dining din cikin fushi batason tayiwa IMTINAN baki tasani sarai matukar ta bude bakinta to ba magana medadi ce zata fito ba shiyasa tazabi datai shiru.
Bakin cikin da IMTINAN ita da mahaifinta ke cusa mata ya isheta kodai ba ita ce ta tsugunna ta haifeta ba sai haka akullum Dad gayawa Imtinan yake Ummee bata kaunarta tunda har take mata fada da hanata dukkan wani abu da take so,akan haka Imtinan tataso dajin cewa Ummee ba kaunarta take ba.
Tayi dana sanin Auran Dad yafi sau million da tasan haka jahilci yayi masa katutu da bata Aureshi ba babu abunda yasani a bangaren Addini sedai ina zaka office daga ina kake office bashi da magana seta office abunnan yana matukar damunta gashi ya sangarta mata yarinya bata ganin kan kowa dagashi har ita data tsugunna ta haifeta balle kuma yan waje da duk inda ta gifta zaginta akeyi.
Mikewatai ta saba jakarta byeee Dady kiss ta manna masa agoshi tana daga masa hannu.
Fita tai tana karkada mukullin mota kai kace bazata taka kasaba kamar wahainiya haka take takawa face dinnan ahade yana zaune akan bencin da get man ke zama sai sauran ma',aikata maza da suke dan shawagin su.
Tunda suka hangota kowannen su yayi shiru da bakinsa sun sani sarai bata da mutunci bata da kunya bataki ta zazzage su aciki harda wadanda suka haife ta amma hakan bazai hana tai musu dibar albarka ba.
Cikin rashin tsammani yaji key din mota a daidai hancin sa wani radadi ne ya ziyarci kwakwalwarsa kafin kace me hancin ya fashe jinine yafara diga da sauri get man ya mike subahanallahi hancinka jini yake Ziyad lumsassun idanun sa ya bude wadanda suka rine da zallar bacin rai danne fushinsa yake yi baya son ya nunawa yarinyar nan ko kadan wanene shi ya shanyeta ya dameta a rashin mutunci.
Get man din ta dakawa tsawa kai koma ka zauna waya baka izinin tashi kai kuma daka tashi kana rawar jiki kanin babanka ne shi da zaka taso da tsohuwar kafarka duk faso kana tsamin dauda ware ni kamatsa daga kusa dani.
Tsayawa get man din yayi cike da tsanin bacin rai da takaici yarinyar da yayi jika da ita takeyi masa wannan rashin mutuncin Allah ka rabamu da talauci bayan talauci mezesa ya zauna jikarsa tana gasa masa magana son ranta.
Kallon sa tayi cikin kyama kallon raini da kaskanci take masa,kai kuma matsiyaci kana cin arziki a karkashin mahaifina shine kana kallo na fito me nagaya maka ina fitowa ka tashi kai driving dina kasan inda zanje ai tsaki tayi tsiyar talaka kenan be iya cin arziki ba tsaki taja tai gaba.
Tsana me sunan tsana ya tsani Imtinan duk wanda baisan darajar dan adam ba bashi da makiyi kamar sa gaba daya idanun sa sun rine da bacin rai bakin sa har wani daci yake yàke saboda fusata,hanky ya dakko daga aljihunsa ya goge hancin sa kafin ya mike Ahankali tana baya ta kame kaikace ubantane CBN gaba daya sai hura hanci take tana girgiza kafa.
Phone din tace tai kara I phone 13 cikin dariya tafara magana beji abunda aka fada mata ba wata dariya ta sake saki nida dan kasar waje ne shi ya dakko ni kinsan dama aikin sa kenan to mene amfaninsa inba haka ba mutum ya koma inda yafito,tsaki taja nifa banda Ummee ta dage bazan zauna wannan tsamin yana driving dina nafi karfin haka amma kinsan Ummee har yanzu bata waye ba nayadda da abunda Dad dina kefadan na bata kauna ta tun ina jaririya.
Ok badamuwa saina kara so kit ta kashe wayar ko kadan be nuna akwai wata halitta acikin motar ba karatun Alkur'ani ya kunna tazo kuwa iya wuya,cikin hargowa take fadin waikai wane irin dan kauye ne da zaka cikamin kunne da wannan karar koka kashe ko kayi abakin aikin ka inya tanka mata to motar ma zata iya tanka mata ko kallo bata isheshi ba.
Yana jin yadda take gaya masa bakake maganganu ya share ta kamar beji ba mahaukaciya ya mayar da ita,kamar zatai kuka haka take hararar sa da manyan idanunta ta tsani wannan driving din dayake mata badan Dad ya matsa baya son ta wahala ba tafi ganewa tai driving da kanta tayi gudu yadda take so amma an takurawa rayuwar ta saiya san ita yayiwa banza.
Har cikin school din ya shaiga da ita dalibaine barka tai kowa da abunda yake yi wasu sunyi group group wasu suna karatu gasu nan dai.
Tunda motar ta tsaya samarin wajan suka zubawa motar idanu jingina yayi da bayan kujerar sarai ya gane nufinta jira take yafito ya bude mata aiko sedai ta shekara aciki,menene nufinka nice zan fita na bude kome kake nufi banza yayi da ita yaci gaba da bin kira'ar sa hannu ta kawo da zummar marinsa caraf ya rike hunnun batare daya motsa daga kishingidan da yake ba.
Duk yadda taso taja hannun kasawa tai ga bacin ran kaskantacce dashi ya rike mata hannunta me daraja da tsada,sàida yayi raayi dan kansa ya cika ta kamar wanda ya shafa mata kashi haka ta dinga goge hannun ta,rai bace ta bude kofar ta fita caaa kowa yayo mata yana kallonta wasu na mamakin waime Imti ta dauki kantane tunkan ta gama daidaita tsayuwarta yaja motar ya bade ta da kura ihu wasu samari sake gefe sukasa tare da tafawa Imti yar wanka suka kara fashewa da dariya.
Mrs Baba Bello Abubakar
.......✍️✍️✍️✍️
💕💕IMTINAN💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
💕💕Marubuciyar💕💕
💕💕WA'AT Free book💕💕
💕💕UNCLE J Free book💕💕
💕💕MA'ADANAR SIRRI paid book💕💕
💕💕And New book IMTINAN💕💕
Page 3&4
Ranta ne ya sake baci ga dizgin da yayi mata agaban wadannan kolawan dan ita fa kaf Nigeria gani takeyi babu wanda ya kai mahaifinta kudi babu wanda ya kaita gata. Wani matashine ya taho yana yarfe hannu daga ganinsa shima irin tantiran school dinnan ne yayane beb ya kika bari waccan Village guy din zai bade ki da kura wannan ba girmanki bane beb wani banzan kallo ta watsa masa kai kuma awa aciki gwalagwaji awane ma'aunin kake tsaki tai tabarshi tsaye awajan cikin takaicin yarfin da tai masa dariya aka sa harda masu yi masa ALLAH ya kara.
Kamar zata kifa saboda hils din data cokala kamar gurguwa haka take tafiya kai tsaye class dinsu ta shiga kawayanta ne suka taso suka rungume ta Imti wanka sunan da aka rada mata kenan a school din babu inda zaka zagaya kaf fadin University dinnan ba asan Imti wanka ba bake ba talaka kirarin da ake yimata kenan,hakan ba karamin sake hura mata kai yake ba seta kara fankama tana bude hanci.
Wajan zama na musamman suka tsarar mata sai ya mutsa fuska takeyi kamar wanda taga kashi,ta kusa da ita ce tai tsaki nifa kinga abunda yake hadani dake kenan Imti na tsani kallon kaskanci da wulakanci ubana yana da kudi Ubanki na dashi damme zaki dinga yi mana kallon kaskanci kallon tara saura kwata kallon nafiku wllh baki fini ba aha.
Aike matsalar ki kenan Fidy wai meyasa kike takara da Imti kodai kina adawa da ita ne,kinga Lubna banason Munafurci kema in zaki fadi gaskiya na tabbatar ba kyajin dadin kallon da takeyi mana alhalin muna tare in aka ci gaba ahaka gaskiya zan fita daga tim dinku kuje can kowa yayi rayuwar sa tsaki Fidy taja tadauki jakarta ta canza wajan zama.
Ko kala Imti bata ce ba ta tabbatar Fidy zata dawo bazata taba iya rabuwa dasu ba, Imti kije ki rarrasheta mana harara ta watsawa Lubnah kar Allah ya sa ta hakura arayuwata bantaba bawa wani mahaluki hakuri ba akanta bazan fara ba,zatai magana kenan Sir Ayyuba ya shigo ransa ahade sarai yasan rainin hankalin yan class din su Imti shiyasa ko wane lokaci baya sakar musu Fuska,abunda ya kawo shi ya fara gabatar wa amma har wannan time din su Imti surutu suke babu wadda tanuna tasan da shigowar sa.
Hy ya buga deks din gaban sa ku tashi ke da ke ku fitar mun a class wani kallon raini Imti ta wurga masa sabon cimgom ta dauko ajakarta ta bare sedata fara tauna tukunna ta dauki hand bag dinta class din yayi tsit kowa yana mamakin girman kai irin natà.
Lubnah ce tai narai narai akwaita da tsoro I'm sorry sir kamar zatai kuka haka ta hade hannayan ta Imti da Fauza ficewa sukai ko ajikin su dama karatun ba wani damun su yayi ba,kowa binsu yayi da ido kallon shigarsu kadai abar ayi musu Addu'ar shirya ne balle azo kan yadda suke mu'amalar su babu kamun kai duk wata sura da suttura da ALLAH yayi musu kowane Namiji kare da doki ya gama kalleta.
Duk cikin su Lubnah ce bata irin wannan shigar ta Allah wadarai zata yafa mayafinta midium dan Mom dinta tsaye take akanta haka Abban ta bataga Fuskar da zatai wannan tantirancin ba.
Sit down cikin farin ciki ta zauna Thanks you sir cigaba yayi da karatun sa hankalin sa kwance ya manta da shara da yayin daya fitar daga class din sa sai ajin ya kara samun nutsuwa yayi tsit kowa ya maida hankali akan abunda ya kawo shi.
Kan wasu kujeru suka samu waje suka zauna Fauza ce ta kalleta ke Imti mutumin fa ance ya shigo Nigeria wata biyu da suka wuce amma duk wata hanya da zamu ganshi tato she,dan tsaki Imti ta saki wai ke Fauza me yake damun ki gaba daya baki da zance saina Darma motsi kadan Darma wai wanene Darmannan da duk inda ka zaga sunan Family din kadai ka fada sai ankalle ka.
Dariya Fauza ta saki ina metabbatar miki Imti da zakiga Darma wllh na tabbatar daga ranar bazaki sake ganin kyan wani Namiji aduniya ba sama dashi ke ance sufa Family din Darma tamkar Larabawa haka suke tsabar kyau kamar su sukayi kansu,amma shegen haryau wasan kura yake da mutane babu wanda zai ce miki yasan taka maimai yaya Fuskar Darma take kowa hasashen kyawunsa yake kinga duk kyannan da kike takamar kina dashi kishiga estate din Darma ALLAH almajira zaki dawo.
Fashewa da Dariya Fauza tai bata rai Imti tai wane irin cin fuska ne wannan yazaki cemin almajira kinsan yadda natsani almajirai kuwa karki kara na gaya miki zamu raba hanya ni da ke,ke kuwa Imti daga yi miki misali banason misalin ta fada cikin hasala wanene wani Darma shidin banza shidin wofi balle wani Family dinsa basa gabana,uhmm kawai Fauza tace amma ita da zata samu ko yayane tashiga estate dinma tafito data godewa ALLAH Imti bazata taba ganewa ba.
Basar da maganar Fauza tai suka fada wata,ankai kusan awa daya sai Lokacin sukaga sir Ayub ya fito wani kallo ya watsa musu kallon da suka rasa na menene kamar na tsana da kyama yawu ya tofar yayi gaba,idanu Imti ta ware kallon Fauza tayi da ita ma Imti take kallo.
Dagaske abunda idanuna ya ganemin hakane Fauza kwarai kuwa dai dai kika gani ga abun kyama yawu ya tofar saboda ganin mu,ai wllh bazan taba yadda ba sai Dad dina ya nuna masa shiba kowa bane har nawane albashinsa da zaimin wannan kallon na rabu dashi saiya gane kuransa.
Mikewa tai kamar zata kifa tabi bayansa da sauri saidai kash har yasha kwana yunkurin binsa take Fauza ta ruko hannun ta haba Imtinan ina zakije wannan ba girmanki bane ya zaki bari wani Village man ya bata miki rai kibarshi kawai saidai yaga sammaci kamar Imti zatai kuka haka ta koma ta zauna amma duk ranta abace taci alwashin saita wulakanta shi tayi masa rashin mutuncin da bazai kara marmarin yi mata abunda yayi ayanzun ba.
Sai girgiza kafa take kamar wadda zata tada bori Fauza na kara zugata tanai mata fanfo ita ko shashashar sai kara hawa take kamar kudin farashi.
Mrs Baba Bello Abubakar
.......✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 5&6
Fidy da Lubna tare suka fito hango su Imti sukayo wajansu ko kallon su Imti bataiba gaba daya ranta abace yake da su kamme zasu zauna a class bayan su suna waje,tsaki Fauza ta saki kedai wllh Lubna baki da zuciya guy dincan ya koreki amma kamar mayya kinace aciki kinban kunya wllh kamar na rufeki da duka dan haushi kindaka ta Fidy dama baku da zuciya keda ita.
Dan murmushi Lubnah ta saki to mene abun rashin zuciya karatu shiya kawo mu shi aka turomu miyi daga gida matukar bamu tsaya minyi ba ina tabbatar miki min zalinci iyayan mu kuma sai Allah ya tambaye mu ranar alkiyama tsakanin iyaye da yayan su akwai hisabi,kinga Lubnah da kata in wa'azi zaki ga masallaci can kishiga kije kiyi ba kisamu agaba kina mana surutu ba bashi nazo jiba ni banason gulma da munafurci yayiwa mutum yawa.
Daga ta gaya muku gaskiya kike tada jijiyar wuya wllh ki daina biyewa Fauza ina tabbatar miki zata kaiki ta baroki ba kaunarki take ba tunda bazata iya fada miki gaskiya kuma wllh matukar muna tare sai min gaya miki gskya sedai kiyi abunda zaki yar rainin wayo kawai.
Cikin jin haushi Fauza ta mike au nice ma nake zugata kartai karatu yarinyar goye ce ita da bata san abunda ya kamace taba karki sake cewa nike hanata karatu zamu bata wllh,to seme dammun bata mekike ban bayan ma ni da kike karuwa dani saiki fadamin innataba zuwa nace ki aramin ficika koki taimakamin da wani abu nake aikin banza tsaki Fidy ta saki.
Daga musu hannu Imti tai kunga ya isheku haka in cacar bakin zakui kuci gaba mikewa tai ta zari jakarta dama lokacin tashin su yayi glass dinta ta kwama no respect har wannan time din bata daina taunar cimgom ba.Fauza ce tabi bayanta dan tsaya dan Allah ku saukeni ahanya ko kala Imti bata ce ba tai gaba yakai kusan 30mnt da zuwa wajan amma tsanar wulakanci irinna Imtinan sai yanzu taga damar fitowa.
Tunda ya hangota ya hade rai ya tsani yarinyar nan matukar tsana tsaki ya danja kamar ta rasa mafadi ko yaushe yana tausayawa Ummee da jajanta mata na samun tantiyar yarinya mara jin magana jakadiyar shedan yana mamakin shedancin Imti kamar aljana ta iya Iskanci kusfafa kusfa ba club din da bata sani ba kaf garin ABUJA.
Komawa motar yayi ya sake gyara face dinsa baya son wargi kokadan,Fauza ce ta bude mata kofar ta shiga ta zauna sannan tabi bayanta sai yamutsa fuska take.Kallon Imti tai wai wanka yaushe zaadinga ganin ki da wannan tsamin gayan kalle shifa da wani gwanjon sa dan 100 ji yadda yake maiko kamar mandako wannan abun kunya ne kamar ki babbar yarinya kaf ABUJA babu wanda besan ke mezafi bace ba kalar kowane gaja bace shikenan se kibari wannan gajan yana janki tir ni wllh kin fara batan rai.
Ya mutsa face Imti tai to ya zanyi tunda Ummee ta kafe akan bazaa kore shiba amma da tuni nasa Dad yayi masa korar wulakanci duk cikin yan aikimmu nafi tsanar shi idanunsa kamar na mayu,dariya Fauza ta saki waya sanima ko mayanne can ta matse masa cewar Imti.
Kaf maganar da suke fada akan kunnan sa idanun sa har kawo kwallah sukai me zafi kalmar maita itace ke yawo akan sa shine yau wata yarinya kanwar kanwarsa ke cemai maye,fisgar motar yayi da tsanin fushi ya mutsa sitiyarin saura kadan ya daki wata babbar mota yayi saurin kaucewa. Tuni Fauza ta fara salati tana karya kashe su ya kashe banza tunda ubansa baida kudin da zai biya diyyar su ko kallo basu ishe shiba tun Imti na daurewa sedata fashe da Kuka ganin yana kokarin zazzago mata da yayan hanji.
Kuka suke shabe shabe harda majina wani shegen titi ya yanka babu kowa atitin yadda zaiji dadin wajiga rayuwar su.Motar har wani tsalle takeyi na tashin hankali akalla takai awa daya yana walagigi dasu sunko jigata fuska tai jajawur duk da shima ya jigata amma haka ya jure sàida jikinsu yayi mugun laushi tukunna ya dauki hanyar gida.
Zuwa wannan Lokaci sau biyu Imti na sakin fitsari a wando glass din ta ya kama gabansa sai haki take tana kuka da tsinemai Albarka har wannan Lokacin bakinta be mutu ba.Ko kallan Fauza beba da take cewa ya sauketa saidaya shiga harabar gidan su Imti ya tsaya asukwane suka bude motar har rige rigen fitowa suke.
Caa ma'aikatan gidan sukayo musu suna kallon su ganin yadda suka koma kamar mahaukata babu takalmi ba dankwali gaba daya gashin su ya hautsine sunga mutuwa ganin idon su.
Ga fitsarin da yake bin kafafun su wata dariya su Shehu suka saka harda shewa da yake ba Acikin hayyacin su suke ba basuma san suna yiba.
Ko Lura da yadda ake kallon su basi ba suka afka parlon da sassarfa sàida Imti ta dangana da dakinta tajita akan bed dinta tasamu relief sai kuma abinda wancan guy din yayi mata ya dawo mata so yayi ya kashe su kenan tirkashi ya daukowa kansa masifa abunda ta ayyana azuciyar ta kenan.
Mrs Baba Bello Abubakar
.........✍️✍️✍️✍️
💕💕IMTINAN💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 7&8
Tsam ta mike tafara zagaye acikin dakin ta tana naushin iska ranta amatukar bace take barbaza gashin kanta,Fauza ce taja tsaki cikin Matukar bacin rai take kallon Imti wai me kike nufi yaci bulus kenan kome to wllh nidai bazan yadda ba ban shirya mutuwa ba haka kawai wani banza can yazo yanemi kashemu amma sewani zagaye kike banga kin dauki matakin komai ba.
Kinga Fauza ki kyaleni bana son damuwa kibarni naji da wancan garan sanin kanki ne bazai taba cin bilis ba matukar Dad yasan yadda yayi wasa da rayuwa ta bazaiji ta dadi ba karshen ta karshen aikinsa ne yazo,zata sake magana aka turo kofa Ummee ce ta shigo tana kare musu kallo wani kallo ta watsowa Fauza sunkuyar da kanta tayi duk wasu kawayan Imti ta tsane su wllh duk sune suke kara ingizata take iskancin da taga dama.
Ko uffan bata cemata ba ta nuna mata hanyar kofa sum sum Fauza tadauki jakarta da wani uban sket kamar zai yage tsabar yadda ya matseta da kallo Ummee tabita tanai mata fatan shiriya azuciyarta,kallon Imti tai wadda tazo iya wuya tagaji da abunda Ummee take mata sai Jijjiga jiki take kamar wadda zata kaiwa Ummee duka.
Fitsararriya ko dukana zakiyi da kike wannan jijjigar Imtinan nasha gaya miki abunda mahaifinki ya doraki akai ba gata yayi miki ba ina tabbatar miki akwai Lokacin da zaki gane hakan lokacin bazai taba yi miki amfani ba kisa wannan aranki ko bayan raina saikinyi nadamar abubuwan da kika shuka zaki girbeshi da hannun ki.Kallon kayan jikinta tayi kalli kayan jikinki wazaice HAUSA fulani ce ke babu wanda zaiyadda da hakan.
Nayi iya yina Imti tunda ni ban isa dake ba duniya ce zata ladaftar dake,daga ke har uban naki dayake saki dik wani rashin mutunci har nawa yake dashi iya Abuja kawai inyaga wasu masu kudin saiya raina kansa Megadi ma be isa adauke shiba daga ke harshi ko ba yanzu ba zaki tuna magan ganun dana gaya miki ina daf da bar muku gidannan bazaku hadu ku kasheni da bakin ciki ba.
Tana gama fadin haka ta juya ko ganin gabanta batayi anya ba acanja mata Imti a asibiti ba wace irin kaddara ce wannan diyarta ta zama tamkar karuwa babu kamun kai babu Addini babu komai akanta sai tsantsar rashin kunya da tasa agaba bakowa ya cuceta ba face Dad yagama da rayuwarta.
Bin kofar tai da kallo babu abunda ya dameta saima wani haushi daya cika mata zuciya kowa mamansa na lelensa amma ita banda ita. Tarasa Ummee wace irin uwa ce da bata waye ba kullum kanta adaure da bakar leda itafa Bazata iya rayuwar da take tunanin yi ba har abada kuwa. Toilet ta fada takai 30mnt kafin ta fito da wani dan mitsitsin towel ko cinya be sakko mata ba gashinta da yasha gyara har wani style akai masa rabi anshafa masa wani mai brown sai kan nata ya koma kala biyu.
Sai farata zako zako dataje aka saka mata ansa mata jan farce ajikin su eye lashes ne zarara zarara a idanun ta duk yadda take da eye lashes bata godewa Allah ba seda aka samata na kanti sai tatu da yake zane radau akafadar ta.
Kyakykyawa ce ajin farko chocolate color ce tana da gashin gira baki sidik amma taje an kankare mata shi ya dawo siriri tana da dara daran idanu kwayar idanun ta brown ne lips dinta kamar ta shafa pink din jambaki siririya ce amma tana da diri shep dinta kamar coca cola tana da bobs kai duk yadda zan fasalta muku Imti ta wuce haka.
Sedai kash gaba daya kyan nata baida amfani batayi amfani dashi ta hanya me kyau ba sharholiyar ta kawai take san ranta saboda Dad dinta ya tsaya mata kome take so saiya yimata duk tsadar shi kuwa tasha kade mutane da mota sedai tai tafiyarta tunda tasan babu abunda za'ai mata Abinda taga dama shi takeyi in kanaso ka mori Dad tofa kaso Imti yanzu ne zaima duk Abinda kake so.
Shiyasa masu jin haushin ta babu wanda yake yadda ya nuna hakan kowa yabar hakan a zuciyar sa.
Aisha Alkasim me gold kenan ya daya tilo awajan Alhaji Alkasim Kamalu me gold babbar kasuwar ABUJA anan yake sàida gwala gwalai sunyi Auran soyayya da mahaifiyar Imti Aminatu gaba dayansu yan nan ABUJA ne kowannen su iyayan sa nada yan canji babu wanda zai nunawa wani arziki acikin su.
Iyayan su aminan junane shiyasa ba wani bata lokaci aka sha biki suka tare a asokoro akalla sunkai shekaru 6 kafin Allah ya bata cikin Imti Dad ba karamar murna yayi da wannan ciki ba Ummee taga gata daga danginta zuwa danginsa. Mahaifiyar sa hajiya Aisha Mutuniyar kirki haka mahaifin sa Alhaji Kamilu mutumin kirki ne yayi suna Sosai babu wanda be sanshi ba ga temako talakawa da marayu.
Wata tara Ummee ta sankato yarta kyakykyawa duk wanda ya dauketa seya tanka saboda tsananin kyawunta ansha suna ankashe nera taci sunan Hajiya Aisha wadda suke kira da Ommu shiyasa aka boye mata suna ake kiranta da Imtinan. Son duniya Alhaji Alkasim ya dorawa Imti babu dama tai lefi Ummee tai mata fada tunda ta fara rarrafe Ummee ta fara shakar bakin ciki akanta tasha yin kuka akan abunda Dad yayi mata kamar ba ita ce ta haife ta in da za'a tsaga zuciyarta tafishi son Imti.
Tunda ta fara wayo in Ummee nayi mata fada agaban Imti zai fara fadin dama bata kaunar ta shiyasa take mata fada hakan yasa Imti tatashi da wannan acikin zuciyar ta na Ummee bata kaunarta.
Ommu da Abba sunsha yi masa fadan sangarta Imti da yakeyi amma daga karshe sedai yaji haushi har yaji yakeyi in akai masa fada akan Imti seya dade beje ya gaida iyayan sa ba yan Uwansa maza da mata har suka gaji suka zuba musu idanu. Ummee tasha kai karar Dad gidan su saidai Mamanta ta bata hakuri akan taci gaba da addu'a dajan yarta ajiki in sha Allah zata canza haka zata dawo amma babu wani canji sai abunda yayi gaba.
Zuwa yanzu duk wani bacin rai Ummee babu wanda bata shanye ba duk me aikin da aka kawo wulakancin Imti ne ke korar sa sedai aga me aiki ta hada kayanta cewar zata ganin gida daganan baza'a sake ganin ta ba.
Wannnan kenan kunji wacece Imtinan.
Mrs Baba Bello ABUBAKAR
.......✍️✍️✍️
💕💕IMTINAN💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 9&10
Babu sallama haka ta fada gidan Umma dake tsugunne tana wanke garin tuwo tabi Fauza da kallo rai bace Umma ta mike tsaye tsawa ta daka mata ke!!! Fauziyya dawo dan Ubanki cak Fauza ta tsaya Sosai take tsoron Umman su kallon ta take daga sama har kasa uwar wa ya dinka miki wannan kayan bama wannan ba fita kiyo sallama kona silala miki jiki wllh kinsanni ai sarai.
Da sauri ta juya ta rangada sallama kamar ba ita ba amsawa Umma tai zonan Umma ta sake kiranta cikin sanyin jiki ta matso inda take tambayarki nakeyi wani dan iskanne ya dinka miki wannan kayan,kiyi hakuri Umma fadawa nai akwata shine na shiga gidan su Imtinan taban kayanta nasa,kafinta rufe baki Umma ta sauke mata wani shegen mari afuska ban raba ki da wannan tambadaddiyar yarinyar ba koban rabaki da ita ba.
Dafe kunci tai cikin kuka take fadin dan Allah Umma kiyi hakuri mari ta sake kawo mata waini Fauziyya yaushe zaki dena kwadayi arayuwar ki kwadayi mabudin wahala nasha gaya miki kitsaya iya matsayinki ki tsaya inda Allah ya ajiye ki banason kakkanba da shegen kwadayi da kika dowara kanki ki kiyaye ni kuma yanzu kishiga daki ki curomun wannnan kayan najikinki ina tsaye anan ina jiranki.
Dakin ta shiga yasha ledarsa sai fridge dake gefe dakin fes fes da alama dakin Umma ne uwar daka ta shige taciro kayan kamar zata hadiyi zuciya amma babu halin magana kamar Mutuniyar arziki haka ta dakko kayan harda dukawa wajan mikawa Umma wafta tai daga hannun Fauzan batai wata wata ba ta dannasu a murhu.
Kuka Fauza ta fashe dashi Umma dan Allah kibani ba nawa bane kinsan kudin kayan kuwa bansani ba dan Ubanki muciya Umma ta dauka tabi Fauza da ita aguje ta fada daki tasa sakata tasan halin Umma sarai yanzu zatai mata jina jina. Kuka take na bakin ciki ta rasa meyasa Umma take takura mata kallon dakin su tai kamar akurkin kaji tarasa wace irin kaddara ce aka haifota a gidan talauci da ana sake gida da tuni tabar wannan shegen gidan haka take ayyanawa a ranta kirjinta har wani suya yakeyi.
Inta tuna da kawayanta gaba dayansu kowa ubansa wanine amma ita kalleta dundum acikin duhu kai Allah ya tsinewa talauci wllh Umma da baba sun cuceta da suka haifota acikin talauci kowa ya sama su Auri juna oho haka take aiyanawa azuciyata da ace Umma me kudi ta Aura da yanzu itama suna da kudi babu me yi mata wualankan ci.
Makarantar da take zuwa ma Dad din Imtinan ya dauki nauyin ta tun wani zuwa da Umma ta tabayi da ita asiti dubiya asibitin na manya ne sai wane da wane asanadin makotan su ita ma Umman ta samu tashiga anan suka hadu da Imti irin wasannan na yara aidaganan Fauza ta mannewa Imti duk da suna da nisa haka take nuko gari tazo wasa wajan Imti tun masu gadi na hanata shiga har suka gaji suka kyaleta saboda tsabar naci bata gajiya saita wuni tana sintiri.
Inta koma gida Umma tadaka ta daka amma gobe saita koma tundaga primary Imti tace asa Fauza wayyo burina Fauza ya cika suka gama aka shiga secondary gashi yanzu har University basu rabuba shiyasa ko yashe Fauza ke takewa Imti baya.
Saidata gama shan kukanta tukunna ta fito har Umma ta gama tuwon masarar ta miyar tasha wake da daddawa sai kamshi takeyi amma Fauza zuciyar ta tafasa takeyi tuna sauran kawayanta suna can da naman kaji agaba da jar miya sai abunda suke so zasuci ai wllh kota halin kaka bazata Auri talaka ba sai me kudi bazata taso cikin talauci ta kare acikin saba abinda bazai taba yiwuwa ba kenan.
Tana ci tana matsar kwalla Umma na kallonta tai mata banza taci tai kat. Alhmdlh Allah ka kara mana wadatar zuci mudaina hangen abin hannun mutane sarai Fauza tasan da ita take,Ita ma Umman ta fadane dan Fauzan taji.
Karfe 6 Dad ya dawo daga kasuwa tunda ya shigo yake kwallawa Imti kira,momina momina zama yayi a parlo yana cire hularsa takai kusan 10mnt kafinta fito daga dakinta kamshinta kadai ya isar musu da sakon zuwanta washe baki Dad yayi haba shalele tun dazu nake faman kiranki,dan ya mutsa face tai kamar wadda taga kashi daga ita sai wani gajeran wando da vest tana tafe tana shan yogurt kusa dashi tazo ta lafe Ummee kamar ta rufeta da duka dan takaici.
Haba dady wai meyasa bazaka tsawatarwa da wannan Yarinyar ba agarin arna muke zata dinga yawo da wannan kayan kalli fa ai batasan wanda zai shigo ba,to Ameena kin fara ni wllh na rasa me yarinyar nan ta tsare miki kinbi kin takurawa Rayuwarta ai yarinya ce nan gaba zata daina.
Aah motsin gado ce shekarar ta nawa 17yers ka dinga cemin yarinya ce kodai bani na haifeta ba iyaka abunda zaka dinga fadamin kenan,aikinji matsalar ki ko saboda sunan uwata nasaka wai kike nuna adawa akanta,rai bace Ummee take kallon sa ni kake fadawa haka daga nayiwa yar gaban goshinka fada zan zuba muku ido amma kome yafaru akanku karku sakoni aciki kaine uwarta kaine Ubanta.
Shikenan simple da tun farko haka kikai da baki dinga batawa kanki lokaci ba ki samana idanu nida Momina akan gskiya muke rayuwar yanci ita zamiyi bazan ta kurawa yata ba inban faranta mata ba wazan farantawa,aiwannan wargaza mata rayuwa kake babu Maganar farantawa Allah ya shirye ku mikewa tai fuuu ta haura sama cikin kunar zuciya.
Mrs Baba Bello ABUBAKAR
.......✍️✍️✍️✍️✍️
💕💕IMTINAN💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 11&12
Yadai Mamana kyabe fuska tai kamar zatai kuka tuni hankalin Dad ya tashi sake gyara mata kwanciya yayi ajikin sa are you okay girgiza masa kai tayi alamun akwai magana tashi tashi kifadamin meya faru, ahankali ta tashi ta zauna yan yatsunta takeja kamar bazatace komai ba sedata gama bashi wahala ta sanar dashi abunda sir Ayub yayi mata adazu.
Dan uban wanene shi a kasar nan da har inya ganki zai tsar da yawu seyasan yayi miki haka zega sammaci seya gwammace kida da karatu,sai share hawaye take kamar wadda aka daka haka Dad ya zauna yayi ta rarrashin ta da kyar ya samu tai shiru har dakinta ya rakata kafin ya wuce nasa. Ummee tana jinsa yana mita ko kallonsa batai ba balle ta tambaye shi mitar me yake yi.
Dad gani yayi garin yaki wayewa da kyar ya bari 7:30 ta cika yar mulkin tana bed amimmike har wannan Lokacin batai sallar asuba ba sai 8 ta fara tana zabga uwar hamma mikewa tai kamar bazata taka kasa ba toilet ta fada sedata bata Lokaci tafito daure da alwala sallaya ta shinfida haka ta babbuga sallar tana idarwa tamike.
Kujera ta jawo ta zauna agaban mirror shafe shafe ta fara da fente fente sedata gama tsaf wata gawn ta dauko jikin ta robane ta wuce mata guiwa amma bata kai har kasa ba,ilahirin jikinta ya fito surar ta radau kamar anzana acikin rigar dan mitsitsin vail ta dora aka dashi gwara babu farace tas ta dauki mayafi red hand bag ma red shoe red kamar shagon sàida turare haka tai barin turare ajikin ta.
Dad yana zaune yana jiranta ya kasa ya tsare kamar baida wajan zuwa, good morning Mamina morning Dad mikewa yayi da kansa ya jamata kujera ta zauna chips ya zuba mata se tea daya hada mata me kauri bawani da yawa tasha ba ta mike Dad ya take mata baya.
Tun sanda suka fito masu aiki suka kawar da kansu suna mamakin wane irin ubane wannan da zaina dora 'yarsa akan aikata barna,da kansa ya bude mata sit din gaba ta zauna Ziyad ne ya taso da nufin amsar key din Dad daga masa hannu yayi alamar baya bukata,nida kaina zan kaita yau gyada kansa kawai yayi ya juya bencin sa daya saba zama nan ya zauna yana kallon ikon Allah.
Ya rasa wace yar wane Uban kai suna ganin abun al'ajabi tamkar ita ce ta haifeshi bashi ya haifeta ba. Wangale masa get baba yayi ya murza kan motar ya fita waje suna tafe yana kara rarrashin ta akan abunda sir Ayub yayi mata. Sanda suka isa school din motar yan Sanda ce a gefe jiniya ce kawai take tashi,kallon Dad tai da sauri murmushi ya sakar mata shafa kanta yayi shalele kina zatan akwai wanda zai tabaki duk garinnan naki daukar mataki akansa babu shi ko duk abunda na mallaka zai kare Matukar aka tabaki sena dauki mataki.
Aguje ya shiga da motar saidaya dai daita parking kafin ya fito again ya kara zagayawa ya bude mata motar akalla takai mintuna uku kafin ta zuro da kafafuwanta kamar bata taka kasa ga jiniyar motar yan sanda nanfa kallo ya koma sama kowa ya zuba idanun wa akazo kamawa akalla police sunkai 20 kamar wanda akai kiransa anyi kisan kai.
Ita ce agaba Dad na bayanta dai police mutum biyar da suka take musu baya sai muzurai sukeyi kai tsaye office din sir Ayub ta nufa dasu. Bawan Allah yana zaune yana kurbar tea be dade da shigowa ba babu noking yaga an banko masa kofa kamar za'a karyata cikin mamaki yake kallon Imti da take wata shegiyar tauna sai busa kwai takeyi da cimgom din bakinta.
Rai bace ya mike da zummar yin magana yaga police nabin layi wajan shigo mai office shiru yayi yana kallon su da Mamaki ga Dad dayake ta hura hanci yana kada makullin mota yawwa officer ga matsiyacin nan kushiga ku fito mun dashi saiya gane kuransa saiya san yata tilo da ban hadata da soyayyar kowa ba ya taba.
Babu bin ba'asi wani tsamurmuri daga cikin police din ya sakawa sir Ayub ankwa ahannu tsabar yadda abun yayi matukar girgizashi kasa magana yayi sai kallon Imti dayake yi tuni idanun sa sukayi jajawur ba'ataba wulakantashi irin yauba ba ataba yi masa tozarci irin wannan ba kamar wanda yayi kisan kai haka police suka sako shi agaba bayan an garkame masa office.
Dalibai sunyi dafifi suna kallon abunda ke faruwa a mota police din suka zurashi suka tada mota sukai gaba dashi Dad ma motar sa yahau ya bisu abaya ba kunya ko wata nadama Imti ta wuce class dinsu tana tafiyar takama da buda hanci kowa ya bita da kallo.
Tana zama Fauzi ta shigo har tuntube take saboda gulma taciji yatsa da batanan aka tafi da sir Ayub,kusa da Imti ta zauna tanai mata jinjina kin masifar burgeni wanka baki taba faramtamin rai irin wannan ba aini sonai tundaga nan sufara jibgarsa har aje station din. Fidy ce ta kalli Fauzi afusace har abun arziki tai da kike kambamata kedai jakadiyar shedan ce wllh wadda bazata kashe wuta ba sedai ta rura ta.
Kallon Imti tayi kamar ta rufeta da duka ke kuma Aisha wllh da bana kaunarki da yanzu na dade da rabuwa dake duk rashin mutuncina nasan wanda nake yiwa amma bazan iya taba malamina wanda yake koyar dani karatu ba kibi duniya asannu akan wannan yar talakawan sai kara tabarbara rayuwarki kike ina tabbatar miki akwai sanda zata juya miki baya da zarar kin shiga bala'i bazata sake nuna tasanki ba koda wasa.
Wai Fidy mena tsare miki arayuwa da bakya kaunata,tsaki Fidy tai harke wata abace da zan zauna ina bakin ciki dake me kike dashi kikalli kayan jikina ki kalli naki kinsan muna da ban banci duk wani abu da Imti takeyi bakece kike ingizata ba kike sake daurata akan hanyar bata.
Sanin bala'in Fidy yasa Fauzi yin shiru tana muzurai,Lubna ce ta muskuta ni kaina Imti banji dadin abunda kikai ba yanzu gashi kinsa kowa yazo wucewa sai kallon mu ake ana nuno mu meye wannan inba zubar mana da class ba a school duk wani rashin mutunci mu ajeshi agefe mutsaya muyi abunda ya kawo mu daga baya koma mene sai ayi.
Mtsw Imti taja tsaki aini bazan san kunji haushi ba sai kun fita kunyo belinsa shine zansan kunji haushin abunda nayi in har bakui hakan ba baku cika masu sanin ya kamata ba,babu wanda ya taba kallon na ya tsar da yau sai shi shiyasa na nuna masa shiba kowan kowa bane har nawa ake biyansa kudinda be wuce abun susar kunne naba dole ne na nuna masa tsakanin mu akwai ban banci iname tabbatar muku sai angama waji gashi zan sa Dad dina ya fito dashi.
Shiru ajin ya dauka abunda ya bawa su Fidy mamaki da hayaniya ta kaure amma time daya anyi tsit,atare suka dago kawunan su dan ganin me yake faruwa idanun sune ya hadu da wanda ya shigo class din sir Ayub ne fuskar sa shimfide da murmushi.
Nanfa kallo ya koma sama sai akalli Imti akalli sir Ayub da yake sakarwa Imti murmushi har wannan lokacin murmushin data rasa gane na menene. Cikin takun kasaita yazo ya wuce ta gabanta babu wata damuwa a face dinsa kwarjinin sa da haibarsa saiya cika ajin gaba daya matsashine meji da kansa ilimi kudi uwa Uba kyau sosai yan makarantar ke rububinsa amma babu wadda take gabansa kaf school din bega ajinsaba bega wadda tayi masa ba.
Kallon kallo ake tsakanin Fidy Imti Lubna da Fauzi wadda bakinta se motsi yakeyi alamar akwai abunda yake sukar ranta tuni wasu sun fara dariya tare da kallon Imti wadda ta kame azaune ko kwakwkwaran motsi ta kasayi tunani take mafarki takeyi ko gaske wanene ya sakoshi ba tare da izinin taba kunjifa wata magana seda izininta zaa sake shi.
Abunda ya faru tunda suka fita basi tafiyar mintuna biyar ba D.P.O dayake zaune yana juyawa akan kujerar sa phone dinsa ta fara tsuwwa ganin wanda ke kiransa da rawar jiki ya dauka har dukawa yake kamar yana gaban wanda ya kirashi angama yallabai. Kit aka yanke kiran wayar yabi da kallo wata Number ya dannawa kira kasa zama yayi gaba daya ana dagawa ya fara zazzaga Masifa ku mahaukatan inane da zakuje ku dauko wannan mutumin kunsan koshi wane kuwa kuyi gaggawar juyawa ku mayar dashi ko kuyi ta bakin aikin ku.
Taka burki officer yayi da sauri na baku nanda mintuna biyar kumayar dashi tare da bashi hakuri angama yallabai ayi hakuri munyi kuskure adari da sittin suka jiya kotakan Dad basu bi ba duk yadda yake tambayar su me yasa zasu juya babu wanda ya tankamai sukaja motar asukwane sir Ayub suka kalla I'm very sorry Oga dan murmusawa yayi ya Lumshe idanun sa yana sakin wani murmushi dashi kadai yasan ma'anar sa wannan shine dalilin da wowa da sir Ayub cikin aminci da mutuntawa.
Mrs Baba Bello Abubakar
Comment dinku yana karan karfin guiwa yin comment shiyake tabbatar min kunajin dadin labari na daure kiyi comment sister.
......✍️✍️✍️✍️
💕💕IMTINAN💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Marubuciyar
💕💕 1/ WA'AT free book 💕💕
💕💕 2/ UNCLE J Free book 💕💕
💕💕3/MA'ADANAR SIRRI free book 💕💕
💕💕 And New book IMTINAN💕💕
Page 13&14
Kasa jurewa tai ta dauki jakarta gaba daya tai waje kamar zata tashi sama tunawa tai drive dinta be zoba tsaki take saki ajijjere ko number sa bata dashi ko da yake mezai kawo number dinsa wayar ta. Shikansa Dad din jitai tana jin haushinsa damme zai bari asakeshi ba tare da an wahalar dashi ba zata je gidan ai zataji dalilin dayasa aka sake shi.
Wasu yammatane da suka zo wucewa suka kalli Imti suka kwashe da dariya daya daga cikin su ta kalli ta kusa da ita oh ni mariya yau kinga abunda nagani kuwa ashe karyar arziki ake mana aini na dauka in aka fita da sir Ayub saidai mu hadu a lahira baza'a taba sakin saba sai gashi ko mintuna goma beba ya dawo police din dai suke take mai baya da rarrashin sa da bashi hakuri.
Dariya suka kara sawa suka tafa wadda aka kira mariya tabe baki tai kamar kinshiga Zuciyata Balkis haka nake ayyanawa munyi bye bye da sir amma abun mamaki sai gashi ya dawo kinsan fa ance gaba da gabanta duk jinkan mutum akwai wanda ya shanye shi ya dame wajan ta kama da arziki tafawa sukai ransu fes sukabar Imti awajan tazo iya wuya kamar ta fashe dan bakin ciki.
Number Dad ta kira ring daya ya daga yadai lele shiru tai masa zuciyarta na tafasa katuro wancan talakan yazo tadauke ni kit ta yanke kiran yana zaune a office dinsa AC tana ratsashi tako ina girgiza kai yayi yana murmushi Mamana brigima Allah ya rayamin ke naga ranar Auranki.
Wayar Ziyad ya kira saidata katse ya sake kira kafin Ziyad ya dauka muryar dad ce ta fara dukan dodon kunnan sa kanaji ina kiranka saboda tsabar wulakanci dan kafara cin abinci da jarmiya kaima wai kawaye ko to inna sallame ka seka koma Inda ka futo ai.
Jira yake Ziyad ya bashi hakuri amma shiru kake ji wai malam yaci shirwa cikin ko sawa da kiran yafurta ina jinka kara kulewa Dad yayi yana mamakin girman kai da izzah irin ta Ziyad shiba kowa ba amma sai shegen miskilanci da rainawa mutane hankali.
Inka ga dama kaje kadauko lele kuma kai mata ahankali karka yadda wani abu ya samu yarinya ta inna daureka kaf Niger babu wanda ya isa ya fito dakai dan murmusawa Ziyad yayi sàida Dad yaji fitar murmushi kafin yayi magana kit Ziyad ya yanke kiran sake kiransa yayi afusace sedai kash ya kashe phone din gaba daya lumshe idanun sa yayi yana sakin ajiyar zuciya shiko Dad wane irin ubane da sai abunda yarsa take so shi zata aiwatar koda shi hakane beyi masa bazai taba tsawatar mata ba Mahaifiyar ta dai Mutuniyar kirki ce Allah sarki.
Akalla ya bata kusan 20mnt kafin ya mike ina zuwa kuma Ziyad Shehu me guga ya tambaye shi zanje na dawo yanzu ya furta kamar bayaso binsa sukai da kallo,Hamisu ne yaja tsaki aikin banza waishi wannan meya dauki kansa kamar dan gidan wani yana fama da talauci amma yana yiwa mutane girman kai jifa yadda kaimasa magana yake wani tabe fuska kamar taiba dariya shehu yayi to kaikuma sa idini kasani ko haka Allah ya halicce shi.
Cikin jin haushin Ziyad daya dade azuciyar Hamisu yace bawaninan kawai girman kaine shiyasa abunda waccan yarinyar take mai ni wllh abun bakaramin dadi yake minba sai muga ta girman kai da jiji dakai.Malam manu me gadi ne ya kalli Hamisu koda naji ashe dama Hamisu bakin ciki kake da Ziyad a gidannan to kurwarsa kur ka sakar masa mara yayi fitsari indai zakasa hassada azuciyarka bakaza taba ci gaba ba nadai gayama.
Cikin rashin kunya Hamisu ya kumbura fuska kaga malam manu ina ganin girmanka karka bari nabi takan girman na take shi mezanwa hassada anan kullum yana fama da riga guda daya gwarani kayana akalla sunyi kala goma kaga kuwa ai bazan zauna ina yiwa me riga daya hassada ba. Kecewa da dariya Shehu yayi aikin banza wai harara aduhu kaifa duk wannan hakilon bazaka iya yi agaban Ziyad ba tsoransa ma kake ji amma kazo ka makale anan kana gulmarsa kabari ya dawo saika fada agabansa.
Anki afada din aikin banza wazanji tsoro kaganni nan babu wanda nakejin tsoro kaf garinnan ko agarimmu ni gagara badaune hmm gaskiya kuwa naga alama Lawan dayake gefe ya samusu baki kallonsa Hamisu yayi kaikuma mekake nufi ah ni bance komai ba inkuma kana so nafadi abunda ke raina to tsit Hamisu yayi yasan Lawan yanzu zai iya bankado masa sirrin sa magauta siyi masa dariya daga lokacin ya kashe bakin Hamisu.
Kafin Ziyad ya karasa Imti ta gama hayewa kamar yist sai hura hanci take ga kallon da yan school din ke mata da masu dariya da masu habaici shiyasa gaba daya duniya tai mata zafi tundata hangoshi take auna rashin mutuncin da zata juye masa sàidata kara kamar minti 5 kafin ta mike tana Girgiza jiki tana wani lankwasgewa kamar tar wada.
Da karfi ta fizgi murfin motar kamar zata karyata kala bece mata ba yaja motar suka fita daga makarantar sàidata tabbatar sunje tsakiyar mutane ta kwarara ihu wayyo Allah barawo barawo satoni kuxo ku ceceni kuka take tun karfinta tuni jama'a suka rufarwa motar tunkafin Ziyad yasan abunda zaiyi suka fusgoshi daga motar🙆🙆🙆
Lallai ya jinjinawa kaidin mata haka yake Ayyanawa a zuciyarsa.
Shin yazata kasance wane kalubale ziyad zai fuskanta sanadin sharrin da Imti tai masa.
Zai tsallake ko zai fada tarkonta.
Fusa tattun jama'ar nan wane kalar hukunci zasiwa Ziyad duk kubiyo ni danjin yadda Zata kaya.
Inkin karanta kidaure kiyi comment sisters.
😡😡😡😡 Kuna sacemin guiwa matukar bazakui comment ba zan ajiye alkalamina.
😍😍😍😍Inayin ku irin sosai sosai dinnan.
Mrs Baba Bello Abubakar
.......✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
💕💕Marubuciyar💕💕
💕💕WA'AT Free book💕💕
💕💕 UNCLE J Free book 💕
💕💕 MA'ADANAR SIRRI paid book 💕💕
And New book 💕💕 IMTINAN 💕💕
Page 15&16
Kamar Allah ya aiko su suka rufe shi da duka tsananin bacin raine ya hanashi maida martani wani tsohone yake fadin kudakata kudakata karku kashe shi baji ba gani haka sukaci gaba da jibgarsa dadi kamar ya kashe Imti da kyar wannan tsohon ya tsawatar musu suka dena dukansa Allah sarki Ziyad kansa sai zubar da jini yake haka bakin sa idanunsa kuwa kasa bude su yayi tsabar yadda yasha naushi tako ina hannun sa ya motsa ahankali wata karar azaba ya saki yana da tabbacin sun mai targade imma basu karya shi ba.
Jiniyar motar police ce ta karade titin tuni labari yaje musu ansamu wani matashi yana yunkurin sace wata budurwa,suna zuwa suka tattarashi suka watsa amota ita ma Imti amotar suka sakata taso tai gaddamar bazata shiga motar police ba sàida wata yar sanda ta kusa waska mata mari.
Asibiti aka fara kai Ziyad treatment akai masa wata katuwar plaster aka manna masa aka targadan hannun sa aka gyarashi gaba daya baya iya bude idanunsa da sukai masifar yi masa nauyi da azabar ciwo,kara kwasar shi sukai aka wuce dashi station bayan kanta aka sakashi tuni aka cike masa file cikin masu manyan lefuka Imti tana zaune tana cika tana batsewa kamme Za'a taho da ita ba'abarta ta shiga mota tai tafiyar taba.
Ummee tana zaune Malam manu ya zabga sallama amsawa tai ta bashi izinin shiga kallon sa tai ganin yadda ya shiga tsananin damuwa Malam manu Allah yasa dai lafiya girgiza kansa yayi ai Hajiya babu wata lafiya abubuwa sun cakude nan ya zayyanewa Ummee abunda ya faru.
Dafe kirji Ummee tai tare da mikewa Innalillahi yanzu Imtinan shedancinta harya kai haka oh ni Ameena naga takaina ina zuwa Malam manu asukwane ta haura sama mayafinta ta dauko kamar zata kifa kirjinta har wani bugawa yakeyi saboda tsananin bacin rai.Muje binta yayi abaya har parking space zan fita Malam manu dan Allah kalura karka budewa kowa kofa matukar bako ne harsai na dawo angama Hajiya Allah ya tsare hanya Ameen ta amsa dakanta take driving zuciyarta acun kushe.
Station din da Malam manu ya sanar da ita ta shiga tana shiga kuwa tai arba da Imti wadda ke zaune a kan benci sai kumbura fuska takeyi sam bata ga sanda Ummee ta shigo ba saijin wani zazzafan mari tai a kuncinta saidatai baya kamar zata fadi tsananin gigicewa yasa ta fasa wata kara wadda ta jawo hankalin yan sandan.
Kara tsinka mata mari tai har huci Ummee keyi saboda bacin rai zata sake kara mata wani marin wata yar sanda tai saurin rike hannunta haba Hajiya ya za'ai kishigo gaban hukuma kina daukar doka ahannun ki komene tsakanin ku be kamata ki biyota har nan ba Ummee fizge hannunta tai anki abari koke kika tsugunna kika haifarmin ita da harzan mata hukunci kirikeni ko kinsan laifin data aikata.
Kallontà ta maida kan Imti kinji na rantse da Allah kamar yadda ya shiga bayan kanta kema sai kin shiga matukar ni nai nakudarki kika fado duniya.
Cikin tashin hankali Imti ta mike jin wai bayan kanta Ummee take kokarin a sakata caraf Ummee ta rike rigarta sarai ta gane nufinta so take tataka da gudu ta fice daga police din sarai tasan wacece Ummee inta fadi abu tofa saita aiwatar kallon yansada matan da sukai tsaye suna kallon ikon ALLAH tai kuriketa matukar Kuka barta tafita kunyi ta aikin ku kallon Ummee sukai daga sama har kasa tabbas wannan badaga tsiya ta fito ba tundaga yanayin fatar ta da Gold din dake zagaye da wuyanta kunne hannu ga zubuna da sukai kawanya a yatsun hannun ta.
Kam suka damke Imti wadda ta fara kuka wiwi da san zillewa office din D.P.O Ummee ta wuce takai kusan mintuna goma kafin ta fito umarni ya bayar akai Imti bayan kanta babu wata damuwa Ummee ta fada Motar ta tai waje bacin ranta yana sauka ahankali.
Babu wani bata lokaci suka tura Imti bayan kanta tana Kuka da kiran Dad dinta wajan da aka sakata yana fesin din inda aka saka Ziyad yana zaune yadda jiri yake dibarsa bayajin zai iya tsayawa akan kafafunsa kiyayyar Imti ta samu wajan zama azuciyarsa aduniya babu wadda ya tsana yanzu sama da ita bashi da makiyi tamkarta sanadinta gashi awani hali babu wanda zai fiddashi sai Allah.
Tun yanajin kamar kunnan sa ke jiyo masa muryarta harya gasgata da gaske yakejin kukan nata ahankali yayi juriyar mikewa itance kuwa tana tsaye tana rusar Kuka wannann fa shine kaikayi koma kan mashekiya tunanin sa meya kawota bayan kanta. Sauraye da wasu kwari kebin Imti data rasa menene ga zarnin fitsari daya gigita rayuwarta glass din data kwama a face dinta tuni ta cire shi yayi nasa wajan Ummee sàidata kwace hand bag dinta kafin tatafi babu wata waya da zatai amfani da ita wajan kiran Dad.
Wani Murmushi ya saki hakanan yaji wani Farin ciki ya cika masa zuciya kobe fadaba kaso 100 na bacin ransa 50 ya tafi hango Imti kadai ya tafi da bacin ransa kamar yadda tasashi amasifa itama gatanan acikin ta. Ajikinta taji ana kallonta dago idanunta tayi da sauri wadanda suka kumbura tsabar yadda tai Kuka caraf suka hada idanu wani murmushin tura haushi ya kara sakar mata waro idanu tai tana kallon sa murmushin ubamme yake mata to lallai zai gane kuransa asanadin sa Ummee tasa aka sata a cell.
Inkin karanta kidaure kiyi comment sister.
Mrs Baba Bello Abubakar
......✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris Ismail
💕💕 Marubuciyar💕💕
💕💕 WA'AT free book 💕💕
💕💕 UNCLE J Free book 💕💕
💕💕 MA'ADANAR SIRRI paid book 💕💕
💕💕 And New book IMTINAN free book 💕💕
Page 17&18
Kawarda kanta tai cikin tafasar zuciya akansa Ummee tai mata haka ta fifita wani talaka can akan yardata haifa tayadda ta amince Ummee bata kaunarta batason ganin farin cikinta tun tasowarta bata taba yin abunda Ummee ta yababa kullum cikin kusheta take to yau ga karshan kiyayya da hannunta ta damkata asata a cell sake rushewa da kuka tai kamar zautacciya.
Ummee hankalinta kwance ta koma gida ita ma ta dandana taji zafi da zugin da Ziyad din yaji ko yayane tasan yadda akejin radadi da kuna tunda ita a rayuwarta babu abinda ta sani sai gata da sangarta.
Dad tin yana kiran Imti harya gaji da tunanin ko bata kusa da wayar ne sai yamma lis ya dawo tundaga bakin kofa yake kiran Mamana Mamana shiru Ummee tana jinsa tai masa banza taking steps yayi ya leka dakinta bata ciki sakkowa yayi ya kalli Ummee wadda ta hakimce a parlor tadau wanka kamar batada wata damuwa Aminatu ina Imtinan aica nake ni ba mutum bace bani da mutunci da kimar da zaka shigo kaimin sallama sanin kanka ne ba coci ka shigo akwai musulma acikin Gidan.
Dan murmusawa dad yayi kefa dadina dake daukar zafi menene to na cewa senai sallama Indai nayi azuciyata ai ya wadatar ni beyimin ba yadda kowane magidanci zai shiga gidansa cikin Aminci kaima ka dinga shiga haka to naji yanzu kifadan ina Mamana mikewa tai muje kaci abinci harzai magana ya fasa.
Saidata tabbatar yaci yayi kat tukunna ta muskuta kana tambayata ina Imti ba gyada matakai yayi tana station kamar dolo haka yake kallon ta yana tunanin inacena station kinga kifito ki fadamin inace station au wai baka gane ba ina ake kama masu laifi to tanacen garkame acikin cell zumbur Dad ya mike wace maganar banza kike fadamin haka yar tawa akasaka acell toko uban wanene yayi wannan gangancin bazai kara marmarin sake yinsa ba.
Murmushi Ummee ta sake ok Allah y bada sa'a zaka iya fita lalubanta akaf station din dake garinnan kaji na rantse wllh bazan fada maka ba Allah y bada sa'a mikewa tai ta haura sama tabar Dad atsaye jikinsa na rawar tashin hankali.
Babbar rigarsa har tadeshi take wajan sauri jiyai driving dinma bazai iya ba Shehu ya kalla kai ina Ziyad bayanan yallabai ina ya tafi muma bamu sani ba,Hamisu yanasin magana Lawan ya takemai yatsun kafa dan dole yayi shiru yana muzurai,barin wajan yayi ya fada mota aguje ya fizgeta duk wani station daya sani sai daya zagaye shi amma magana dayace ba akawo yarinya ba nan fa tashin hankalin Dad ya karu sai zabgawa Ummee kira yake tana gani taki dauka.
Harya fidda rai zai koma gida ya tuna da wani juya kan motarsa yayi ya nufi hanyar police station din yana parking yaga motar gidansa a parking space hakanne ya tabbatar masa Imti tana ciki. Rai bace ya shiga kamar kububuwa sannu da zuwa yallabai ko kallon su beba ya nufi office din dpo kamar ankoro shi haka D.P.O yaga Dad sai haki yakeyi sam bai lura da Wadanda ke office dinba masifa ta rufe masa idanu.
Ina yata metai za'a wulakanta ta to bazan taba yadda ba daganan har kotun koli semunje daku ammana shari'a,kayi hakuri ka zauna Alhaji abun duk bana fada bane zai sake magana Abba ya tari numfashin sa sannu me ya nace sannu tunda mu gaba daya daga sama muka fado sai Lokacin Dad ya lura da mahaifinsa sai yayansa Abubakar daya kafe Dad da ido kamar akansa aka fara haihuwa.
Mikewa Abba yayi ya mikawa d.p.o hannu suka sake gaisawa wani kurtu ya bawa umarnin afito dasu Imti har Ziyad din. Imti na fitowa tai arba da Dad dinta daya rasa kan maganar ganin Ziyad ma yafito abun ya sake daure masa kai towa ya kawo su garin yaya ko shune akai musu dagudu ta fada jikin Dad wanda ya lula Duniyar tunani shafa kanta yakeyi yana buga bayanta.
Abba ne ya matsa kusa da Ziyad yana kallon sa sannu ziyadu murmushi ya saki ina wuni yadan sunkuya dan gaida Abba lafiya lau Ziyad kayi hakuri kaji babu komai ya furta ahankali nagode dan murmushi Abba ya saki haka nan Ziyad yake burgeshi yaro me hankali,kallon Imti tai wadda ta makale ajikin Dad tana rusar kuka harara Abba ya watsa mata matukar bazaki hankali ba nina san matakin da zan dauka akanki ko uban naki be isa ya ketare umarnina ba balle ke karki bari na waiwayeki Aisha.
Tsabar takaici yaya Abubakar kasa magana yayi ganin yadda yasata agaba kamar zai fashe da Kuka soyake su kebe yaji wane me tsautsayin ne ya sata a cell,zaka wuce kutafi ko ciki zaka maida ita gaba yayi tare da rike hannun Imti kuje Ziyad Allah ya kara sauki kudi Abba ya mika masa akallah zasiyi 50k ga wannan kasiyi magani girgiza kai yayi alamun bazai karbaba batarai Abba yayi banyi maka dan na raina samunka ba sai a matsayinka na jikana.
Kallon Abba yayi gyada masa kai Abba yayi kaima jikanane Ziyad karbar kudin yayi ngd ya furta ahankali yataka yabar wajan baya ya bude ya shiga Dad haushi ya cikashi ganin yau zaiyi driving din maaikancin sa wanda yake ci akarkashin sa. Sai sakin tsaki yake kamar tsaka shidai Ziyad jingina bayansa yayi da kujerar ya Lumshe idanun sa jin yadda kansa yake matukar Sarawa kamar zai tarwatse.
Inkin karanta kidaure kiyi comment sister.
Mrs Baba Bello Abubakar
.....✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
💕💕 Marubuciyar 💕💕
💕💕 WA'AT free book 💕💕
💕💕 UNCLE J Free book 💕💕
💕💕 MA'ADANAR SIRRI paid book 💕💕
💕💕And New book IMTINAN free book 💕💕
Page 19&20
Tunkan Dad ya gama daidaita parking ya balle murfin ya fito tsura masa idanu su Malam manu sukai ganin katuwar plaster a goshinsa daga musu hannu kawai yayi ya wuce dakin da yake kwana wani dan karamin dakine da katifa irin ta yan bording sai jakar kayansa da basufi kala biyune aciki ba katifar yahau ya zauna har wannan lokacin zuciyarsa zafi takeyi akan abunda Imti tayi masa.
Zazzafan huci ya furzar wanda yake jinsa ya tsaya a mako shinsa hannunsa ya kalla dayake masa ciwo har wannan time din wata tsuwwa hannun keyi masa rufe idanun sa yayi kamar me bacci.
Dad da kansa ya ruko yar mulkin sai matsar kwallah takeyi Ummee na zaune a parlo babu abunda ya dameta kallon su tai yadda suka shigo rikici rikici,mikewatai afusace ta dakawa Imti tsawa koma kiyi sallama kona canza miki kamanni jiki na rawa ta matsa daga hannun Dad sosai tsoran Ummee ya mamaye zuciyarta komawa tai da baya kafin tayi sallama sàida Ummee ta tabbatar taji sallamarta sannan ta barta ta shigo hanyar dakinta ta nuna mata sum sum ta bar wajan.
Cikin takaici Dad ke kallonta wai Amina menene yahau kanki da zaki dinga yiwa 'yarki irin wannan hantarar kamar ba jinin ki ba, kauda kai Ummee tai Alkasim Ummee ta ambaci sunan sa sunan da ya dade bejeshi abakin taba numfasawa tai kafin taci gaba bazaka taba sanin iya adadin kaunar da nakewa Imti ba karka manta ni nadau cikin ta tsahon wata tara bantaba gajiya wa ba sedata fito duniya ne zan kosa.
Ina sonta fiye da yadda kake sonta ni ina bida sonta ta hanyar data dace kaima ina so ka bida son da kake mata ta hanyar data dace mikewa tai ta barmasa wajan binta yayi da kallo yana nazartar maganarta.
Dan tsaki ya saki ita fa Ameena tana da matsala haka kawaii Allah ya bashi ya daya tilo saiya shigar mata rayuwa ya hanata sukuni ina bazai taba yiwu ba. Barin parlour yayi ya haura dakin sa.
Safa da marwa kawaii yake acikin dakin sa duk yadda yaso ya goge Abunda Imti tai masa ayau ya kasa hannun sa ya kalla daya sake kumbura akaf tarihin rayuwar sa kujewa betaba yiba balle tar gade asanadin waccan me kama da aljanar wane mataki ya kamata ya dauka akanta kwafa yayi kan yar katifar sa ya fada idanun sa yayi jajawur jijiyar kansa tai rada rada lumshe idanun sa yayi kamar me bacci amma abubuwa yake sakawa masu yawa aransa.
Yayi kusan sati baya driving saboda hannun sa Dad da kansa yake kai Imti school yaje ya dauko ta sangarta da Iskanci sai Abunda ya karu.
Karfe 10pm Ummee tafito daga dakinta kishirwa ce ta futo da ita hango dakin Imti abude shiya dakatar da ita tadanyi mintuna atsaye kafin ta karasa dakin hango ta datai a kan bed shiyasa tai kokarin juyawa amma sai Zuciyarta taki bata damar hakan,shigowa dakin tai sosai tana kare masa kallo kan bed din ya sake kalla bata taba ganin Imti ta rufe har kanta ba saiyau karasawa tai ta yaye blanket din Abunda taganine ya sata zaro idanu waje.
Fulalluka aka jajjera bazaka taba cewa ba mutum bane toilet ta leka babu Imti ba labarinta saidata karade gidannan kaf bata ganta ba gaba daya zufa ta wanke mata fuska Zuciyarta ba karamin bugu take ba. Harabar gidan ta fita ko ina tarwai da haske wajan Malam manu ta nufa sallama tai masa ya amsa sannu da fitowa Hajiya yawwa dama nace ko kaga Imti ta futa.
Eh Hajiya tafuta tun wajan karfe 9 meyasa ka bude mata bani da hurumin hanata Hajiya tunda ba aban umarnin karna bude mata ba barin wajan tayi kamar zata kifa tana tunanin ina tatafi da wannan daran, fitowar sa kenan ya hango yadda Ummee ke zuba sauri ko ganin gabanta batayi ahankali ya tako har kusa da ita Ummee ahankali ya furta sunan batare da yasan hakan zai fito daga harshen saba cak ta tsaya ahankali tajuyo ganin idanun ta cike da kwallah yasashi kawar dakai.
Ummee tana da wata daraja da kima a idanun sa macece me matukar karamci matukar ta ganka adamuwa zatai iyaka kokarin ta wajan ganin ta magance ma matsalar ka iska yadan busar daga bakin sa,meyasa meki Ummee sedata danyi jim kafin ta furta dan Allah Ziyad ko kasan inda Imti tatafi girgiza mata kai yayi alamar àah cikin sanyin jiki ta juya daniyar tafiya,zan lalubo miki ita cak ta sake tsayawa kafin Zuciyarta ta cika da farin ciki Nagode Ziyad Allah ya faranta maka kamar yadda ka faranta min Ameen ya amsa akan labbansa.
Da sassarfa yabar wajan binsa da kallo Ummee tai inama shi ne danta ba Imti ba ta tabbatar Mahaifiyar sa tayi saar da gaba tayi ta shige parlour ta zauna zaman jiran tsammani.
Kai tsaye wani club ya nufa yana da tabbacin tana can duk wani kwaro da kwaruwa awannan babban club din zaka sameshi matukar yanaji da kansa.
Tunda ya shiga harabar wajan yake karewa wajan kallo mata da mazane sai parking suke babu me fita saimasu shiga babu me shigar arziki acikin su wasu daga pant sai bra kai Abunda babu kyan gani. Wasu matasa ya hanga da suke zaune sun zagaye wani matashi da alamar shima babban kaine ahankali ya fara takawa dan giftawa ta inda suke muryar wani matashi yaji ta daki dodon kunnan sa VK yaufa tsuntsuwar daka dade kana hari tazo hannu aiki ya kammala.
In bakwa comment zan aje alkalamina.....✍️✍️✍️
Mrs Baba Bello Abubakar
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 21&22
Wani shegen murmushi wanda aka kira Vk ya saki cocaine din hannun sa ya zuka aikin ka nakyau Nazi kace yau zanyi uku sau uku ihu suka sa tare da tafawa irin nasu na yan duniya,gaba yayi tamkar beji Abunda suke tattaunawa ba tunda baya gabanshi ba kuma hurumin sa bane. Amma, hakanan yaji yanason yasan wace yarinya ce wannan cikin club din ya shiga wasu azazzaune wasu na rawa da Dala suke yiwa masu rawar liki sukuwa sun zage baji ba gani rawa suke da anwatsa kudi akwai masu kwashewa su adana daga gefe.
Girar sa yake dan sosawa daya bayan daya yakebin wajan da kallo amma kome kama da Imti be gani ba dan fara takawa yayi ahankali fuskarsa adaure tamau kamar besan menene dariya ba haka yadinga dubawa sako da lungu babu ita ba dalilinta shikansa ya gaji badan Ummee ba babu yadda za'ai ta Fito Iskanci yataho nemanta.
Dan dakatawa yayi danya dan huta kamar ance ya kalli gefansa wani room ne me kofar glass wani babban daki ya hango kamar mutum yake hange akan gadon harzai basar yaji yana bukatar dubawa da sassar fa ya tura kofar glass din idanun sane ya fada akanta daga ita sai wata riga iya cibiya da dan mitsitsin wando runtse idanun sa yayi cike da takaici kara kyamar Imti yayi a Zuciyar sa dakin yashiga kamar ya dauki kashi haka ya tattaro ta gaba daya ya fito da ita.
Hanyar da yasan bamutane tanan yabi harya sata amota babu wanda ya lura dashi jan motar yayi yafice daga club din baki daya Zuciyar sa tana daukar zafi ya tabbatar da Imti ballagaza ce ta ajin karshe mara kamun kai yana da tabbacin ta gama zubar da mutuncin ta tun tuni yadda titin yayi tsit hakan ya bashi damar sheka gudu sosai hon ya danna megadi ya wangale masa get din ya shiga.
Tunda Ummee taji karar mota ta fito da hijab dinta har kasa har neman faduwa take wajan leka motar ajiyar zuciya ta sauke ganin Imti aciki saidai kamar bata hayya cinta,kallon Ziyad tai idanunta na cikowa da kwallah face dinta dauke da murmushi Ngd Ziyad Ngd abunda take furtawa kenan takasa magana murmushi yadan yi bakomai Ummee yiwa kaine.
Amma Ziyad kamar bata Numfashi dan karkacewa yayi ya kalleta bacci take dan Allah taimaka ka dakko min ita dan jim yayi kamar bazai dauketa ba,muryar Ummee yaji tana fadin kayi hakuri na takurama ko, da sauri ya dauko Imti ko kallon Fuskarta baya kaunar yi har dakinta Ummee ta nuna mai ya direta akan bed ya fice kare mata kallo Ummee tai bacin ranta na sake hauhawa lallai ta yadda Imti tayi nisa zata tatashi ta sameta seta kusa kasheta dan duka.
Ficewa tai rai bace Dad yanacan yanata sharar bacci bemasan abunda ya faruba hankalin sa kwance yake antaya bacci.
Alwala Ummee ta dauro nafila tayi ta dade azaune tana Addu'a ALLAH ya shirya mata Imti yasa ta dawo hanya madai dai ciya. Karfe 6 Ummee ta futo daga room dinta da wata shegiyar bulala sai sheki take afusace ta shiga dakin Imti abunda ya matukar bata mamaki yadda aka ajiyeta jiya haka take da alama ko muskutawa batai ba ras taji gabanta ya fadi ware idanun ta tai tana sake kallon ta.
Yadda bulalar hannun ta tayi ta haukan bed din girgizata tai amma ina bawani labari hannunta ta kama tana saki ya tafi luuu innalillahi Imti meya sameki sauke hannun tai da sauri ta fice daga dakin Dad yana kwance yana sharar bacci bubbuga kafar sa tai dady ka tashi ba lafiya gyara kwancuyarsa ya sake yi wai mene haka Ameena ina bacci zaki dinga damuna.
To Imti ce ba lafiya tunkan ta rufe baki ya mike har neman kayar da ita yake asukwane ya fada dakin gaba daya yasata ajikin sa Imti Imti kallon Ummee yayi da hankalin ta yayi matukar tashi idanunta har sunfara zubar da hawaye dan tabbas in har Imti bata mutuba to tana cikin wani hali daukarta Dad yayi zai fita da ita rike shi tai dawo min da yarinya nasa mata kayan mutunci inma mutuwa tai aganta da suttura ajiki duk Abinda ya sameta wllh bazan yafe maka ba sai Allah yayi mana hisabi tsakani na dakai fusgo Imti tai wata doguwar riga ta dauko ta saka mata.
Sai karamin hijab data kara mata dashi saika dauko ta gaba tai tabar shi awajan sun kutar Imti ya sakeyi tunda suka fito su shehu suka mimmike sunsan ba lafiya ganin yar mulkin a hannu kamar matacciya.
Da sauri Ziyad ya mike ko basu fadaba yasan ba lafiya ba mota ya shiga daidai lokacin dad ya bude back sit ya sakata aciki shima yashiga Ummee na kokarin shiga ya ture ta dole ta hakura tashiga gidan gaba.
Alkhairat teaching hospital ya nufa dasu dayake asibitin na kudine suna zuwa da gaggawa aka amshi Imti emagency aka shiga da ita sam Ummee da Dad sun kasa zaune sun kasa tsaye zagaye kawai suke na tsananin damuwa da tashin hankali tun suna sa ran ganin Doctors din su fito har suka sare akalla sunkai awa daya da rabi kafin su fito suna sharce gumi.
Alama sukaiwa Dad akan su biyo su office din babban likitan suka shiga zama sukai gaba daya suka zubawa doctor din idanu,glass din face dinsa ya cire tare da sharce gumi daya tsatstsafo masa agoshi Numfashi yadan sauke mikawa Dad hannu yayi sunana Doctor Muhammad Umar gyada kai Dad yayi Alhaji Alkasim Kamalu sake musabaha sukai file ya dakko ya sunan mara lafiyar Aisha Alkasim kamal cikewa yayi kafin ya maida kallonsa kan su Ummee.
Ya akai hakan ta faru Alhaji kallon rashin fahimta dad yakebin doctor dashi ban fahimceka ba,asaka makon yarinyar tasha kwayar datafi karfin kwakwalwarta in har ba Allah ne ya taimaka ba hakan ya taba Brain dinta zata dinga abu kamar na marasa hankali amma matukar Allah ya dafa mana zamiyi Iya kokarin mu ganin min dakushe wannan matsalar.
Idanun Dad kamar zasu fado kallon bakin Doctor kawai yake yarsa ce take shan qwaya kukan Ummee ne ya katse masa tunanin da yafada cikin kuka Ummee ke fadin katemaka doctor ita kadai Allah ya bamu ko nawane zamu kashe dan Allah kayi iya kokarinka na ganin bata rasa tunanin ta ba.
Kiyi hakuri Hajiya karki manta komai na ALLAH ne ba abun mamaki bane ya bata lafiya ta warke kamar ba ita ba fatammu daya kudage da Addu'a kuma duk yadda zaai karku barta takara aikata kuskure irin wannan zata kashe rayuwar tane da kanta gyada kai Ummee tai Dad tuni wutar kansa ta dade da daukewa jiyayi duniya tana juyawa dashi shalelen tasa ce zata zama mahaukaciya.
Da kyar ya tsaya akan kafafun sa dakin da aka kwantar da ita suka shiga wasu na ura aka jajjona mata aka ta jikin computer dakin suke ganin yadda suke jujjuyawa akan ta wani hawaye Dad yaji ya taho masa kamar karamin yaro haka ya fashe da kuka Ummee jitai kamar ta rufeshi da duka ko kallo be isheta ba balle ta rarrasheshi duk wa yaja musu Inba shiba ya daura mata yarinya akan hanyar da bazata taba bullewa da ita ba daga karshe ficewa tai tabar masa dakin.
Comment dinku na karfafamin guiwa.
Mrs Baba Bello Abubakar
.......✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 23&24
Wasa wasa saidai Imti ta kwashe 2weeks a gadon asibiti ko yaushe asibitin cike yake da yan uwa da abokan arziki su Fidy sunzo dubata har kuka seda sukayi saboda ganin halin da Imti take ciki tarame tayi fari sosai kamar babu jini ajikin ta Ommu ce awajan ta sai Ummee yarbi dabi suke har Maman Ummee ita ma wani zubin tana kwana awajan ta kowa kagani cikin damuwa suke akan abunda ya sameta duk da dayawan mutane basu san abunda ya sami Imti ba.
Akalla ta farka kusan sau uku amma gaba daya acikin maye take tashi tadinga bige bige kenan abunda ya kara tashin hankalin Dad da Ummee kenan tayi Kuka kamar idanunta zai tsiyaye haka Dad bashi da aiki se Kuka duka ya rame ya fige kamar bashi ba. Shima Abba ya shigo damuwa sosai na halin da jikarsa take ciki shine yake dan kwantarwa da Dad hankali dayi masa nasiha akan yadda da kaddara har gwara Ummee tafishi tawakkali shiko ai dan karamin zararre ya koma.
Tana cika sati biyu ranar wata laraba Imti ta farka cikin hankalin ta Ummee kamar ta zuba ruwa akasa tasha da sauri ta matso gabanta Imtinan kin gane ni kallon rashin fahimta Imti tai mata najin tambayar da take mata meze hanata ganeta ita kuwa gyada mata kai tai alamar eh tare da jin haushin tambayar da Ummee tai mata kamar wadda tawarke daga ciwon hauka zatai mata wannan tambayar.
Dad ne ya shigo har babbar rigarsa na neman tade shi Mamana kallonsa tai taga yadda yaketa washe baki dakin ta kalla sai Lokacin ta lura a asibiti take dan kallon Dad tayi alamun tambaya ne akan fuskarta shafa kanta yayi alhmdlh Mamana ta warke Ummee ce ta rike hannun ta inane yake miki ciwo girgiza kanta tayi amar bakomai doctor ne ya shigo sake auna Imti yayi babu wata matsala madam Kuka ya kare dan murmushi Ummee ta saki Ngd doctor Allah ya saka da Alkhairi ameen Hajiya Allah ya kara lafiya Ameen ta amsa kafin ya fice.
Sàida Imti ta kara 1 week kafin asallameta ta warke garau sosai Ummee take tattalinta dayi mata nasiha ako da yaushe Dad shima ba abarshi abaya ba sai riritata yakeyi kamar kwai haka yakeji da ita.
Ummee da kanta ta shiga kasuwa ta dinkowa Imti hijabai da mayafai na arziki amma me Imti daka tsalletai alambar bazata sa wannan abun zafi ya kashe taba tun Ummee na ganin abun nata wasa ne harta tabbatar da gaske take aiko sekinsa konai miki dukan kawo wuka dan Ubanki ji nake kinyi hankali yadda kikaje kika shawo Abunda yafi karkin kanki da yanzu kinacan kinabin bola bola shine har yanzu bazaki san daidai da akasin sa ba.
Kuka Imti ta faahe dashi nidai wllh Ummee bazan sa wannan kayan nauyin ba saidai kibawa wahalalliya ta saka dauketa da mari Ummee tai nice wahalalliyar kenan sakayyar da zakimin kenan Imti ni kike kallon tsabar idanuna kice mun wahalalliya to zangani ke kika haifeni ko nice na haifeki muzuba dani dake shege ka fasa watsa mata kayan tai ajiki ta fice tabar dakin Kuka Imti ta kara saki ita dai ta yadda Ummee bata Kaunarta ko kadan in banda rashin adalci zamanin su nada da wanda aka haifota ayanzu ai akwai banbanci kome zatai bazata sa wannan kayan ba.
Tadade tana kuka kafin bacci ya dauke ta Allah sarki Ummee duk yadda taso rike kanta batasan sanda ta fashe da kukan bakin ciki ba tarasa wace irin yarinya ce Imti da batajin magana ko kadan babban burinta ako yaushe ta nuna mata bata isa ba, ita bakowa bace awajanta face me dafa mata Abinci bata isa ta bata umarni tabi ba wai yartace take mata wannan dibar albarkar agaban ta tace bazatabi Abunda take so ba daga hannunta tai sama hawaye na kwarara a Fuskarta astagafirullah Allah na tuba idan wani laifi na aikata abisa kuskure ka jarafce ni da haka Allah ka yafe mini karasawa tai cikin Kuka wanda tundaga kasan zuciyarta yake tasowa.
Yau take Monday yaune kuma Imti zata koma school karfe 9 ta sauko da hand bag dinta a hannu riga da sket ne ajikinta sun masifar dameta rigar yadda kasan babu kafada ajikinta gaba daya kirjinta awaje yake street sket ne tsagarsa ta wuce guiwa sosai kanta yasha gyara wata kalba akai mata me kala biya gaba daya gashin an sanza masa kamanni ansa blue ga brown ga baki duk agashi daya gaba daya tafita daga kamannin musulmai.
Tundata sakko Ummee take binta da Kallo kamar zata amayo da zuciyarta yadda zuciyar ke mata zafi da radadi idanunta har wani yaji yaji yakeyi tsam ta mike tunkan tai magana Dad ya daga mata hannu karkice komai kemeyasa ko yaushe bakinki baya taba fadin alkhairi sai akasin haka har yaushe ta farfado daga cuta dan Allah karki sake maida ita ruwa karki dora mata wata cutar.
Kur Ummee ta tsura masa idanu ko kiftawa batayi jujjuya kalamansa kawai take acikin zuciyarta kirjinta har dagawa yake saboda yadda ranta yayi kololuwa wajan baci tana kallo Imti tazo ta wuce ta gabanta ko arzikin kallo bata samu ba balle kuma tagaishe da ita kamar andasa Ummee haka ta koma atsaye har wannan lokacin.
Tunda ta fito turaranta ya sanar dasu ko wacece zubo mata idanu su Lawan sukai sunyi tunanin cutar datai zaisa tayi laushi ashe ba haka Abun yake ba anya wannan yarinyar babu aljanu ajikin ta gudun karta kamasu suna kallon ta yasa su kawar da kawunan su daga kanta Allah ya shirya baba megadi ya furta daidai sanda take karasowa wajan.
Jatai ta tsaya tare dayin kasa da glass din fuskarta wane me warin bakimme yayi magana acikin ku shiru sukai ba wanda ya tanka wata tsawa ta daka musu ba magana nake muku ba nine Ziyad dayake kishigide ya furta batare da yadago ya kalleta ba kansu suka mayar kansa da mamakin siyan fadan da yayi sunsan wanda yayi maganar amma shi yasiyi fadan.
Kamar zata kifa takarasa inda yake tanai masa wani wulakantaccen kallo amatsayinka nawa kake min fatan shirya aini ashrye nake munafuki algungumi wanda tsiya tai maka katutu kaf dangi babu kasamu adan dauke ka za'a rufama asiri kakewa masu gida rashin kunya,to abunda ubana yake baka senayi sanadiyyar daka rasa shi se akoma kauye afara noma.
Ko kallonta beba dan bashi da lokacin ta ayanzu yana da abubuwa agabansa bata isa ta katse masa tunani ba mikewa yayi babu wata damuwa a zuciyarsa binsa tai da kallo anya wannan kare be lashe mai zuciya ba tadauki alwashin saiya bar gidansu tunda bana ubansa bane tuni ya shiga mota ita kadai yake jira yaja su tafi bam ta bame motar bayan ta shiga sai jan tsaki take tana harare harae kamar idanunta zasu fado.
Inkin karanta ki daure kiyi comment sister.
Mrs Baba Bello Abubakar
.....✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 25&26
Wayarsa ce ta fara ring cirota yayi daga aljihu wata kwarababbiyar wayace tasha kyauro bayanta ko murfi babu Imti kwashe wa tai da wata shegiyar dariya tana nuna wayar hannun sa har kwanciya tai dan dariya cikin Dariya take fadin eh lallai na yadda kai talakan talak ne zaka iya rokata na canza ma waya kasan akwai arzikin gaba da baya.
Kamar beji abunda ta fada ba haka ya kara wayar akunnan sa ina kwana inna huraira maimaita sunan tai ta sake shekewa da dariya Allah ya bashi lafiya taji ya amaba ta a hankali zanzo in sha Allah katse kirani yayi kallon sa tai cikin dariyar izgilanci take fadin kace tsohuwa me dattin zani ce taikira ka ja gako tafiya kauye ya kamaka sai abarwa mutane Gida ko yadaina tsamin dauda.
Duk da ransa ya baci amma be nuna mata ba daidai lokacin suka shiga cikin school din motar aka zubawa idanu dan ansan motar daga ina ta fito,sedata gama shan kamshinta kafin ta bude murfin motar tafito matasa da yammatan wajanne suka zubo mata idanu samari sai gyara zaman riganr su sukeyi ko Allah zaisa su burge Imti.
Matan kuwa kishine ya turnike su duk yadda kake zatan ka dauki wanka idan Imti ta shigo school din gaba daya tauraruwar su dusashewa take cike da bacin rai suke kallon ta harda masu jin kamar su tashi su hauta da duka amma ba dama. Wani kallo ta watsa musu ganin yadda suka zubo mata idanu kamar zasu cinye ta tsaki taja dan ta tsani kallo arayuwar ta hand bang dinta ta sake rikewa kafin ta fara tafiya cikin rangaji da kwalisa.
Binta sukai da kallo addu'ar su bata karbu ba kenan tun sanda sukaji labarin rashin lafiyarta suketa Addu'a ALLAH yasa ta mutu sa huta ko mazan school din zasuyi tatasu saidai kash ga shegiyar ta dawo da batanan harsun faracin kasuwa amma tunda ta dawo har sun fara ganin canji daga wajan samarin su.
Kamar wahainiya haka take takawa karar ta kalmanta ne ya jawo hankalin yan class din juyowa sukai dan ganin wace gwanar ce wannan kamar wadda ta daura kacau kacau akafa Fauza ce ta saki Murmushi ganin mutuniyarta taji sauki cik sir Sagir ya hade Fuskar sa tun sanda ya nuna yana san Imti tai masa wulakanci daya ganta yake hade rai kamar be taba dariya ba kallon kallo sukai a tsakanin su kawar da kansa yayi kamar yaga kashi tsaki taja ta nemi wajan zama ta zauna kafa daya kan daya ta dora tana girgiza kafarta.
Kowa ya dakko pepper zami test zura masa ido kowa yayi wane irin abune wannan babu shiri kamar tashin duniya yace test murmushi Imti ta saki tasan abun dake ransa saboda ita yace zeyi test din tunkan kowa ya dauko pepper ita ce ta fara dakkowa rai bace ya fara rubuta zafafan tambayoyi kallo daya taiwa white board din kan yakai karshen question ta amsata yana ajiye maka tana ajiye biron hannun ta yadda ajin yayi dif kowa kansa yadau charge harda masu yarfe gumi ya matukar shammatar su.
Jingina tai tana kallon kowa daya bayan daya mintuna biyar na cika ya fara karba ko kinyi ko bakiyi ba ke kika sani yana zuwa kan Imti ya fige pepper din kamar zai yagata fuuu ya fice daga class din binsa tai da kallo tana sakin wata shakiyiyar dariya lumshe idanunta tai tana kallon su Lubnah da suka zuba mata idanu shedan cin Imti yana matukar basu tsoro sunyi zatan inta tashi dawowa zasu ganta da zumbulelen hijab har kasa kosu ganta da mayafi na mutunci amma se suka ga sabanin haka.
Allah ya shirye ki Imti Lubnah ta furta cike da damuwa da zuciya daya suke zaune da Imti sunajin zafin yadda tamaida rayuwarta kamar mara mafadi karanta takeci babu babbaka,tsaki Fauza taja dama kowa neman shiryar Allah yakeyi Munafurcin bamza ku waya san abunda kuke aikatawa ba gwandama wanda ya fito fili ya shana ba akan me fuska biyu abaka musa aciki fir auna.
Kinga Fauza in ana magana da mutane kidaina saka baki baki kai matsayin da zamu zauna muna goga kafada dake ba bayanma Imti ta jawo mana raini ina mu ina zama dake a inuwa daya kigayamin kaf garinnan wanene yasan da zaman Ubanki mukuwa fa babu wanda zata fadi sunan Ubanta akasa sanin shi cikin kunan rai Fidy ta gama fadin haka.
Afusace Fauza ta mike ta shaki wuyan Fidy harni zaki dinga zagi har nawa uban naki ya tara da zaku dinga hurawa mutane hanci ko kawa ce ta sarke Lubnah ce ta shigo tsakiya danta rabasu yan aji shewa suka saka yau angan su arana Imti tana zaune ko motsawa bataiba balle tayi yunkurin rabasu,tabe baki tai duk wanda yaji ajikinsa zai bari.
Saida kyar wasu yammata suka raba fadan duk anya kushewa Fauza fuska dama fuska tadau mai seta zama kamar wata aljana sai zage zage takeyi kamar wata zararriya,kinga Fauza ki kyale kunnu wanmmu su huta haba sai faman ihu kike wa Mutane aka shiru tai da yake Imti ce tai magana sai girgiza kai take kamar kadan garuwa.
Kima barta yar matsiyata kawai bacin yau ba nagobe ta dinga hurawa mutane hanci shiru sukai sai faman harare harare suke yi Boss tayi magana shiyasa ko waccan su tayi shiru har aka tashi babu wadda ta sake kula wani.
Karfe 5:30 da rabi Ziyad yayi sallama a kofar maine parlo Ummee dake zaune tana kallo ta amsa da fara'a wa nakeji kamar Ziyad eh nine to shigo mana ai kaima gidan kune Uhm kawai yace akasan carpet ya zauna haba Ziyad tashi kazauna akan sofa man aah Ummee nan ma ya isa murmushi ta saki kaidai kanajin kunya tane kawai kaima da nane yadda nadauki Imti haka na dauke ka kama faranta min fiye da yadda take faranta min fuskarta ce ta maye da damuwa.
Sai hakuri Ummee abunda yace kenan Dad ne ya sakko daga sama fuskar sa ba yabo ba fallasa ya sakko ya zauna barka da yamma Alhaji yawwa sannunka meke tafe dakai dan muskutawa yayi dama anyi kirana daga can garimmu babana baida lafiya shine zanje na dubo shi,dan jim Dad yayi nanda yaushe zaka dawo sai yadda naga jikin nasa.
Ummee ce ta tari numfashin Dad ganin rashin dacewar abunda yayi ya mutum yacema mahaifinsa ba lafiya bakacemai Allah ya sauwake ba kafara tambayarsa yaushe zai dawo azuciyarta take ayyana hakan,cikin jimami take fadin Allah ya bashi lafiya kaje Ziyad babu matsala kazauna ka kula da mahaifinka har Allah ya bashi lpy to Hajiya Ngd Allah ya saka da Alkhairi Ameen Ziyad mikewa tai ina zuwa.
Dad ne ya bita da kallo yana jinjina shishshigi irin na Ummee bata jima ba tadawo hannun ta dauke da kudi mikawa Ziyad tai gashi kasai mishi magani aah kibarshi Ummee saifa ka karba aiba rokata kaiba nina baka.
Dad ne cikin jin haushin Ummee yake fadin shegen rawar kai irin naki tunda baya so ki kyaleshi mana ko ana dole,sake mikawa Ziyad tai dan Allah ka karba jin ta hadashi da Allah saiya karba godiya ya yimata bkm kayiwa me jiki sannu Allah ya tsare hanya Ameen jikinsa asanyaye ya fita.
Kaidai wllh Dady ka guji kyamar talaka yanxu wannan yaron menene laifin sa ni hakanan naji ya kwantamin azuciya wllh,seyayi ta kwanta miki kimayar dashi cikima ni babu abunda ya shafan kinga zaki iya.
Dakinsa ya shiga ya dakko yar jakar kayansa dama basufi kala ukuba ya rataya jakar taji jiki duk ta kukkuje. Wajan su shehu ya nufa mika musu hannu yayi ni zandanyi wata tafiya sai Allah ya dawo dani Lawan da Shehu sun mikomai hannu amma Hamisu makale hannun sa yayi Allah ya raka taki gona to hauka nake zammikoma hannuna bayan talauci ya mamayeka gaba da baya haka kawai ka sake shafamin karin talaucinka akan nawa aah badani ba.
Zuba masa idanu sukai cike da takaice Lawan yaja tsaki kaidai Hamisu Allah ya tsinewa jahilcinka kullum kanka kamar na tinkiya babu iklasi babu tauhidi tunda baka godewa ALLAH niimar da yayima ya ajeka anan ba zaka godewa Azabar sa. Aini nakasa magana ma inji Shehu da yayi sakare yana kallon Hamisu kallon Ziyad sukai da yayi fakare yana kallon Hamisu cike da Mamaki kayi hakuri Ziyad wannan da kake ganinsa hassada gaba daya ta gama cinye masa zuciya kuma ahaka zai kare dan kawai kafishi kyau yakema bakin ciki.
Dan murmusawa Ziyad yayi babu komai Shehu ai zaman tare ya gaji haka Allah ya kaddara saduwar mu gaba yayi yana jujjuya maganar Hamisu aransa.
Inkin karanta kidaure kiyi comment sister.
Mrs Baba Bello Abubakar
.....✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 27&28
Hakan yabawa Imti damar tuka kanta tunda ya tafi takecin karanta babu babbaka haka zata hau titi taita tsuga mugun gudu babu abunda ya dame ta kullum Ummee acikin yimata fada take amma kamar kara zugata takeyi sam ta gagara tayi hankali sai kara botsarewa takeyi tun anasa idan ganin Ziyad har aka daina akalla yakai wata daya da tafiya ba amo ba labari sosai Ummee ta shiga damuwa alasa dai ba mahaifin nasane ya rasu ba.
Yau weekend kowane ma aikaci yana gida yana hutawa da iyalin sa adai dai wannan lokaci Ziyad ya sauka akan dan acaba can baya da unguwar su Imti dan be isa ya shigo jerin manyan gida jannan da kwarababban mashin dinsa ba kudinsa ya biyashi yayo gaba yasha wata jallabiya taji jiki matuka ga wani takalmi sha kwana kaga dan uwanka.
Kwankwasa kofar get din yayi Malam manu daya leko yayi arba da Ziyad da sauri ya bude masa kofa yana washe baki Ziyad kaine ai mundauka bazaka dawo dan murmushi ya saki gani kuma na dawo to Alhmdlh munji dadi matuka ai Hajiya ma tana yawan tambayar ka haryau baka dawo ba Allah sarki abunda ya fada kenan ya kara gaba dan karamin dakinsa yasa key ya bude yayi kura sosai tsintsiya ya dauka ya share dakin tas sannan ya ajiye jakar kayansa.
Ko zama beba aka fara kiran sallar azahar mikewa yayi yayi Alwala masallacin gidan ya fada dan madaidaici anan sukeyin sallah akwai limami na musamman da Dad ya dauka shine me ja musu jam'i. Futo warsa kenan daga masallacin yana danna yar kwara babbiyar wayar sa gaba daya hankalin sa yana kan wayar da alama akwai abunda ya dauke masa hankali acikin ta.
Garam yaji sunyi karo da Mutum tunkan ya dago yasan dawa sukai karo yaji saukar wani lafiyayyan mari a fuskarsa dafe kunci su shehu sukai jin yadda marin ya dake su tamkar su aka mara dago rinannun idanun sa yayi ya zube akanta tunda Uwar sa ta haifeshi babu wanda ya taba daga hannu yayi masa wannan marin se ita.
Kallon tsana da kyama yake mata akuma daidai wannan lokaci Abba da Ommu suka shigo gidan kamar hadin baki mahaifan Ummee suka biyo bayansu a tasu motar dama sun shiryawa hakan yau zasu kawo wa yayan nasu ziyarar ba zata akan idanun su Imti ta daga hannu ta zabgawa Ziyad mari.
Cikin huci da hargowa take fadin mahaukacin inane kai da bazaka dinga kallon gabanka ba tsabar kauyanci da kida humancin da kaje kauye ka sake koyowa zaka zo haka kawai ka bangajeni kabi ta akaina ko wani sabon salon iskancin kaje ka koyo wanda bansan da shiba kanta rufe baki Abba ya dauke ta da wani shegen mari ashe baki da mutunci Aisha bansan rashin tarbiyyar taki yakai hakaba tunda kika iya daga hannu kika mari kamar Ziyad wanda agirme ya girmeki nesa ba kusa ba.
Cikin Kuka take fadin yanxu Abba akan wannan kaskantaccen kamareni wanda ko amegadin gidana bazan dauke shiba seko yabar mana gida tunda ba tare da ubansa aka gina gidan ba Ommu ce ta gwabe mata baki kedai bakiji dadin halinki ba bakiyo halina ba ni saiyanzu nakejin bacin rai da aka saka miki sunana danni ba haka nake ba nasan mutuncin dan Adam nasan girmansa bana wulakanta kowa cike da bacin rai take wannan maganar.
Abba ne ya kalli Ziyad wanda ya sunkuyar da kansa ya kasa magana hannunsa kawai ya kama suka koma Masallaci Baba ya kalla mahaifin Ummee biyoni Alhaji binsa yayi abaya su Mama cikin gida suka wuce cike da mamakin takadiranci irin na Imti.
Zama sukai amasallacin liman Abba ya kalla zaka zama waliyin wannna baban Ummee ya kalla dasu Shehu da suke zazzare idanu ku kuma kuzama shaidu, Ziyad daya daskare azaune yana kallon ikon ALLAH me Abba yake shirinyi Malam Ziyad yanzu nawa ne ajikin ka cikin sanyin jiki yasa hannu a aljihunsa dakyar ya lalubo dubu biyar ya mikawa Abba mikawa liman kudin yayi ga sadaki nan.
Atake awajan aka daura Auren Aisha Alkasim kamal da Ziyad Muhammad akan sadaki naira dubu biyar,kansa ne yayi wata masifar sarawa kallon abun yake kamar amafarki yarasa wadda za'a aura masa sai Imti yarinyar data gama tambadar da mutuncin ta jiyake kamar ya furta kalmar saki take awajannan inya so daganan yadauki jakar kayansa ya bar musu Gida.
Amma girma da kwarjinin Abba bazai barshi yayi hakan ba yana da wata irin girma da mutunci awajan sa bazai iya watsa masa kasa a ido ba be sanshi ba besan daga inda yake ba ya dauki jikarsa ya bashi ina bazai yi wannan butulcin ba. Babu wanda be girgiza ba da wannan gawur taccen al amari daya faru da tsakar rana.
Sake kama hannunsa Abba yayi har cikin parlon suka shiga tukunna ya sake shi har Lokacin Ommu ranta abace yake haka Mama Ummee kuwa ai ba'a magana kamar tatashi ta rufe Imti da duka haka takeji Dad ne ya sakko daga sama duk abunda ke faruwa bashi da masaniya gimtse fuskarsa yayi hango Ziyad azaune da wasu ko daddun kayan sa.
Shikuma wannan me yakeyi anan sirikin kane Abba ya furta babu wata damuwa a Fuskar sa,kallon rashin fahimta yake bin Abba dashi kamar yadda su Ommu Mama Ummee suka zubo masa idanu suna neman karin bayani.
Inkin karanta kidaure kiyi comment
Comment dinku shine kwarin guiwa ta 😍😍😍😍.
Mrs Baba Bello Abubakar
......✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 29 & 30
Ko wannan su zubowa Abba Idanu yayi yana jiran karin bayani.
Kwarai kuwa Abba ya Jijjiga kansa karkacewa yayi ya zaro kudi a aljihunsa ke Aisha zonan kamar bazata taso ba da kyar tadai taso taci wasu riga da wando sun masifar matseta nuna mata kusa da Ziyad yayi alamar ta zauna kamar taga kashi haka ta yatsina fuska can nesa dashi ta zauna dan batajin zata iya zaman sacan daya akusa da Ziyad.
Ungo kallon kudin tayi sunyi dauda duk sun wani ya mutse tura baki tayi mezanyi da wannan kazaman kudin karbi kedai kamar zatai Kuka haka ta karbi kudin tana toshe hanci murmushi Abba ya saki to Alhmdlh sadakin kine wannan kudin lakadan ba ajalan ba har naira dubu biyar dummmm kaf mutanan parlon zuciyoyin su suka buga atare Dad da Imti suka mike tsaye cikin tashin hankali.
Cikin rawar murya Dad ke fadin Ab Abbah ban gane abunda kake nufi ba to bari nai maka gwari gwari Aisha yarka na Aurar da ita ga Malam Ziyad saboda na yaba da hankalinsa kamar yadda take ganin sa kaskantacce kome gadi be isa tai dashiba shiyasa na nuna mata bata isa ba ita ba kowa bace face baiwa me girmankai hade da izzah da jiji dakai.
Numfasawa Abbah yayi kuma ba kowa ya nuna mata hakanba face kai shiyasa na nuna muku daga kai har ita akwai na gaba daku Aure ya riga ya dauru yanzu zai tarkata matar sa sutafi .
Ba kauye ba in kan tsaunine garinsu yaje su zauna tare ta hakanne zata san mutuncin talaka da mutuncin kanta,wata kara Imti ta fasa sai gata akasa sumammiya tashi sukai gaba daya suna kiran sunan ta banda Ziyad dako motsawa beba da zata mutu ayanzu saiyafi kowa farin ciki.
Dad ne ya fashe da Kuka kakashe ni Abba wllh bantaba zatan baka kaunata ba saiyau har na tanadi kalar mijin da nake so ta aura karasa wanda zaka aura mata sai fakiri matsiyaci meci a karkashina.
Ummee ce ta nufi Fridge ta dauko ruwa me sanyi kwarawa Imti ruwan tai wata ajiyar zuciya ta sauke kafin ta fara bude idanun ta ahankali,kantane ya tariyo mata abunda ya faru fashewa tai da wani azababban kuka Dad katemkeni willh bazan zauna dashi ba wayyo na shiga uku,dena kuka lele babu wanda ya isa ya rabani dake bazaki taba yin rayuwar wahalaba muddin ina raye babu wanda zai fitar min dake kamar yadda ya Aure ki haka yanzu zai sakeki.
Cikin fitsara da rashin kunya Imti ta mike wllh tallahi aikaima kana da yayan kodai yanzu Dad ya saki Ummee ka Aura masa ko kuma ka saki matar ka ya Aura tunda Abun sankaine ni dama na dade da sànin baka kaunata sai yau na sake tabbatar wa bukatarka ka kasheni da bakin ciki kai kuma matsiyacin talaka kodai ka sakeni ko yanzu na dauko wuka na kasheka kuma wllh na kashe banza.
Dau aka wanketa da mari cikin bacin rai Ummee ke nuna ta harni zaki ce asaka ya Aure ni ko asaki uwata ya aura inkinga Aurannan ya kare to ki tabbata Ziyad ne ya sakeki amma ke baki isa a warware wannan Auran ba.
Cikin fusata Dad ya juya ya shimfidawa Ummee mari jikinsa har rawa yake tsabar masifa da tashin hankali kinga Amina akan wannan Auran tsaf zan iya sakinki wllh inyaso dama ga iyayanki nan azaune su tattaraki su tafi dake.
Eh nagodewa Allah iyayena sunban cikakkiyar tarbiyya ba irin kaba ni bazan taba kallon idanun iyayanka na fada musu bakar magana ba saboda nasan darajar su kaida baka san darajar nawa iyayan ba kaci gaba da zaginsu cikin Kuka take wannan maganar.
Ommu ce ta mike rai bace Alkasim in kara wata magana akan Amina nono na da kasha Allah ya isa. Cak wuta ta daukewa kowa dan Ommu macece me matukar hakuri da dattako ba kowane abu ke bata mata raiba saita kai makura take nuna bacin ranta.
Afusace Dad ya juyo a bazata ya shaqi wuyan Ziyad ko motsawa beba wani ba hagon mari ya sauke masa dan ubanka sakarmin 'yata kai zagin da Dad betabayi ba ko akuruciyar sa awannan Lokacin saidaya sauke shi akan Ziyad.
Kamar zararre haka Dad ya zage yana kaiwa Ziyad duka cikin bacin rai Ommu ta dauke Dad da mari sai Lokacin ya dawo hayya cinsa Alkasim mahaukacin inane kai zaka kama sirikin ka da duka to kasa aranka wanann Auran zama daram babu saki ba yaji babu jeka kadawo ya dauru kenan matukar nina haifeka kasake fadin tak ban yafe maka ba.
Komawa tai tazauna zuciyarta na mata suya kamar anzare masa laka haka maganar Ommu ke masa kara akunne matukar ka sake cewa tak ban yafe maka ba fashewa ya sakeyi da Kuka haba Ommu yazakimin haka yazaki hanani magana akan abunda yake mallakina hakkinane na zaba mata miji nagari amma wanann bana gari bane karki manta acikin 'yayanki nine mafi soyuwa agareki.
Adaba da kakejin magana amma banda yanzu ahalin yanzu kaine da mafi bakan tuwa azuciyata tunda aka haifamaka 'ya kake cusamin bakin ciki da bacin rai to matukar nina haifeka ban amince kakara cewa komai ba.
Fashewa da kuka Imti tai kafafun Ummee ta rike dan Allah Ummee kitaimake ni bana sonsa wllh natsane shi janye kafarta tai Murmushi ta saki wanda yafi Kuka ciwo sai yau nake da amfani agareki sàida lokaci ya kure miki bazan taba jayayya da umarnin Abba ba kuma ni wannan Auran yayi mini daidai ina da tabbacin Ziyad mutumin kirki ne bazai taba cutar dake ba.
Kuka take tana birgima akan saiya sake ta Abba ne ya daka mata tsawa batasan sanda ta mike tsaye ba,kai Ziyad dago kansa yayi fuskar sa bazaka taba gane awane hali zuciyar sa take ba.
Malam Ziyad awane gari iyayanka suke Azare ya amsa ahankali to Alhmdulillahi zamu dinga waya Lokaci zuwa Lokaci karka taba kawota gidannan saika tabbatar ka sake mata sabuwar tarbiyya tatashi daga sangartacciya takoma tauraruwa agidan mijinta lokacinne zaka kawo mana ita.Gyada kai kawai Ziyad yayi Zuciyarsa na daci da kuna shiya kamata yayi Kuka ba itaba shida aka bawa ragowa.
Tashi kajata kutafi Allah ya tsare hanya duk inda zakuje ma kutafi Allah ya bada zaman lpy.
Ahankali Ummee tataso kama hannun Imti tai da awannan lokaci ta zama kamar tababbiya har gaban Ziyad ta jata hannun sa ta kamo ta hada dana Imti murmushi ta sakar masa nasan ka Ziyad kaidin mutum ne me rukon amana toga amanar yata nan nabaka inaso ka kulamin da ita dan Allah gyada kansa kawai yayi juyawa tai ta haura sama hijaban data dinka mata kwanaki taki sawa kaf ta kwaso su da kayanta masu dan mutunci saidata cika mata wata akwati.
Sakko watai da hijab guda daya a hannunta sakawa Imti tai da har wannan lokacin bata dawo hayyacinta ba.akwatin ta mika masa Allah ya kiyaye hanya karba yayi tare dajan hannun Imti data rasa tunanin ta binsa kawai take abaya kamar sha sha sha,tasowa sukai gaba dayan su harda Dad wanda yakejin duniya tana juya masa ko waiwayowa Ziyad beba harsuka fice tsugunnawa Dad yayi akan guiwowinsa fashewa ya sakeyi da Kuka kafin ya zube kasa ba numfashi.
Lawan Kuka mashi kushigar dashi parlo cikin sanyin jiki suka kinkimi dad wanda yayi dogon suma.
Janta kawai yake suna tafiya gaba daya zuciyar sa tadauki zafi idanunsa sunyi jazir jikinsa har rawa yakeyi saboda fushi,yanayin unguwar da babu ruwan wani da wani har suka fice babu wanda ya gansu tafiya sukai me nisan gaske tuni fuskar Imti tai jajawur bata saba da wahala ba, napep ya tare musu sunan wata tasha ya fada masa fusgota yayi tatafi luuu kamar babu rai ajikin ta jikinsa ta fada gaba dayanta.
Bacin ransa sake lunkuwa yayi jiyayi kamar garwashin wuta ta manna masa hankadata yayi ta sake tafiya luu kanta ya daki napep din amma ina bata masan abunda ke faruwa ba suna zuwa tashar ya kara jawo ta kamar kayan wanki wannan karan ai bazata iya tsayawa akan kafafunta ba babu yadda ya iya haka ya sabata akafada gaba daya motocin sun tashi sai wata akori kura guda daya da take shirin tashi.
Azare ya furta kamar me ciwon baki dan jim me motar yayi zaku iya zaman sama dan nann gaba akwai wadanda zan dauka gyada kansa yayi alamar eh wullata yayi kamar ya samu boll kamar kafin ya dora akwatinta akai shima yahau aka dauki hanya tafiya ce ta yada kanin wani duk inda suka zo wucewa sai ambisu da kallo yuuu idanun Jama'a ke binsu.
Wahalace ta farko da ita ga azabar rana ga yunwa ga Zazzabin daya rufe ta wahala goma da ishirin ce ta hade mata dakyar ta bude idanunta da sukai matukar yimata nauyi ruwa ruwa abunda take kira kenan yana jinta yayi mata banza kamar besan da zamanta awajan ba.
Tun tana ruwa har tagaji tai shiru sai magari ba suka fara shigowa zariya tsayawa akai direba yace sallah zaiyi shima Ziyad sauka yayi yabarta amotar sai idanu da take zarewa kamar mazarin tsire.
Fiyo wata ya wullo mata sai wani busashshen rogo daya gama shan wuyar duniya ya watsa mata daga haka be kara bi takanta ba,dakyar tabdaddafa ta ta zauna wata hajijiya take gani ga iska data addabi rayuwar ta tuni hancinta ya tattoshe ruwan tasha da kyar ya zauna acikin ta wani amai ne yake tuko mata.
Rogon ko kallo be ishe taba tunanin ta ina zai kaita koma inane zai dawo da ita da kansa.
Fans kufito kuraka Amarya dakin Mijinta daganan har Azare kar abarku a baya.🤣🤣🤣
Comment dinku na karamin karfin guiwa fans.
Mrs Baba Bello Abubakar.
........✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 31 & 32
Cikinta ba karamar kullewa yayi ba Kuka ta fashe dashi tsabar bala'in yunwa kukan ma baya fita sosai batasan sanda ta juya ta rarumo rogon da tunda uwarta ta haifeta bata taba cinsa ba sai wannan lokaci tanaci tana Kuka kamar ansata dole,tana gamaci cikinta ya kulle kwamciya tai rike da ciki tana gursheken kuka amai ta fara kyalayawa saidata amaryar da rogon da taci tas sannan ta samu salama gefe ta kona ta rube.
Duk Abinda takeyi yana kallon ta wani murmushi ya saki dana kasa gane ma'anarsa saishi wanda yayi shi yasan ma'anar kayansa basu suka shiga azare ba sai 11 na dare atasha aka ajiye su Zazzabi sosai ya sake rufe Imti sai rawar sanyi takeyi hakoranta sai haduwa suke da junan su.
Tashar tsit take babu kowa sai haushin kar nuka da yake tashi gabas da yamma ya kalla bega wani mashin da zasu hau ba tsaki yaja akwalar wayar sa ya dakko ya danna wata number shazali kazo tasha ka dauke ni kit ya kashe wayar dan jigina yayi da rumfar me shayi tana tsugunne ta kasa tsayawa akan ka fafuwan ta.
30mint shazali ya karaso da wata kwarababbiyar napep taji jiki matuka,kallon Ziyad yake da mamaki meya dawo dakai Ziyad naga yau dinnan ka koma kala bece masa ba akwatin ya fara zurawa kafin ya tsaya akan Imti datakeji duniya na juya mata hawaye wani na korar wani inkin ga dama kitashi.
Sai lokacin shazali ya lura da ita bakinsa cike da magana akan wacece amma babu hali yasan halin Ziyad sarai baya son tambaya da kyar ta mike a dudduke take tafiya harta shige napep din abarda ko amafarki bata taba zatan zata hauta ba ina wllh da sake dole ne ma ya sake ta yamaida ita hannun iyayanta.
Sunyi tafiyar 30mnt kafin su karaso wani kauye babban kauye ne babu mutane sosai awaje yawanci kowa ya rufe gidan sa sai tsirarun mutane ke kaika wo a hanya. Kofar wani gida suka tsaya almajiraine birjik a kwakwkwance wasu kuma suna zaune suna sake tisa karatun su.
Fita yayi ya dauki akwatin fito Malama fitowa tai kamar sokuwa haka take kallon almajiran da suka jere reras a kwance gidan da suke kwance akofar sa nan suka shiga babban gidane sashi sashi Irin dai ginin kauyannan da yake lokacin zafine wasu na kwakwkwance atsakar gida yarane rakwacam kanana da manya.
Kofar wani daki ya tsaya cikin sanyin murya yayi sallama daga dakin aka amsa wa nakeji kamar Ziyadulle wata dattijuwar ta furta yaye labulan dakin tayi har zata sake magana idanun ta ya sauka akan Imti dake rawar sanyi har wannan lokacin. Da bakuwa kuke tafe gyada mata kai yayi alamar eh to shigo mana.
Kamar zata shiga kurkuku haka taji wani shegen warin daddawa ne ya daki hancin ta da wowa tai da sauri ta sake cakewa akofar dakin kallonta yayi kamar ya waska mata mari uwarme ya fito dake cikin tsiwa da rashin kunya ta furta uwarka ce tasa ni fitowa dau ya dauke ta da wani bahagon mari da sauri ya kumbo ta sake lekowa cikin mamaki take kallon su.
Haba Ziyadulle meyayi zafi zaka dake ta haka bana son saurin duka kaji na gayama ka kwafa yayi bakisan fitsarar wannan yarinyar bane ya kumbo bata da Mutuncin ko kadan,ai hakuri akeyi taho kinji haka tabi bayan ya kumbo sosai marin ya shigeta.
Wani mugun zafine adakin ga sauro sai shegen kuka yakeyi gado ya kumbo ta Nuna mata ga gado nan hau ki kwanta dakyar tahau gadon sai kiki kiki yake kamar zai karye jitai kamar ta kwanta akan katako tsabar taurin gadon wasu zafafan hawaye ne suka sake zubowa daga idanu wanta tunawa da nata dakin katafare babu abunda babu aciki babu zafi ba sauro amma kalleta awannan dakin dako karan gidan su baza a saka ba.
Tunawa da batai sallah ba yasata mikewa bayan Ziyad ya fita kallon ta ya Kumbo tai ina zaki ko zaki zagaya ne, girgiza mata kai tayi Alwala zanyi to ya kumbo ta amsa fita tai ta dauko buta ta zuba mata ruwa,ahankali ta futo daga dakin anan tsakar gida tai Alwala ta koma daki kabbara sallah tai tana idarwa ta mike kamar zata kifa tsabar yunwa ga zazzabi.
Kusan kwana tai tana Kuka tun ya kumbo na bata baki harta gaji ta kyaleta yadda Imti taga rana haka taga dare,sallar asuba ba saba tashi taiba tanaji ana sallah taki tashi ita kuma yakumbo ta dauka ko bata sallah ne shiyasa bata tashe ta ba. Har karfe 7 tana kwance tana aikin Kuka idanunta sun kumbura sunyi suntum sai azababban ciwo da kanta keyi tajawa Abbah Allah ya isa yafi sau shurin masaki.
Da kyar ta sakko daga kan gadon ta nufi kofa kanta ko dan kwali babu dama bata saba dashi ba yarane birjik jage jage dasu ba wanka ba wanki se matan gidan kowacce da daurin kirji sai kicicin dama kunu akeyi awata katuwar tukunya wannan tukunyar kuma dumaman tuwone gandara gandara kamar kajefi kato dashi.
Duuuu taga matan gidan har yayan gidan suka tsaya da abunda sukeyi suka zura mata idanu tundaga sama har kasa suke kallon shigarta a tsorace take kallon su bata taba kallon mutane masu kamannin su ba ita dai ba ganin yan kauye take ba balle ta shaida ya kamannin su yake kowannen su yayi busu busu kamar wadanda suka shekara basi wanka ba kanta gama wannan tunanin ashe har anzagaye ta kai hatta samarin gidan kallonta suke kamar sunga namun daji.
Fashewa kawai tai da kuka dan tarasa abunyi akalla mutanan da suka zagayeta sunkai mutum hamsin harda alamajiran waje duk wanda yashigo yaga abunda yake faruwa saiyaja ya cake shima fitowarsa kenan daga daki ya hango dandazon mutane ancika makil sosai abun ya bashi mamaki kome suke kallo oho kutsa kansa yayi hangota yayi atsaye ta rufe fuskarta tsoron kallon suma take yi.
Maida kallonsa yayi kan matan gidan abun takaici hadda wadanda tsabar kallo suka saki baki ido da hanci ko ina kallon yakeyi,cikin kakkausar murya ya furta kai kowa ya watse da sauri suka dinga dare wa suna tafiya suna wai waye kamar zasu kifa abinda ya basu mamaki irin mutanan da suke gani a TV yau ita suka gani agaske shiyasa suka susu ce.
Wani banzan kallo ya watsa mata wuce ke kuma kiba mutane waje kazama kawai ware idanunta tayi akansa wani bacin rai na taso mata,matsowa tai har kusa da shi tana binsa da wani wulakantaccen kallo ni dakai za'a ga wanene kazami kuma kaji nafada maka dole kamai dani inda ka dakko ni bazan iya zama acikin tsiya da talauci ba ko yini daya bazan karayi a wannan banzan village din ba.
Murmushi ya saki na tura haushi to ai wannan Village din ashi zaki rayu kiyi yaya da jikoki harda tattaba kunne ammafa ba dani ba bayan na sakeki zan samu daidai dake dazan jona masa ke Yayi maneji ni nawuce da ajikin ki. Mace me mutunci zan nema wadda ta san mutuncinta ta yadda cewa ita macece wanda aka sani da kame kanta da kunya.
Ammake babu wata nagarta da zaa gani atare dake duk kin gama watsar da kanki a titi wannan ya yaga ya barwa wannan a hakan kike tunani ke aka cuta,uhm to ni aka cuta da aka likamin ke kamar yadda nake saurayi budurwa zan nema me kunya da kamun kai ba ballagaza irin ki ba. Wani tukuki ne ke yawo azuciyar Imti ita wai itance kuwa drebanta yatsaya agabanta yake gaya mata magana son ransa aiko kura ta karye tafi karfin langa da kare.
Mrs Baba Bello Abubakar
......✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 33&34
Harta mika hannu zata damki wuyansa yakumbo ta fito daga bandaki hannunta rike da buta take kallon su, lafiya kuwa naganku atsaye kamar zakaru,kansa yadan shafa ciwon tane ya tashi cikin rashin fahimta Imti take kallon sa haka ita ma yakumbo ta kemai kallon karin bayani,wani munafukin murmushi ya saki gyada kai yayi eh ya kumbo tanada tabin hakaline shine dalilin dayasa mahaifinta ya bani ita mutaho tare saboda Malam ya dinga yi mata rubutu tana sha sannan adinga koya mata karatu bakomai akanta.
Allah sarki cike da tausayawa ya kumbo ke kallon ta sannu yarnan Allah ya baki Lafiya kuma Ziyadulle sedaka fada na gasgata duba da yadda naga kayan jikinta kalli kanta fa kala daban daban zako adage ai hauka mugun ciwo ne.
Kamar idanun Imti zasu fado haka take kallon su zuciyarta kamar zata fashe wai ita ce mahaukaciya kamar ita ya lakaba mata ciwon hauka wata kwallar bakin ciki ce ta cika mata idanu kama hannunta ya kumbo tai jekiyi wanka 'yarnan kyaji dadin jikinki naga sai uban maiko kikeyi kamar kin shafa man kuli.
Kamar ta danna musu zagi dagashi har ya kumbo sekawai tai shiru buta tazara tai hanyar toilet jatai ta tsaya ganin wani mugun bandaki masan ma ta rufta seda dabara ake hawanta kasan bandakin babu siminti ko kadan ya jagule zarnin fitsari da warin kashi sai tashi yake ga wani mugun fitsari daya matsi Imti ga mutane atsakar gidan balle ta saki abunta awajan fashewa tai da Kuka tana yarfe hannu ita kam tashiga uku yarda butar hannun ta tai ta fada dakin ya kumbo akwatinta ta kinkimo tai waje hanyar kofa take nema dan tarantse bazata sake kwana a wannan shegen garin ba.
Kallon ya kumbo yayi wadda tai sakare tana kallon Imti wani Murmushi ya saki kingani ko ya kumbo yanzu haka ciwon tane ya tashi matukar ba'a dauki wani mataki ba guduwa zatai kota fara duka,dafe kirji ya kumbo tai au har duka takeyi kwarai kuwa yadda kikasan talauci haka take da karfi in aljanun kanta suka motsa,aiko ya zama dole adinga killaceta adaki muda mike da kananan yara inta kassara wani fa.
Kukan bakin ciki da takaici Imti ta fashe dashi kafin ta durkusa akan guiwowinta,me Ziyad yake nufi da ita inane nan ya kawo ta me ake yunkurin aikata mata batasan amsar ba bata da zabin daya wuce ta sake fashewa da kuka saita rama dukkan wani abu da Ziyad ya aikata mata.
Matan gidan tsayawa sukai da ayyukan su wata matace baka kirin da jajayan idanunta bakinnan inaga tunda ta duro Duniya be taba samun brush ba cikin tafa hannu take fadin na hige su ni Hinde ashe bata da cikakken hankali shiyasa kalli kanta kamar tozon rakumi bari a sanar da malam gwara tun yanzu asan nayi dan aradu ban shirya cin duka ba hanyar soro tai bagazan bagazan.
Imti wadda ta daskare atsaye tanajin irin cin mutunci da tozarcin da Ziyad yake yimata jatai ta tsaya cak jitai wani dattijo yana ashsha aida ganin ta gagarumanne akanta ke bintalo kutaru kudakkota akaita dakin rukiyya.
Ram suka rike Imti sai Kuka take tana kokarin fizgewa amma ina abunka da wadanda sukaci tuwo jikinsu dumurmur haka yake daukar Amarya sukai wa Imti daga me warin hammata seme warin baki aciki za'a iya samun wadda tai sati biyu batai wanka ba basu direta ako ina ba sai awani daki babban dakine alluna ne birjik ga buzu irin na fata se mari da wasu manyan sarko ki.
Yauwa Hinde ku ajeta anan kan wani buzu aka daurata kusake dannemin ita ko kwakwkwarar motsi Imti kasawa tai wani shegen mari Malam ya dakko akasawa Imti duka kafa biyun saida suka tabbatar ansa kwado ankulle marin suka saketa suna maida numfashi oh ni dije mun tsallake rijiya da baya ni wllh saiyanzu hankalina ya kwanta da aka daure ta yo ina dalili mahaukaciya tazo ta hauka da duka.
Tsabar bakin ciki Imti ta kasa kuka gaba daya idanunta ya soye da tashin hankali ga fitsari ga yunwar data addabi rayuwarta,yawwa Malam Mamuda kushigo daga ciki wasu garadane suka dinga layin shigowa sàida kusan mutum 20 suka shigo kowannen su dauke da Alkur'ani a hannun sa zagaye Imti sukai aka sata a tsakiya nan aka fara karatu baji ba gani amma Imti ko motsawa bataiba in banda binsu da kallo da take.
Karatun 30mnt akai babu wani labari kai sunusi fita kadebomin rushi dagani masu taurin kaine aiko zakuci ubanku. Da hanzari wanda aka kira sunusi ya fita garwashi ya debo niki niki a wani katon kasko agaban Imti aka ajiye dandanan wani mugun zafi ya ziyar ceta wani turare Malam ya dakko aka antayashi a rushi dinnan hayaki gaba daya turnike dakin yayi gaba daya Imti gigicewa tai da wannan hayakin wane irin mummunan bala'ine ya sameta haka.
Kowa tari yake amma haka Malam yadinga zuga turaran nan fitsarin daya matsi Imti tuni ta dade da sakin kayan ta cigaba akai da karatu nan ma ba bayani afusace malam ya dakko wata shimfidediyar dorina me baki biyu ya shimfida wa Imti agadon baya wata kara tasaki tatafi sharaf sumammiya tunda Allah ya halicce ta bata tabajin radadi irin wannan bulalar ba.
Sharce gumi Malam yayi yana kiran Alhmdlh shedanun kanta sunfita🤣🤣🤣 gaba daya garadan Alhmdlh suke kira anaiwa Malam kirari sai hura hanci yake shibe yadda ba babban Malam,tundaga dakin sa saidayaji ihun Imti wani shegen Murmushi ya saki yanzu ma akafara wasan haka ya ayyana acikin zuciyar.
Ke ya kumbo zo kudauki wannan yarinyar kusan su shida suka shigo dakin kwance mata marin kafarta Malam yayi yawwa kudauke ta da zarar ta farka asake yi mata wannan.hayakin wani garin magani ya mikawa ya kumbo to angode Malam Allah yasa kafi haka Ameen Ameen ya fada yana jan wata zungureriyar cazbahar sa,sake daukarta sukai suka ajeta agadon ya kumbo fita sukai ko wacce ta kama aikin gaban ta.
A hankali ya lumshe idanun sa dan danan fuskarsa tai jajawur lallai ba shakka akwai wani abu daya tuna wanda yayi masifar bata masa rai hakoransa har haduwa suke sabida azabar fushi barbaza gashin kansa ya hauyi hannun sa agoye yake zagaye dakin kome ya tuna oho.
Tofa kaka kakara kaka meyake shirin faruwa da Imti wane irin tanadi Ziyad yayiwa Imti daukar fansa yakeyi ko ramuwar gayya atakaice ma wai wanene Ziyad kuci gaba da bibiyar labarina danjin yadda zata kaya.
Ina masoyan Imti shin tafara baku tausayi ko har yanzu da sauranta fans din Ziyad anya ya aikata dai dai kuwa ina jiran amsoshin ku.
Mrs Baba Bello Abubakar
Matar dan Aljannah.
💞💞💞💞💞
........✍️✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 35&36
Babu wanda ya san suma tai dan kanta ta farfado tana farkawa ta fashe da kukan bakin ciki da takaici tatsine wa Ziyad yafi cikin tirela ya kumbo ce ta shigo oh sannu yarnan Allah ya saka miki ai mutanan boye basa kyautawa haka kawaii sun shiga sunyi kane kane ajikin ki jibi dan Allah har canza miki kamannin gashi sukai sunmai daki kamar wata aljana.
Imti na jinta tsabar takaicine yasa tai mata banza tashi kije kiyi wankan magani gashican na dafa miki,kan Uba ta ayyana aranta wankan magani tirkashi da kyar ta mike tana fita yara da manya aka fara hannu ba kuwa hannu wani takaicine ya sake turni ke ta ko kallon su batai ba ta shige toilet a daddafe tana dafa bango santsi ne ya kwasheta wata katantanwa tai saiga kafarta daya acikin shadda.
Ihu ta runtuma aguje matan Gidan suka taho suna tambayarta ko Lafiya suna shigowa suka hangota tsamo tsamo acikin tutu dama shaddar ta cika da dabara ake hawan ta,ya Kumbo ce ta dafe kirji mun shigesu ni Larai mezan gani kutemaka aciro ta kama kama akai da kyar aka zaro Imti da tai caba caba acikin tutu toshe hanci sukai saboda azabar warin daya ziyarci hancinsu a toilet din suka ajeta akasa kazanta kan kazanta kuka take tana kallon jikinta.
Ita kanta amaine yake tuko mata fita sukai gaba dayan su sai ya kumbo datai saura a bandakin tashi ki cire kayan wannan kaya ai sedai akaisu bola wazai wanke mikewa tai ta fara kici kicin cire riga kallon ya kumbo tai datai kikam a bandakin metake nufi to agabanta zata cire kayan,yi sauri mana tanaji tana gani sàidata cire kayan gaba daya ta mikawa ya kumbo aleda ta zuba su tabawa yara sukai bola.
Wani katon baho ta dauko ruwa ta kandamo arijiya sàidata kusa cikata ta kinkima takaiwa Imti dake tsaye cikin rawar sanyi kanta sai sarawa yake ga hayakin da tasha adazu idanun ta sai zugi yake sun hadu sunyi jajawur soda ta dakko mata da wani sosan buhu yaci duniya. Maza ungo ki wanke jikinki tas kidena tashin wannan warin bin kwandon tai da kallo yadda kasan ya shekara dubu tsabar yadda ya tsufa har ya fara ragargajewa amma ahaka ake yin wanka dashi.
Ganin tsayuwar bazatai mata ba sodar ta dakko a mulmule take kamar ta taba kashi haka take taba sodar da hannu ta dinga wanke kafafun ta sedata tabbatar warin ya fita ta dauki ruwan ta sheshsheka bazata iya wanka da wannan sosan ba tsaf zai yayyage mata fata,zanin da ya kumbo ta ajiye mata a kyaure ta dauka ya kode sosai duk da awanke yake amma daga ganin sa kasan yasha jiki.
Adarare ta futo tana daddafa bango gudun karta kara shan kasa,ido biyu sukai da Ziyad wata bakar leda ce a hannun sa yana kokarin shiga dakin ya kumbo kamar idanunta zasu fado haka take hararar sa kamar ta shakeshi dan takaici da bakin ciki gira ya dage mata alamar yadai na wuce da tunanin ki.
Karasa shigewa dakin yayi tsaki taja me kara buta ta dauka tai Alwala kusan karfe 10 sai lokacin zatai sallar asuba sake fitowa taga yayi ko kallontà beba ya fice daga gidan,tana idar da alwalar ta fada dakin ya kumbo kayanta data hango agadon ya kumbo ta tsaya kallo hijaban da Ummee ta dinka mata tagani guda biyu sai pants dinta da bra bayan su bata ga komai ba sai wasu kaya aleda.
Wuwurga idanun ta take adakin ina zataga akwatinta amma me ba ita ba labarin ta duddubawa tahau yi ya kumbo ce tashigo kallonta tai me kike nema kamar zatai kuka saidata dau Lokaci har ya kumbo ta fiddaran zatai magana akwatita nake nema kallonta ya kumbo tai ai Ziyad ya fita da ita ga kayan kinan acikin leda.
Kallon rashin fahimta take mata wai ya fitar mata da kaya yakai su ina to wajan ledar ta karasa ta zazzage ta waro idanu tai tana kallon kayan wasu atamfofine guda Uku leda irin na yan kauyannan kaya yau wasu burma burman rigu nane asa kamarta su uku aciki sai zani da dan kwali kamar idanunta zasu fado take kallon kayan zubewa tai akasa tare da sakin wani marayan kuka Ziyad ya cuceta.
Kayanne bakya so kike wannan kukan ko kallo ya kumbo bata isheta ba cigaba tai da kuka kamar Allah ya aiko ta saidatai me isarta ko cikanki ya kumbo bata kara ce mata ba kunu ta dire mata sai dumaman tuwo wani gandarere da koriyar miya babu alamar mai ba kayan miya ga abun karin kinan karewa Abincin kallo tai babu ta yadda za'ai taci wannan abun acikin ta.
Hijab dinta kawai ta zura ta kabbara sallah haka tai tazaune ga yunwa da takeji ga bazata iya cin wannan Abincin ba. Wasa wasa saida Imti tai sati daya bata sake ganin ko inuwar Ziyad ba tunda ya zubar da ita be kara bi takan ta ba tun bata iya cin tuwo harta dan fara cakula haka yayan gidan basu daina zagayeta inta fito ba saboda kyanta da suke gani.
Tuni Imti ta fara ramewa sai idanu awaje yau akalla takai sati biyu ba Ziyad ba labarin sa tana zaune akofar dakin ya kumbo gaba daya duniya tai mata zafi ko kofar Gida bata taba zuwa ba balle tace zata gudu wata yarinya ce dake kan fo ta fara fadin Hinde ke Hinde na gama,Hinde dake daki fitowa tai dan kwalinta a hannu keko Indo bakiji dadin halinki ba yanzu yarinya na cewa tagama bazaki tashi ki wanke mata ba.
Wani banzan kallo Imti ta watsa mata wai Indo ko wane dan iskanne yace musu sunan ta indo ni kikewa wannan kallon tsaki taja tatashi tabar mata wajan gaba daya dakin ya kumbo ta koma tana bakin gado tana kulla kuka da su barko no.
Kedawa nake jinki awaje Aisha kallon ya kumbo kawai tai batare da tace komai ba zatai magana kenan ya doka sallama akofar dakin ya kumbo,fadada fara'arta tai a'ah Ziyadulle yau kaine tafe shafa kansa yayi eh ya kumbo zama yayi akan tabar mar daya gani shimfide adakin.
An wuni lpiya Lafiya lau Ziyad ya kasuwar Alhmdlh Allah ya bada sa'a Ameen,kallon Imti tai ke baki iya gaisuwa ba harara ta watsa masa batare da tace komai ba ta kawar da kanta murmushi ya saki kyaleta ya kumbo kinsan duk wanda ya warke daga ciwan hauka sai ammasa uzuri gyada kai ya kumbo tai gaskiyar ka Ziyadulle.
Wani katon Allo yashigo dashi yawwa dama nace ga allonta nan sai adinga rubuta mata tundaga alu ambaki har Allah yasa ta fara gane karatu washe hakora ya kumbo tai aiko ka kyauta dama kullum yaran Gidannan zakaga suntafi makaranta banda ita ai zaman ba dadi haka kaga itama taje adinga karatun da ita.
Wani shegen murmushi ya saki yana kallon Imti datai mutuwar zaune duk wani tuninta ya tsaya cak kamar wawuya haka take kallonsa idanunta yayi bala'in ja tsabar bacin ran da yake sakko mata wata kwalla ce me zafi tataru acikin idanun ta.
Fans yanzu ma aka fara kuci gaba da comment naci gaba da suburbudo muku zazzafan labari.
Taku harkullum Mrs Baba Bello Abubakar.
😍😍😍Inayinku irin sosai sosai dinnan.
Masu korafin a dinga yi musu posting sau biyu a rana bukatar ku zata karbu ayau da daddare zan sake yimusu posting yanayin comment dinku da sharhin ku akan abunda Kuka karanta in bakui ba ba maganar sakin wani da daddare 😌😌😌😌
.......✍️✍️✍️✍️✍️
💕💕IMTINAN💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 37&38
Ya Kumbo ce ta kara washe baki kaidai Allah yayi maka albarka kaga yau sena bawa Yahuza yayi mata rubutu gobe da safe sesu tafi dasu Kulu ai kaga hakan yayi,gyada kai yayi kwarai nima zaman na duba ba aikin fari balle na baki gwara ta fita neman ilimi, ya kumbo da batasan dawan garin ba sai gyada kai take Allah sarki kuma se yaushe zaka mayar da ita wajan iyayanta tunda jikin nata Alhmdlh taji sauki sosai.
Girgiza kai yayi ba yanzu ba munyi waya da babanta adazun yace abarta sai antabbatar shedanun dake kanta sunfita akallah tai wata biyar ko shekara,to to Allah sarki gaskiya ya yadda dakai sosai ziyadu gashi harya baka yarsa kataho da ita hakane ya kumbo.
Sanin halin ya kumbo da shegen surutu mikewa yayi ni zan koma dama abunda ya kawo ni kenan caraf Imti ta mike in har kaga kafita daga Gidannan kafata kafarka bazan taba bari katafi kabarni awannan Gidan da bashi da maraba da prison wllh saika maidani gidammu mugu azzalumi sai Allah ya sakamin.
Ke mezan gani ni jikar tabawa rashin kunya zakiyi masa daga yana nema miki Lafiya aiko tunda Ubanki ne yace abarki babu inda zakije kina Gidannan,kallon ya kumbo tai kamar ta shake mata wuya dan haushi kalleni babu inda zakije yi tafiyarka kokarin binsa take ya kumbo ta riketa ram duk da shekarunta amma shegen karfine da ita kuka Imti keyi tana kokarin fisgewa amma ina babu hali tsatstsauran riko tai mata kamar wadda tai sata.
Zubewa tai adakin tana kuka me taba Zuciya sosai takejin kiyayyar Ziyad a zuciyarta seta wulakantashi ta daidaitashi badai ita yayiwa wannan abunba saiya gwammace kida da karatu. Tabe baki ya kumbo tai saikije kitayi ai kai ni wannan yarinya daga gani iyayanki sun shagwaba ki ga shegiyar fitsara da rashin kunya ke zaki ta wahala abanza matan gidannan ma sun isheki.
Tadade akwance tana aikin kuka kan bcci ya dauketa tundaga wannan rana Imti ta fara zuwa Makarantar Allo bata da aiki sai kuka in taje makaranta saidai Malam ya jibgeta kamar jaka amma bazatai karatu ba gashegiyar gaddama da taurin kai tun bata gane abunda ake rubuta mata harta fara ganewa.
Kayan da Ziyad ya dinko mata dan dole ta fara sawa sune dibar ruwa yo itace ita da yammatan gidan da duk babu sa aninta sai kannan ta wahala dai Imti ta wahaltu tsawon wata 6 kenan babu Ziyad babu labarin sa in aka dora katuwar tukunya acikata da uban tuwo haka matan gidan zasu ce tafuto ai tukin tuwo da ita tun bata iya ba harta saba tadan fara iyawa.
Sau uku tana yun kurin guduwa Allah be bata saa ba da zarar ankamota Malam zai sata amari setayi kusan sati adaure kamar akuya kafin da kyar ya kumbo zatayo belinta tayi baki ta rame idanu yayi zuru zuru kamar mazarin tsire gashinta ya danqare to baya samun gyara temakon da Allah yayi mata hijaban nan guda biyu su ta samu take dan sawa kamar yadda Imti ta tsani rayuwar talauci sai gata acikin ta tsamo tsamo.
In wankinta ya taru haka zatasa omo ta wanke tun hannun ta na fashewa harya daina inda me wankin kayan fitsarin 'yayanta haka zasu tulowa Imti dolanta ta wanke tun tana Kuka harta gaji ta daina tsinuwa kuwa ai ba'a maganarta ta tsinewa Ziyad yafi sau shurin masaki.
Karfa ku dauka Imti ta fara Nadama kokadan babu hakan acikin zuciyar ta kiyayyar talaka tana nan aranta ta tsani talaka kai ahalin yanzu tsanar da tai musu ada ta yanzu ta ninkata.
Bangaran Ziyad yana sane yayi biris da ita saita dan dana kudarta kamar yadda ta sha wulakanta duk wanda taga dama itama saita dandana radadin da akeji da rayuwar wahala sai sunzamo jinin jikinta,betabajin tausayinta daidai da rana daya ba tunda itama bata taba tausayawa wani mahaluki ba hatta da mahaifiyarta bata kyale ba taya zai bar Imti ta shashi salula asanadinta yaci mugun dukan da tunda yazo duniya ba'ataba yimai ba ta wulakanta shi ta daga hannu ta mareshi aduk sanda ya tuna haka Zuciyarsa daci take tsanarta sake nin kuwa take azuciyar sa.
Saiya sauke girman kanta da jijidakai Izzah da Alfahari zai tabbatar mata da ita bag kowa bace darajar Ummee kawai taci da Abba inya batar da ita kaf garinnan babu me iya gano ta.
Yau tunda ta tashi da safe kanta yake azabar ciwo jikin ta cizon sauro ne rudu rudu tana kwance agadon ya kumbo warin daddawa da take gudu tuni ta saba dashi dan daddawa akusa da kanta take kwana kullum,wata yarinya ce ta shigo hannun ta rike da wani mugun cup tayi dagaje dagaje da ita shi kansa cup din yadda kasan wanka akeyi dashi.
Wai ga hi inji dije tace kalacin kine na kawo miki bude idanun ta tai tana karewa kunun da yarinyar kallo cikin karfin hali ta kalleta jeki shanye washe hakora yarinyar tayi gaba takaita dama bata koshiba duk da yadda cikinta yai tulele kamar me haihuwa ficewa tai ranta fes binta da kallo Imti tai cikin tafasar Zuciya in har ta lissafa daidai yau watanta shida cif awannan bakin gidan bazata taba mantawa da wahalar da take sha acikin sa ba.
Bari mu waiwayi Gidan Ummee.
Tun sanda Dad ya zube akasa aka kwashe shi aka maidashi parlo ruwa aka yayyafa masa amma shiru ba labari dole aka dauke shi sai asibiti da kyar aka samu numfashin sa ya dawo jininsa Yayi mugun hawa,baccin away daya yayi yafarka kansa na azabar ciwon kuka ya fashe dashi kamar karamin yaro haka yake sharbar kuka bubu wanda yace ci kanka dan kansa yagaji yayi shiru.
Saida Dad ya shafe sati daya kafin jikinsa yayi dama dama gaba daya ya rame ya kajan me abun tausayi tun Ummee bata kulashi hatta dawo tana rarrashin sa tasan tabbas dole ya girgirza da hukuncin Abba to ya zeyi sai hakuri. Tana tunanin yarta tana tunanin awane hali take daurewa kawai take sauda yawa takan shiga daki tai Kukan ta share shiyasa Dad yake mugun jin haushin ta yace da ita aka hada baki aka bada yarsa sadaka.
Saidai tai shiru tana Kallon sa bashi da aiki sai kuka saidai ya dauko hotunan Imti yasa agaba yana gursheken kuka,kai hatta office daina zuwa yayi saida Abba yamai jan ido tukunna ya koma harkokin sa damuwa na sakecin zuciyar sa.
Ance xancan duniya baya buya anrasa wa yafitar da maganar Auran Imti da Ziyad nan fa kasuwar gulma ta bude masu murna nayi sun rabu da alakakai yanxu zasiyi yadda suke so me hana ruwa gudu tatafi. Su Lubnah sanda labarin yaje musu gaba daya kasa yarda sukai dan sun san abunda bazai taba faruwa bane ace Imti ta Auri dreban ta harma sun tafi can garin su.
Takanas suka wanki kafa suka tafi gidan Ummee anan ta tabbatar Musu anwa Imti Aure tana can tare da mijin ta shiru sukai suna kallon kallon zuciyar su dauke da damuwa amma banda Fauza farin ciki ne ya cika mata Zuciya ashe ita datake yar talakawan ma zatafi Imti hutawa dan tayi alkwarin saita samu miji na nunawa saa me kudine gaske zata aura.
Amma afuskarta bazaka taba gane hakan ba haka suka taso jiki asanyaye kowa hanyar gidan su ya nufa Fauza tana tafe tana sakin murmushi ta tabbatar ita ma yanzu zatai Babban kamu dama Imti ce tai bake bake matukar suka fita tare to bame kallon ta saidai aita kallon Imti akalla tayo samari biyu ko uku kafin su baro Inda sukaje.
Ashe abun yana bakantawa Fauza rai tanajin daci da radadin hakan duk wata kauna da take nunawa Imti ta karyace da yaudara kamar yadda Fidy tasha nusar da Imti Fauza fa ba kaunarta take ba da zata shiga cikin bala'i tafi kowa maraba da hakan,ashe maganar Fidy gaskiya ce dama ance makashinka yana tare dakai.
Tun sanda suna yara haduwar farko Fauza taji hassadar Imti ta mamaye Zuciyarta ganin kayan jikin ta gata kyakykyawa tafita kyau ga iyayanta masu kudi tun Daga wannan Lokacin take jin haushin Imti gashi ko yaushe sai cigaba take ita tana komawa baya. Shiyasa tunda suka zama yammata kome Imti zatai saidai Fauza ta kara zugata ta ingizata atunanin Imti Fauza masoyiyarta ce ta hakika.
Kai hatta masu aikin Gidan su Fauza ke bata salo salon da zata kore su ita kuma wawuyar data koma gida zata gwada abinda Fauza ta kitsa mata,tasha shekawa yan aikin su tafasashshen tea wasu da dama da tabon konuwa suke barin gidan batare da sunyafewa Imti abunda tai musu ba.
Tunda tashigo Umma ke kallon ta ganin sai walwala take kamar ammata bishara da kujerar hajji,kasa hakuri Umma tai ta kalli Fauza wai wani abu kika samu kike wannan murnar Dariya ta danyi ai Umma abun farin cikine ya samemu anyiwa Imti Aure,kallon rashin fahimta Umma tai mata bangane akamme kike magana ba.
Ganin irin kallon da Umma ke mata yasa tai saurin gyara bakinta am wata kawata akaiwa Aure shine nake tayata farin ciki,tsaki Umma taja kyaji dashi aike gakinan sai kara gandamewa kike babu mijin Auran sai yan karya suyi miki karairayi sutafi kin kasa tsaida hankalin ki kisamu miji Nagari kiyi Aure.
Ita sana'a ko yaya take indai Miji zai fita ya nemo ba shikenan ba,zumbura baki Fauza tai tana kunkuni bataga dalilin da zaisa ta Aure kaba batare daka tara ba saika cika ka tumbatsa kudi na sosai ba muna kudi ba sai tazama babbar Hajiya ta zagaya kasashen duniya shine babban burinta.
Hmmm Fauza kenan
Mrs Baba Bello Abubakar
.......✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕 💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 40&41
Indo Indo Dije dake daka atsakar gida ta kwallamata kira, kamar bazata fito ba, sedai tafito, rai bace kamar zata fasa kuka ga hannunta da yake mata radadi dukan da Malam okasha yayi mata adazu da safe. Allon ta yayi daka daka amma taki wankewa, kullum biya mata yake amma kan yaki ja.
Da kika fito, kina kumbura ko duka na zakiyi, sunkuyar da kanta tai kasa (oh rayuwa, wai yau, Imti ce take sunkui dakai gudun kartai laifi dama ance duniya juyi juyi kwado ya fada ruwan zafi).
"Nuna mata kayan fitsarin 'ya'yanta tayi, bayan su, akwai kayan da suka saka sukai cidin cidin abun koko ne sharar majina ce, kai babu abunda babu ajikin kayan. Ga wanki na nan, maza ki dauka kiyi, saura suki fita na lahira saiya fiki jin dadi. Kuma baki da tuwan dare. Idanun tane ya ciko da kwallah ganin uban wankin da aka tile mata kamar wata jaka.
Rike kugu Dije tai, au ko bazaki yiba? saurin girgiza kai tai alamar àah, tuni hawayan fuskarta ya fara sakkowa.
"Ahankali ta sunkuya, ta dauki kayan. Wani babban baho ta dauka rijiya ta nufa danta debi ruwa. Wawakekiyar rijiya ce kana daga nesa ma ji kake kamar zaka fada, balle kaje kusa da ita. Kallon rijiyar kadai, sa kanta juyawa yake. Balle, taje janruwa cikin ta, ji take kamar janta akeyi".
Sai data debi daidai yadda zatai amfani dashi, takuma dukawa tafara wanki tanayi tana kuka abun tausayi (da gaske fa Imti tayi laushi da yawa) kumfar ce tai dauda ta zubar. Bakin rijiyar ta kara matsawa, ta zura guga, santsin kumfane ya kwasheta gaba daya tatafi jikake tinjim ta fada rijiyar.
Dafe kirji Dije tai, na shiga uku!!! Jama'a ku kawo dauki, Indo arijiya. Wayyo Allah na. Da gudu Almajiran dake kwar gida suka dinga fadowa.
Ya kumbo da bacci ya fara daukarta, wani allan dungure ta zuba sai gata atsakar gida. Daga ita sai wani buje kannan yayi fari sosai,gaban rijiyar ta tsaya ta dora hannu aka tare da fashewa da kuka, na shiga uku 'yar Amana arijiya wayyo Allah Dije kin cuceni, kin gama da rayuwa ta, kankace me, gidan ya cika yara da manya.
Igiya aka samu, aka zura yahuza ciki, tariga tayi kasa sosai, neman duniya be same ta ba. Ana tsaye, kowa kagani fuskarsa cike da damuwa, da alhini, kamar daga sama Ziyad yayi sallama cikin takunsa kamar yana sassarfa.
"Kare musu kallo yake kamar yaga sabbin halitta, hango shi da Ya Kumbo tai da gudu ta zuro tanajan hannun sa".
Yawwa Ziyadu, ga Indo can arjiya neman duniya ba aganta ba, katemaka acirota. Ras yaji gabansa ya fadi, karfa 'yar mutane ta mutu ahannunsa. Zabura yayi ya matsa kusa da rijiyar, kallon rijiyar kadai zai iya raunana zuciyarka. Da baya ya dawo, da sauri ya juya yafice, mintuna biyu ya kara dawo wa.
Tamkar dama tare da yan kwana kwanan ya taho,10mins sejin jiniyar motar su akai, su kusan 7 ne suka shigo cikin shirin aiki tsaf kai tsaye.
Bakin rijiyar suka nufa wata na'ura suka dakko kamar computer, bincike sukai be wuce na minti daya ba, mutum biyu ne suka fada rijiyar, abunka da wadanda su kasan takan aikin su, basu haura 5mnt ba saigasu dauke da Imti wadda jikinta ya saki gaba daya tamkar babu rai a tattare da ita.
"Yana tsaye, hannayansa a harde, idanun sa alumshe, bazaka taba tantance awane hali face dinsa take ba, ammafa, rannan nasa a hade yake cik, kamar bai taba sanin mene Dariya ba"
Alhmdlh da yaji ana ambata, ita, ta tabbatar masa da anciro Imti. "Ahankali ya bude idanunsa da suka canza launi zuwa ja, kallon sa ya mayar kanta, an akashimfide ta akasa, gashin kanta gaba daya ya tarwatse, ya mammanne, a face dinta, saita kara wani irin haske, da sheki, kauda kansa yayi daga kallon ta".
"Maida kallonsa yayi kan garadan Mazan da kowa ya dora idanu akanta, kamar sun sami TV". damma kayan jikinta, ba wadanda suka matse ta bane, amma, duk da hakan sun kwanta ajikinta, gaba daya surarta abayyane take,haka nan yaji ransa ya baci da zafin nama ya karasa wajan cak ya dauketa uffan bece da kowaba yayi hanyar waje da ita, yuuu Jama'a suka bishi abaya, kamar masu rakiyar gawa.
Duk da nauyin data kara saboda yanayin yadda ta sha ruwa, hakan be canza yanayin tafiyar sa ba, suna fitowa sukai arba da wasu shegun motoci, tunda sukazo duniya basu taba ganin azababbun motoci irin su ba, kara tamke Fuska yayi tunkan ya karasa aka bude masa wata farar mota, fara ce sol har daukar idanu takeyi, kai da ganin wannan motar a ranar aka bareta daga kwalinta.
Sauran gaba daya bakake ne akalla sunkai 20 jere reras, wasu manyan mutanene masu kirar karfi, duk wanda kakalla yadda kasan be taba Dariya ba.Fuskar nan ahade take, babu alamar fara'a, a tare dasu. Jikin su na sanye da suit black shor black sai suka hadu suka kara dafewa acikin kayan.
Nanfa kallo ya koma sama, 'yan kauye sai kallon kallo suke, wannan ya kalli wannan, wannan ya kallo wancen, kowa maganace abakin sa fal amma babu damar furtawa, duba da yadda wadannan kartin ke muzururai, abunda yakara firgitasu, kowanne su, dauke yake da binding AK-47 sai zazzare idanu suke.
"A dari da sittin sukaja moto cin da masifar gudu, motarsa ce atsakiya 10 abayan sa 10 agabansa, damma hanyar bata da dadin gudu amma duk da haka gudu suke shekawa, tuni Ogansu yayi musu inkiyar akwai matsala, Oga na bukatar tafiyar gaggawa"
"Sài da suka fita kan titi dodar, suka dauki hanya gudu suke kamar yaki" Tafiyar 50mnt sukai suka karaso airport, abunda ya matukar bani mamaki tamkar ansan da zuwan su, wasu guids ne akallah sunkai su 30 sukai wa motar kawanya, kamewa sukai kamar gumaka".
Minti daya zuwa biyu aka bude murfin motar kafarsa ya fara xurowa, kamar bazai fito ba, gaba dayan sa ya fito, ni kaina, saidana razana da ganin wanda yafito daga motar sàida nai suma nawucin gadi saboda tsabar kaduwa da Mamaki"
Wani azababban guy ne yafito, farine tas tamkar balarabe gashin kansa anannade ya kwanta luf, face dinsa sanye take da mask, bazaka taba tantance ya ainihin fuskarsa take ba.
Suit ce ajikin sa maroon color, saita sake fito da kyawunsa,wuyana kamar zai tsinke wajan leken ina Ziyad ta sama yabi kota kasa babu shi babu alamar sa, leka kaina nayi cikin motar wani sanyin AC ne ya bugi fuskata, babu abunda babu awannan mota, hatta TV akwai acikin ta.
Gadon marasa lpy aka gunguro har gaban motar, back sit ya bude guide dinsa ne suka taho da sauri, dan su ciro Imti, daga musu hannu yayi alamar baya bukata, cak ya kara dakko ta, tananan yadda take takara wani irin haske, tamkar wadda aka karawa kyau, haka hancinta yadawo kamar biro, dorata yayi akan bed din kafin sujata jirgi naga sun shige da ita.
Bani da zabi bayan nima nabi bayan su, guid dinsa kawanya sukai masa kamar wani shugaban kasa, na tabbatar wannan ba karamin mutum bane amma tunani na guda dayane, ina Ziyad ya shiga? haka naketa sake sake azuciya ta.
Babban jirgine, na gaske, tunda nake yaune karo na nafarko, dana taba shiga jirgi, tsabar yadda na rude da haduwar shi jinai kamar zan fadi, sai dakyar na samu nakai soket dina kan wata luntsumemiyar kujera, danci gaba da dakko muku rahoto.
Sai baza idanuwa nake naga Imti amma shiru ba labarin ta, kai tsaye wanann matashin inda matuka jirgi ke zama nan naga ya shiga, idanu na zaro dan ganin shine da kansa zai tuka jirgin jujjuyawa nai kaf cikin jirgi banga fasinja ko daya ba sai wadannan guide din, har wannan time din muzurai suke.
Futowa ya sakeyi wata kofa naga yaja ashe dakine, maida kofar yayi ya rufe akalla ya kwashe 30mnt kafin ya sake fitowa Uniform ne ajikin sa na pilot har wannan time din ya gagara cire mask din Fuskar sa.
Da tashin jirgin, da saukarsa, bazai wuce mintuna 30 saida jirgin ya daidaita akan kasa, kafin su fara jerin gwanon fitowa, motoci ne birjik da alama ansan da zuwan su.
"Doctors ne suka fito, daga wani daki, share zufar goshinsu sukai, alamu ya nuna, ba karamin aiki suka shaba, sun sha gwagwar maya".
Tattakawa yayi da kansa, dakin da suka shiga nan naga ya shiga, few minutes sai gashi ya fito dauke da ita ahannun sa, gown ce ajikin ta me azabar kyau da tsada, angyare mata kanta wani kalar style akai da gashin nata, Numfashinta na sauka a harharde alamu sun nuna har wannan time din bata dawo hayya cinta ba, wata shegiyar mota aka bude masa.
Sai Lokacin idanuna, ya kalli Number dake jikin motocin, baro baro naga an rubuta, Darma 1 Darma 2 kai yadda kasan saida aka zauna zaman jera Numbobin tsaye suke reras wannan nabin wannan, Mamaki ya kasa barin kwanyata Darma abunda nake nanatawa kenan, kamar nataba jin wannan sunan abaya, koma dai yane zan gano nan gaba kadan.
Sai dana karewa airport din kallo na lura ashe garin ABUJA ne, mata da yawa fata suke inama ko saudaya ne suga Darma, koda bazai Aure suba suyi magana dashi,karku dauka yayan Malam shehu ne, a'ah 'ya'yan jiga jigan kasar ne, ko wacce burinta Darma Dollars.
Aguje suka fita daga airport din, ko tafiyar 20mint ba aiba, wasu motoci ne akalla sunkai 10 karar harbi ce ta karade ilahirin titin, sun Matukar shammatar guide din a bazata suka kawo musu hari, dayake suma manyan kaine cikin kwarewa suka fara maida martani, da san kare ogansu duk Abinda akeyi ko motsawa beba, yana kwance bawai dan bayaji ba, a'ah ba sukai wadanda zasu tsaya yana bacin rai akan su ba.
Anshafe 20 mint ana gumrzu, da tata burza, suma maharan da gani sun san takan aikin su, cikin bakaken kaya suke baka ganin komai na jikinsu hatta da gashin kansu anannade yake.
Babban burinsu su hari motar sa, amma yaransa sunki bada damar hakan, basu fasa sharara gudu akan titinba, haka suma basu fasa bin suba,gaba daya titin ABUJA gagarar bi yayi Jama'a kowa ta kansa yake, Matukar kanasan tsira da rayuwar ka.
"Motar Soldiers ce ta cika titin kawanya sukai wa motocin dan bada kariya agare shi, hakan ya bawa motocin Darma damar tserewa maharan suka barsu suna fafatawa da Soldiers din"
Hmmm ana wata ga wata kaka kara kaka ga Imti ga Ziyad yanzu ma aka fara fans kuci gaba da surbudo comment naci gaba da sanbado muku labari.
Tim din Imti kunji dadin barowarta kauye ko kuwa,zata fara rayuwar jindadi koda sauranta,ina tim din Ziyad? sainaji ra'a yoyinku.
Mrs Baba Bello Abubakar
......✍️✍️✍️✍️
IMTINAN
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 42_43
Huci me zafi ya furzar, wata katafariyar unguwa suka shiga me azabar kyau da tsari, security ne tako ina, haka suka dinga silalowa suna shiga Unguwar, tsai dasu yayi cak suka da kata a tsakiyar unguwar, ko karin futowa yake da azama suka budemai kofa,fitowa yayi back sit ya bude ya zaro Imti mota daban ya sakata aciki drive sit ya zauna zasu biyoshi ya daga hannu alamar baya bukata.
Da mugun speed ya taka motar ya fice daga unguwar baki daya, akalla yayi tafiyar 40mnt kafin ya iso wata Unguwa daka ganta kasan Unguwar masu rufin asiri ce, akwai kananan gidaje acikin ta dai dai kofar wani Gida ya faka motar baza'a kira Gidan da kwarababbe ba ba kuma za'a kirashi me kyau ba.
Yadan jima da tsayawa kafin ya fito ya zagaya kofar gidan key ya ciro daga aljihun sa ya bude gidan,again sake dakko ta yayi sai daya dangana da cikin daki ya ajiyeta, babu komai agidan sai wata katifa sabuwace kar sai ledar tsakar daki dakuna biyune agidan sai Kichin, da bandaki, sai tsakar Gida, daya fara farfashewa.
Kan katifar ya direta yana sakin huci me zafi ransa bace ya juya ya fice daga gidan,mintuna 15 da fitarsa ta bude idanun ta da sukai mata nauyi jitake hancinta ya tattoshe hatta kunnan ta wani dum take jinsa kamar ba nata ba.
Karewa dakin kallo tai nan ta tabbatar ba dakin ya kumbo bane to inane nan, ya akai aka kawota wanann gidan, jikinta ta kalla ganin kayan dake jikinta ya sakata saurin mikewa tana karewa jikinta kallo wanene ya saka mata wannan kayan, tukunnama inane nan? tasan dai ta fada rijiya kodaga rijiyar ne ta zarto nan abunda take ayyanawa kenan azuciyarta.
Ga zafin daya addabe ta ga yunwa da take cin cikinta 'yayan hanjinta sun masifar kullewa, kanta sai kjuyawa yake kai wahala goma da ashirin,tana nan zaune batasan iya adadin Lokutan data kwashe ba, ko mikewa ta kasayi, gaba daya jikinta yayi mata wani irin sanyi jitake kamar babu laka ajikinta.
Alamun shigowa taji zubawa kofar idanu tai tana jiran ganin wanda zai shigo,ido biyu sukai da Ziyad jikinsa sanye da wata kodaddiyar shadda tasha ruwa taji jiki wata muguwar hula ya dan kwafa aka face dinnan tasa a hade babu alamar annuri. Kallon tsana da kyama Imti ke binsa dashi, aduk lokacin data tuna wai akwai igiyar Auran sa akanta tana tsintar kanta cikin tsananin bakin ciki da bacinrai.
A wannan Lokacimma fashewa tai da Kukan bakin ciki, jingina yayi yana kallonta hannunsa harde akirji wani murmushi ya saki, sake kular da ita yayi kamar idanunta zasu fado take hararar sa tsaki take ja ajajjere,gimtse face dinsa yayi arayuwar sa ya tsani tsaki koda da kuskure ne balle kuma ana sane ayi masa shi.
Juyawa yayi da sauri yabar dakin, matukar yaci gaba da tsayawa shakka babu zai iya aikata mata ko menene,saida tai kuka ma ishi kafinta share hawayanta.
Cikin wadanda sukai gudun ceton rai harda Dad, ahanyarsa ta dawowa daga meeting, saura kadan bullet ya bula masa kwanyar kai, da zafin nama ya sunkuya bullet din ya fita ta glass din motar sa, Hankalin sa tashe ya karasa Gida sàida ya shiga maine parlour Hankalin sa ya kwanta.
Ummee dake kallon News abunda aketa nunawa kenan irin bata kashin da akai a titin ABUJA. Kallon Dad tai dayayi wuri wuri kamar wanda aka tsamo daga cikin ruwa. Dady Lafiya kuwa? zama yayi yana sauke Numfashi, ina Lafiya Amina inacan cikin masifa, yau Darma ya shigo ABUJA aka kawo masa hari saura kadan abun ya shafe ni.
Kai Alhmdlh tunda Abun be shafeka ba mungodewa Allah, Numfashi ya sauke kai ai wannan dan iskan yaron kwaro ne nake gayamiki, duk wata hanya da za'ai samu information akansa ya rufeta ke kaf garinnan bazan ce miki akwai wanda yasan taka maimai inda Darma yake rayuwa ba, yawo yake sassa daban daban. Office dimmu babban fatammu muzauna da Darma ko saudaya ne, zamu samu babban cigaba in yazuba hannun jarinsa amma shegen ganinsa ya gagara.
Numfashi Ummee ta sauke, kai ainima wannan abu yana ban mamaki kana ganifa 'yar gidan kawata Hajiya Jamila 'yarta Nusaiba tana can bata da Lafiya tace inba Darma ba bazata Auri kowa ba ninarasa wannan masifa wllh.
Shiru Dad yayi aduk sanda yaji an ambaci 'yar wasu saiya tuna da tasa yar, da besan adunyar da take ba,hawaye ne yake zuba aface dinsa, zuba masa idanu Ummee tai idanun ta na cikowa da kwallar ita ma, tana matukar tausayin Imti ko saudaya basu taba jinta awaya ba tsahon wata 7 saidai suyi magana da Ziyad ya tabbatar Musu tana Lafiya.
Bata taba zatan zatai kewar Imti irin haka ba, jurewa take tana matukar san sanin awani hali yarinyar ta take, amma tana dannewa sabida Dad. Matukar ya daga hankalin sa jinin sa ke hawa sai Doctor ya dubashi,share hawayen face dinsa yayi yanzu Ameena kina ganin Abba yayimin adalci, ya dauki 'yata ya bawa fakirin talaka shikansa be ciyar da kansa ba balle ya ciyar da 'yata.
Kayi hakuri Dad kasan Abba bazai taba cutar dakai ba, ka kara hakuri zamiyi Alfahari da Auran Imti,rai bace Dad ya mike ke dai zakiyi Alfahari tunda dama ba kaunarta kike ba, ke har mahadi ya bayyana bazanyi Alfahari da wannan Auran ba, ya zama dole ya sakarmin 'yata komai daren dadewa fuuuu yabar wajan ransa na kuna. Binsa da kallo Ummee tai Allah ya kyauta.
Tashitai ta futo daga uwar daka iska kamar zata kayar da ita, yana zaune akan tabarma dakin ko arzikin sofa be samu ba,zuwatai ta tsaya akansa kamar ta shakeshi haka take ji. Cikin dacin zuciya take fadin kaga malam yunwa nakeji tunda dama kai kasaba da tsiya da talauci ni ban saba dashi ba.
Kuma wannan kayan na jikina a ina kaje ka samo su? na tabbatar sato su kayi, dan baka da arzikin da zaka iya siyamin wannan kayan, kai kanka kalli jikin ka,talauci yayima dabaibayi,kasakeni,natafi inda zan huta na wataya nasha iska,in har kayadda nabar hannun ka, asannan zaka gane wacece Imti bana sanayya,bana ragayya,wannan karan sharrin da zamma ba abayan kanta za'a saka kaba, rataye ka za'ai da ranka.
Banza yayi kamar be jita ba, dun gure masa kai take tana ci gaba dayi masa rashin kunya, caraf ya murde hannun kara ta saki sabida azabar data ziyar ceta,fadowa jikinsa tai tana gunjin kuka amma tsabar mugunta irin ta Ziyad kin sakinta yayi, saidaya tabbatar bakin rashin kunyarta ya mutu kafin ya cika mata hannun.
Jitake kamar ba ajikin ta hannun yake ba,kasa motsa hannun tai gaba daya,har time din tana kwance dare dare acinyar sa da alama ta mance inda take,tunawa akan cinyar watake tai saurin mikewa, tana karkade jikinta, da sauri tabar wajan tana rike da hannun ta, Murmushi yadan saki shikadai yasan ma'anar Murmushin sa.
Betashi kawo mata Abinci ba sai Magariba, wata tsohuwar langa ya dauka shinkafa da wake ya siyo mata anan wajan me sàida abinci, batafi ta 150 ya siya ba, yar tafat bata da yawa yana shigowa ya dangware mata agaba, inkinga dama ki dauka kici inbakyaci nakaiwa almajirai.
Abincin take kallo ta kalle shi tsabar ya raina mata hankali, yarasa abunda zai kawo mata sai wannan busashshen Abincin, gashi bamai ba yaji,boll tai da langar Abincin aiko ya bare akasa kallonta yakeyi yama rasa meze ce mata, kafadarsa ya daga alamar ke kika sani hanyar kofa yayi sam besan sanda tataso ba, jinta yayi kawai ta rungume shi ta baya Kuka ta fashe dashi.
Wallahi bazan zauna ba saika maidani gidan ubana, saidai mutafi tare bazan zauna awannan gidan ba nikadai kamar mayya,rintse idanun sa yayi jin albarkatun kirjinta na sukar bayan sa.
Da sauri ya janyeta daga jikin sa tuna wasu karatan banza sunga ma amfani dashi, mazan gari babu wanda be kalle suba, makoshinsa har wani daci yake wani dunkulallan abune ya tokare mai a kahon zuciya.
Yunkurawa tai zata bishi amma ina kafin takai kofa ya fice tare da janta da mugun karfi, key ya sawa kofa asoron ta zube tana sakin Kuka me taba zuciya, wane irin Laifi ta aikatawa Abba, data cancanci wannan hukuncin agare shi, ya kashe mata rayuwa ya cuceta matukar cuta.
Mikewa tai ta dawo cikin gidan sai kuma tsoro ya kama ta, Kukan maguna ta faraji sosai take tsoron mage da gudu ta karasa dakin tare da datse kofar tana rushewa da sabon kuka kamar zata shide. ALLAH sarki Imti
Kwanan wahala tai awannan rana tana bacci tana firgita, sai taji kamar magen ke tafiya ajikinta farkawa tai taganta akan katifar dakin, yana gefanta akwance babu wata damuwa atattre dashi, talakan banza dama ina zaka kasa bacci ka saba da wahalar rayuwa.
Sauka take kokarinyi bazata taba kwanciya waje daya da shiba, gudu taji anayi akan kwanan kamar mutane ke wannan gudun amma duk wannan didifniyar maguna ke yinta,asukwane ta fada kan katifar kusa da Ziyad ta matsa gaba daya hannun ta tasa ta kankame shi,jikinta na matukar kakkarwa duk abinda takeyi yana jinta amma banza yayi da ita ko sau daya be nuna yasan tana yiba.
Yayi niyar tureta amma ganin yadda jikinta ke rawa hakan yasa ya rabu da ita. Da Asuba da kyar ta sakeshi Kuka take rusa masa saiya fitar da ita daga wannan gidan, jinta kawai yake buta ya dauka toilet ya shige kafin ya daura Alwala, agida yayi sallah saboda yanayin unguwar be gane kanta ba.
Kan tabar mar parlo ya sake kwanciya, wajan karfe 9 ya dauki cup ya siyo mata koko da kosai, bata da zabi wanda ya wuce tasha.
Mrs Baba Bello Abubakar
.......✍️✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 44_45
Tana sha tana matsar kwallah, babu suga haka ta dinga sha,😭😭 hawaye wani na korar wani, ashe haka yunwa take dama, shiyasa zakaga mutane kamar zararru, yunwa babu abunda bata sawa,yana kallon duk wani movement din ta, dariya ce take son kufce masa, amma ya gimtse, lallai ya yadda girman kan Imti ya fara sauka.
Kadan ta rage, sai Lokacin taji ta dawo dai dai, sai kuma zafi daya addabeta, mikewa tai tafice, gidan akwai panpo wani tsohon boket ta gani, tarashi tai ya cika taf kafin ta dauka takai toilet, babu sabulu haka ta kwakwkwara ba Laifi taji dadi ajikinta,kayan jikinta ta mayar inda dane bazata taba sa kaya ta kara maaitawa ba, yau segashi tayi wanka ta maida na jikin ta.
Kanta asunkuye ta shigo dakin, yana zaune inda tabarshi, ya kamata taiwa Ziyad da bara, ko ya fitar da ita daga Gidannan, inyaso saita gudu daga baya,a sanyaye ta matso inda yake, zama tai tare da tankwashe kafa. Yaya Ziyad ta ambata, ita kanta wani banbara kwai taji balle shi da aka fadawa, dan bude idanun sa yayi ya zube su akanta.
Dan Allah kayi hakuri abunda naima abaya sharrin shedanne, ko kuma kece shedaniyar ba, ya ayyana hakan a zuciyar sa, please for give me har wata kwalla ke zuba a idanun ta irin ya yadda dagaske tayi Nadama. Dan Allah kasakeni natafi gidammu kayiwa Allah ka rabu dani.
Hade hannayan ta tayi alamun roko agare shi, kallonta yake da wani irin yanayi dana kasa tantan ceshi,Numfashi ya furzar saki kike bukata? saurin gyada kai tayi alamar eh, huci ya furzar zan sake ki, washe baki tai,da tsananin farin ciki,amma ba yanzu ba,fara'ar fuskarta ce ta dauke,sai yaushe? kamar zata fashe da kuka.
Nina barwa kaina sanin lokacin,amma zanso ki sanar dani dalilinki na neman saki agare ni. Shiru tayi to me zata ce masa, ina sauraronki, kawai banajin sonka a zuciyata, ni ban taba jinka a zuyata ba.
Murmushi ya saki gyara maganar ki, aidama batun so babu shi, kamar yadda bakya sona, haka nima bana sonki,ke gaba daya ma wahala kika zamemin, kinga nima da zamu rabu ayanzu sainafi kowa farin ciki,shiru ya danyi yana sake duban Imti fadi abunda ke ranki.
Muskutawa tai, bazan iya zama da talaka kamar kaba, kai gaba daya mani bazan iya Rayuwar talauci ba, wannan wahalar daka bani kaje na yafema, amma daga nan wajan ka sallame ni nai gaba.
Dan Lumshe idanun sa yayi shi talaka ba mutum bane kenan? ko kina tunanin Allah ya manta dashi? ku ya baku kudi shiya barshi a talaka,to kisani, Allah yana sane dashi, da sannu wannan talakan Allah zai azurtashi.
Kallonsa take da manyan idanun ta, ji take kamar busa yake mata, bazata taba yadda talaka zai dawo me arziki ba, musamman ma shi.
Kasa hakuri tai ta kalle shi a yatsine, amma banda kai, dan tsiya da fatara awajanka suka kare, ni bantaba ganin wanda Talauci yayiwa da baibayi ba kamar ka, har abada banga ta hanyar da zaka sayi ko bulo ne ka ajiyeba balle kasamu kudin siyan fili.
Dan ware idanun sa yayi akanta, ada na dauka kin zubda makaman yakinki, tarbiyya ta fara hawa kanki, ashe ba haka bane, saboda kin samu sarari kinsha iska abirni, to yanzu kuwa zan maidaki kauyan can da kika baro.
Mikewa yayi alamar abunda yafada shi zai aikata, fashewa tai da Kuka ni wllh bazan koma kauye ba, bazan taba yadda nafito daga cikin wuya na koma cikin taba,sun kuyawa yayi alamar zai dauketa, da sauri ta kankame kafafun sa, Kuka take kamar wanda yace zai maida ita prison,haikan aziman take Kuka, baji ba gani, yana tsaye yana kallon ta, cikani, abunda yace mata kenan.
Kin sakinsa tai jan kafarsa yake kokarin yi, tana sake mannewa kamar kaska,abazata yaji ta fado jikinsa, sai daya runtse idanun sa, kokarin raba ta da jikinsa yake tana sake manne wa,batasan a masifar data sashi ba, amma ta sake shi abu ya gagara jingina yayi da bango ya runtse idanun sa da masifar karfi, yadda taji bugun Zuciyarsa abun ya matukar razanar da ita, da sauri ta sake shi.
Dama abunda yake jira kenan wuff ya fice daga dakin, gaba daya ma gidan ya bari a gaggauce, Imti ta ballo masa masifa sai jan tsaki yake kamar zai tsinke bakin sa,binsa tai cike da Mamakin meya canzashi lokaci guda, baki ta tabe koma dai mene ina ruwana, tunda dai be tafi dani ba.
Be dawo cikin gidan ba sai da Magari ba, kin yadda yayi su hada idanu, bakar Ledar daya shigo da ita ya dire agan ta,uwar daka ya shige ya barta zaune a parlo, jawo Ledar tai ta bude, wani kamshine ya bigi hancin ta, gurasa ce da nama taji cabej da tumatur, ta sha kuli kuli, makwat Imti ta hadiyi yawu, andade ba'a hadu ba.lol
Duk yawan gurasa da naman nan sai data kusa cinye su tas, drink din daya kawo mata taja ta bude, sàidata kwankwada ta dire tana maida numfashi, har wani gumi ne yake yanko mata,ragowar ta dauka har daki ta bishi da gurasar, ga naka kaima,kallon ta ya danyi, ni talaka ina zanci wannan ai sàidai ku masu kudi.
Shiru tai tana kallon sa, ta kara auki dama ba kalar ka bace, "hakamma tausayi ne yasa nayi ma tayi"juyawa yayi ko kala bece mata ba, gama tsayuwarta tai ta samu waje ta kwanta, daga can gefan sa,mikewa yayi tsam ya koma parlo. "Sake gyara kwanciyar ta tayi dama ya takura mata" aiko bajewa tai tasha baccin ta.
Tun daga wannan rana Imti ta farayiwa Ziyad ladabi, har dukawa take ta gaishe shi, dan duk yaketa tatafi,sarai yasan ba biyayyar gaske take maiba, ta gulma ce, basarwa yayi kamar besan abunda take yi ba.
Tunda tazo gidan da kaya daya take rayuwa, wannan doguwar rigar ita kadaice kayanta, sedai intayi datti, ta kulle gidan, ta tube, ta wanke ta, saita saka hijab haka zata zauna jira harsaita bushe zata saka.
Tana zaune a tsakar gida ta zuba uban tagumi, abun Duniya ya hade mata Dady take tunani batasan hawaye na zuba a Fuskarta ba, saidata taba taji danshi a Fuskarta, ALLAH sarki Dady ko yana ina yanzu yana tunani koya manta dani,tasan Ummee bazata taba yin kewar taba, dama ta gaji da ita ba kaunarta take ba, rushewa tai da kuka.
Tunda yashigo yake tsaye akanta dan furzar da hucin bakinsa yayi, waya ya ciro daga aljihun sa, kira ya danna ring Biyu aka daga, mika mata yayi kamar bazata karbaba, saidai ta karba, kara wayartai akunne dan jin wanda yake son yayi magana da ita.
Ziyad taji am ambata, cikin muryar da ko shekaru nawa zatai bazata manta da muryar ba,Ummee ta ambata cikin tsananin Farin ciki, abangaran Ummee sàidata mike tsaye, Imti ta ambata cikin matukar kaguwa da fatan Allah yasa ba gizo kunnuwanta ke mata ba.
"Cikin rawar murya take fadin Ummee kece? kamar tana gabanta take gyada mata kai nice Imti, idanun ta cike da kwallah na tsananin kewar 'yar tata"
A bangaran Imti hakan takeji ashe dama haka akejin kewar Mahaifiya, idan akai nesa da ita, bata taba zaton tana son Ummee ba, saidatayi nesa da ita,cikin zakuwa Ummee kefadin kina jina Imtinan? eh Ummee hawaye na sake shatata akuncinta gaba daya sunkasa magana yadda Imti ke sharar hawaye haka Ummee ke sharar hawaye.
Wata irin kewa ce da basu taba zatan in sukai nesa da juna zasuji ta ba. I'm really missing you Ummee same too Imtinan Ummee ta furta ahankali.
Muryar Dad ta juyo yana tambayar kukamme take yi mikamai wayar tai ba tare data furta komai ba, kara wayar yayi a kunnan sa cikin so happy ta furta Dady, ko daga magagin bacci ya tashi yasan muryarta, harshan sa na rawa Lele kece? eh Dady nice nice take furtawa kamar ta jawo su su karaso gare ta, zaman sofa ne ya gagari Dad dakkowa yayi gaba daya ya zube akasa.
Jikin sa har rawa yake yaushe zanganki Imti, daga kanta tayi ta kalli Ziyad daya tsura mata idanu, tamkar yau yafara ganin ta, azahiri ba ita yake kallo ba wani wajan yake kallo daban kunnan sa gaba daya baya tare da ita. Nima ban san sanda zan zoba Dad, kifada min inda kike nazo na dakko ki,girgiza kai tayi hawaye na sake zuba a idanunta, bansan inda nke ba bansan inane nan ba.
Rushewa tai da Kuka me tsuma zuciyar me sauraron ta, ciwo takeji a Zuciyar ta. Tana matukar son Dad dinta gashi tayi nesa dashi batasan ranar daxai zo gare taba ko ita taje gareshi,fadamin Lele yana yimiki wani abune namiki alkawari sai nayi shari'a da wannan yaron, dolene ya sakeki kota halin kaka sai kinbar hannun sa,dago kanta tai suka hada idanu da Ziyad data kasa tantance fuskarsa awane hali take.
Kawar da idanun ta tai daga kansa, kallon cikin idanun sa na matukar bata tsoro, aduk sanda suka hada idanu, bugun Zuciyar ta karuwa yake, tarasa me yasa yake mata kwarji ayanzu.
Ba kyaji na Imti zanzo na dauke ki Imti saiya sakeki, indai kudi suna magani, Ummee ce ta amshe wayar ganin zai sake hautsina mata yarinya.
Imti ina so ki zauna Agidan Mijin ki, kici gaba dayi masa biyayya, matukar kika bishi zakici riba Imti. Karki manta Ajannarki tana karkashin kafafunsa, saiya daga zaki shiga,kizama kamilar mace, me Alfahari da gidan Mijin ta, haka Miji yayi Alfahari dake, kimin alkawari Imti zaki zauna da Ziyad da zuciya daya, kisani ba wanda yafi wani awajan Allah sai wanda yafi jin tsoron sa da bauta masa abinda aka haneshi yayi nesa dashi, abunda aka umar ce shi ya aikatashi.
Yayi Umarni da kyakykyawa, yayi hani da mummuna, ita dukiya Imti ba komai bace Allah yana azurta wanda yaso yamaida talaka mekudi ya talauta wanda yake da arziki, duk wannan cikin kudurar sane da ikon sa,ina mai tabbatar miki Ziyad mutumin kirki ne, ninaji hakan ajikina bazai taba cutar dake ba Imti amatsayina na Mahaifiyar ki Umarni nake baki kiyi masa biyayya.
Kimin alkawari Imti bazaki bani kunya ba,kuka Imti take tun fara maganar Ummee, taya zatai mata Alkawari bayan tasan bazata iya zama da Ziyad ba, bazata rayu da shiba har abada, baya ranta, baya daga cikin mzan da take burin Aura, wanda duniya ta sanshi, wanda kowa fata yake ya rabe shi, wace riba zataci azamanta da Ziyad, sai bacin rai da bakin talauci.
Inajinki Imti ke nake saurare dago fuskatai ta kalle shi, yana inda yake atsaye ba ita yake kallo ba, maida kanta kasa tai bazan iya ba Ummee, biyayyar ce bazaki iya ba dama nadade da sanin ban isa dake ba Imti kaf Duniya babu wanda yakai ni sonki, ya kaini kaunarki, duk wani ci gabanki nikadaice akaf duniya bazan miki bakin cikin samun sa ba sai mahaifinki.
Keko ciki daya Kuka fito da mutum yanzu ba abun yadda bane, akwai cigaban da zai sameka dan uwanka ciki daya yaji hassada aziciyar sa, akan wannan daukaka daka samu,shin kina zatan zan zaba miki abunda zai cutar dake Imti,Numfashi Ummee ta sauke amsar daya ce à'ah,bazan saki abunda nasan bazakici ribar saba kidaure kidanne zuciyarki ki koyi son Mijin ki, wata rana zaki soshi fiye da yadda kike son kanki, zakiji hatta Rayuwar ki zaki iya bayarwa danki fanshi tasa.
Goge hawayen fuskarta tayi anya tayiwa Ummee adalci kuwa, tin data haifeta take fama da ita, sanin kanta ne Ummee tasha yin Kuka agaban ta, saboda bakin cikin da suke cusa mata ita Dad,abaya bata taba jin maganarta ba, koda saudaya meyasa ayanzu ba zata karbi maganar taba, anya tayiwa Ummee adalci kuwa?.
Tambayar datayiwa kanta kenan, àah tabawa kanta da kanta amsa, zanyi abunda kikace Ummee zanyi, tafada tana ci gaba da share hawaye, murmushi Ummee ta sake tare da lumshe idanun ta, yau rana ta farko, karo na farko, Imti ta karbi maganar ta, duk asanadin Auran Ziyad, ta Tabbatar wannan Auran akwai Albarka acikin sa.
Allah yayi miki Albarka.Imti baki taba faranta min irin yau ba, in kikai hakan kin goge dukkan laifukanki na baya, wadanda kika aikata agare ni, nayafe miki Duniya da Lahira, Imti inai miki dukkan fatan Alkhairi khairi acikin rayuwar ku.
,Dif Ummee ta kashe wayar jin Kuka ya taho mata, yau karon farko Imti taji magarta, abunda ta dade tana roko da fata, daga hannun ta tai sama ALLAH na gode maka, daka shiryar min da Imtinan kaci gaba da karemin ita, katsaremin ita, aduk Inda zata shiga.
Dad da yake kallon ta hawayan shima ya share, dama Ummee tana jin ciwo da dacin abunda suke aikatawa agare ta? tunda ta haifi Imti bata huta ba, kullum bata mata rai suke, jiyayi yana jin kunyar hada idanu da ita, a sanyaye ya tashi ya haura sama ta bishi da kallo.
Kan kame wayar tai a kirjin ta, Kuka ta sake saki me tsanani zafi da kuna takeji a kirjinta, dama tana kaunar Ummee haka, dama Ummee tanajin dacin kinjin maganar ta, ina ma zata tariyo rayuwar ta tabaya, data gyara kura kuranta, da taji maganar Ummeen ta, da tayi hidima agare ta.
Jin saukar hannayan sa tai a kumatunta, yana share mata hawaye, dago idanun ta tai tana kallon sa, sam ta gaza gane awane yanayi fauskar sa take.
Ni kaina wannan page ya bani tausayi matuka saidana share hawayan fuskata iyaye dabanne iyaye na musammanne masu san ci gaban ka akoda wane lokaci masu sanya ka akan hanya da zarar kafara karkace wa.
Allah kabar mu da iyayan mu Ameen.
Fans natabbata wannan page kuma ya taba zukatan ku inajiran ganin ruwan comment.
Kuci gaba da bina yanzu ma aka fara.
Taku me muku fatan Alkhairi akoda yaushe.
Mrs Baba Bello Abubakar
........✍️✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 46_47
Wani Murmushi ya sakar mata da bata taba gani a face din saba, saida Numfashinta ya kusan daukewa, kura masa idanu tai kirjinta na lugudan faduwa, da sauri taja da baya tamkar ba Ziyad take gani agabanta ba, sai yanzu ta lura da hakan.
Wannan wani hadaddan balarabe take gani agaban ta, gashin kansa ta kalla daya sakko har kunnuwan sa luf luf gashin ke kwance akansa, sajan Fuskar sa ta kalla da yayi matukar kawata Fuskar sa, cikin rawar murya take nuna shi da dan yatsa wanene kai.
Tabbas wannan ba Ziyad bane, amma idanun sa sun tabbatar mata dashi dinne, dama farine ya koma chocolate color, ina wannan cukurkudaddan gashin nasa? ina wannan gemun dayake duguzun zuzun? ina wadannan gaftara gaftaran hakwaran nasa? cikin Kuka take fadin who are you tana yi tana matsawa baya cak ya tsaya yana kallon ta, blue eyes ne dashi tamkar mejin bacci haka idanun sa suke.
My name is Ziyad Muhammad Muhammad,yana tun karota tana matsawa baya, sosai zuciyarta ke razana aduk lokacin da take kallon sa, Numfashinta ne ya fara barin gaggar jikinta, kwarjinin sa ya cikata yayi mata yawa, ta kasa dauka bazata iya ba, shine dalilin sumanta, kantakai kasa caraf yayi wani tsalle ya taro ta gaba daya ta fado kansa, daidai nan Numfashinta ya bar gangar jikinta tai suma na wucin gadi.
Kurawa fuskarta idanu yayi hawaye na taruwa akwarmin idanun sa, cak ya dauketa yayi hanyar fita da ita, wasu tsofaffine guda biyu, da alama miji da matane, mikillin gidan ya mika musu har kasa suka duka suna zabga masa godewa angode Alhaji Allah yasaka da Alkhairi Allah yasa kafi haka gaba yayi batare daya amsaba.
Wata dalleliyar motace akofar gidan sabuwa ce kar 2023 Toyota RAV 4 back sit ya kwantar da ita kafin ya yiwa motar key, har wanann time din tsofaffun nan basu daina kwarara masa Addu'a ba.
Sai da su kaga kulewar sa, kafin su fada gidan sunan goge kwallar farin ciki.
Tafiyar 30mnt ya isa wani katafaran Hotel tin kafin yazo an yimasa bking, key din ya karba a hawa na biyu room din yake budewa yayi har wannan time din Imti bata farko ba, tana a yadda ya dakko ta, katafaran bed na alfarma anan ya kwantar da ita,furzar da isaka yayi daga bakin sa.
Kallon sakanni yayi mata da hanzari yabar wajan toilet ya fada, sai daya cika bathtub da ruwa me dumi, kafin ya shige ciki ajiyar zuciya yake saki a jejjere kamar wanda yayi wasan tsere.
Ya jima aciki kafin ya fito jikin sa daure da towel hannusa dauke yake da karamin towel yana goge kansa, ni kaina haryanzu na kasa yadda Ziyad ne wannan ingarman Namiji ne, jikinsa a mummur de daga ninsa yana ya samu trening na musamman, saidaya gama shafe shafen sa gaban wata akwati me shegen kyau ya tsaya, saidaya sa password kafin akwatin ta bude, naso lekawa na gano muku menene aciki saidai kash nima Zuciyata ayau ta cika da tsoron New Ziyad.
Wata tsadaddiyar waya ya fito da ita, ko ba afada ba kasan cewa an narka makudan kudade kafin amallake ta, wata number ya laluba maganar minti daya akai ya yanke kiran,wasu kaya ya dakko yasa ka abayan rigar an rubuta ADIDAS fararene kar wandon bekai guiwa ba, tsaf ya tsaya gaban mirror ya gyara sumar kansa, har wani style yayi mata sak balarabe haka ya dawo.
Sun ko amshe shi ba karamin kyau sukai masa ba, 5mnt akai norking tashi yayi ya bude order Abinci ya yimusu karba kawai yayi yamaida kofar ya rufe, wadda takawo abincin tasha wani mini skirt sai karairaya takeyi amma ko kallo bata isheshi ba, abun ya bata haushi kan dole ta juya tatafi.
A hankali ta fara bude idanunta da sukai mata nauyi, sosai take karewa dakin da take kwance kallo,ganin ta akatafaran daki tamkar ba a Nigeria take ba, yasata saurin zabura,ta kasan ido yake kallon ta saika rantse bacci yakeyi.
Sai Lokacin idanunta ya sauka akan sa, can karshan gadon ta koma sosai tsoron sa ya darsu azuciyar ta, takasa yadda wannan din Ziyad ne kamar yadda ya sanar da ita.
Fashewa tai da wani marayan kuka, hade hannayan ta tai waje daya dan Allah kaimin rai kadaina bibiyata, ina Ziyad dina, kai ba Ziyad dina bane, cikin subul da baka ta furta hakan gaba daya ta rude taya Ziyad fakirin talaka zai zama wannan hadaddan Handsome din.
Abazata yaji kalmar ta dira a kunnan sa harsai daya dan Lumshe idanun sa, bude su yayi ya zubesu akanta, da saurin ta kawar dakai shanyayyun idanunsa na razanar da ita.Murmushin gefen baki ya saki kaji munafuka wai Ziyad dinta, ahankali ya taso daga kan sofar da yake kwance sai kwarjinin sa yacika dakin gaba daya sake takurewa tai tana rusar kuka.
Abunda ya bashi dariya dama Imti akwai wata halitta da zata bata tsoro, hatta razana kanta haka,yana matsowa gareta bugun zuciyarta na karuwa, kan bed din ya hau batare da tasan ya matso inda take ba, jin hannun sa tai ajikinta gaba daya yadakko tamkar baby, sake zaburatai zatai baya, saidai kash, rukon da yayi mata ba wanda zata iya kwacewa bane, rukone irin na jarumai.
A faffadan kirjinsa ya sakata wanda ke cike da gargasa tayi luf sai sheki take, jijjiga ta yake kamar baby, sam baya fatan ta kara sume masa, sai daya tabbatar ta fara samun nutsuwa, da ita ajikinsa ya mike fridge ya bude ruwa me sanyi ya dakko tare da cup, da wowa kan sofa yayi ya zauna har wannan lokacin be ajiyeta ba, sai zare idanu take kamar sakarya gaba daya jikinta rawa yake jinta ajikin Namiji dare dare.
Wanke cup din yayi cikin wani bowel ya zuba ruwan, tsiyayawa yayi a cup din yakai bakinta, bata da zabin daya wuce ta karba, face dinsa adinke take tsaf tamkar be taba dariya ba,sàidata sha medan yawa ya cire cup din daga bakin ta.
Jingina yayi da jikin kujerar tare da lumshe idanun sa, wani kamshi takeji wanda tarasa inda tasanshi,ras gabanta yafadi tabbas ajikin Ziyad takejin wannan kamshin, har tambayar sa tatabayi awulakance ta kalle shi.
Waiko ka fara satane wannan turaran na jikinka, tas sai ansai da gidanku na kauye, ahada da gonar tsoho, in tsohuwa ma tana da tata gonar asiyar, kafin kasayi wannan turaran,awannan Lokacin ko kala bece mata ba sai binta da yayi da kallo, amma gaba daya yanayin fuskarsa ya canza.
Tunawa da abunda tagayamai taji gabanta ya fadi, in har wannan Ziyad ne to taya ya canza kamannin sa batare da kowa ya gane hakan ba, tana bukatar amsoshi daga gare shi, amma tasan ko giyar wake tasha a yanzu bazatai masa tambaya ba ta zabi ta rufe bakin ta ruf.
Tofa anzo wajan wai Imti ta fara nadamane ko haryanzu zata nemi takardar sakinta,menene dalilin Ziyad na boye ainihin kalar sa ya boye wanene shi,duk ku biyoni danjin yadda zata kaya.
Taku har Kullum Mrs Baba Bello Abubakar.
......✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 48_49
Sake mikewa yayi da ita ajikin sa, toilet taga ya nufa da ita, a mamakance take kallon sa me yake nufin yimata a toilet din, sarai yaga kallon datake masa amma ko afuska be nuna yasan tana yiba,sai daya shiga har toilet din sannan ya dire ta, ruwa ya tara a bathtub me dumi wanda yasan zai mata dadin wanka.
Juyowa yayi yana kokarin jan gown din jikin ta, da sauri ta dafe hannun sa jikinta na muguwar rawa, kamar idanun ta zasu fado take duban hannunsa data damke acikin nasa, wani shegen laushi taji kamar hannun jariri sake damke hannun tai a kokarinta na hanashi abunda yayi niyya.
Zare hannunsa yayi daga nata gaba daya yayi sama da rigar ya zare ta, saurin zagaye hannu tai a kirjin ta daga ita sai wannan gown din sai pant dama can bra bata dame ba.
Kuka ta fashe dashi tana kokarin durkushewa dan kare jikinta, saurin rukota yayi da hanata aiwatar da Abunda take shirinyi, tsam ya dagata yana kokarin sata a bathtub, ganin hakan yasata saurin fadawa jikin sa abazata yaji ta yimasa kyakykyawar runguma, saida numfashin sa ya dauke na wucin gadi, har wata Hajiyaya yaji kansa nayi gaba suka tafi shida ita tsundum suka fada bathtub din tare.
Lumshe idanun sa yayi da Azabar karfi, gaba daya duk wasu kofofin gashi dake jikinsa seda suka bubbude, yanayin yadda take kara mannewa ajikinsa, hakan na kara zafafashi.Yau Imti so take ta halakashi, dan danan idanunsa suka kankance cikin yanayin daya dade beshiga ba, yau gashi ta shigar dashi.
Cikin zafin nama ya mike yana kokarin fita amma idanun Imti ya rufe, dan karyaga jikin ta,sake kankame shi tai, ya salam, ya furta ahankali shikadai yasan abunda yakeji. Ta sake shi ya samu mafita amma hakan ya gagara, abazata ya juyo yafara kissing dinta tako ina, tamkar mayunwacin zaki haka yakoma, tuni Imti ta manta da maganar karyaga jikinta ta koma kokarin kwatar kanta, alokacin da besan wannnan yaren ba saida yaragewa kasan zafi sosai.
Kukanta ne ya fara dawo dashi daga cikin hayyacin sa, kasa motsa koda yatsansa yayi illa furzar da numfashi da yake yi,yarasa kukan ubamme take masa, maza nawa ta rabawa awaje, shi sai yanzu ma ya dawo hayyacin sa, rai bace ya tureta daga jikin sa azafafe ya fita daga toilet din gaba daya jiyayi jininsa har tafasa yake yi.
Aduk lokacin daya tuna yawon Club da Imti ta dingayi yasani yasha ganin ta, sai kowa ya kwanta zata fice ranar karshe ce Ummee ta gano fitar da take harta sashi fita neman ta.
Inya tuna yadda mazan titi suka kare mata kallo na shigar banza data dingayi saiyaji sam bazai iya zama da ita a matsayin mata ba, ya tsani mace mara kamun kai, baya shiri da macen da batasan ciwon kanta ba ko kadan,uwa uba mahaifiya abar so da kauna ga kowane da Nagari, amma ita tasha sa Ummeen ta Kuka Dad yasha marinta a dalilin ta, yasha kama Ummee abayan gidan tana Kuka na bakin cikin da Imti ta cusa mata taya zai so Imti harya kaunace ta.
Tana cin albarkacin Ummee ne, amma batakai wadda ta isa ta rabi inda yake ba, balle harya hada jiki da ita.
Bar baza gashin kansa yake zuciyar sa na sake daukan zafi, tsaki yake ja ajejjere gaba daya haushin kansa ya kamashi,ruwa me sanyi ya dauka saidaya kwankwade shi ya wullar da robar zama yayi yana sauke numfashi ahankali bacin ransa ya fara sauka.
Tunda ya fita Imti ke rusar Kukan abun da yayi mata, atarihinta babu wani na Miji daya taba rike mata hannu saishi, ancemai ne zata zauna dashi, ita bata sonsa bata kaunar sa, bazata sake yadda ya rabu da jikin ta ba seta samu wanda take so zata mallaka masa zuciyarta, da gangangar jikinta bashi ba.
Har yanzu zuciyarta rawa take mata akan wanene shi? mutum ne ko aljan,yadda kirjin ta ke mata zafi hakan ya sata kara fashewa da Kuka, ba karamar azaba suka sha a hannun Ziyad ba, mugu azzalumi ta furta cikin Kuka.
Zubda ruwan ciki tai ta tara wani, daure da bathroom ta fito fuskarta ahade kamar bata taba dariya ba, sai cuno baki take tana bata rai, ko kallo bata ishe shiba ya wuceta toilet din ya koma.
Saida yasake wankan dolen data jawo masa, daure da towel ya fito tana nan inda ya barta a tsaye, kamar dogari. Wuceta yayi ya tsaya gaban mirror, taje kansa yayi ya shafeshi da mayuka masu kamshi.
Ba tare daya kalleta ba ya ruko hannun ta, ko karin fizgewa take wani kallo ya watsa mata ba shiri tabi bayan sa, kujera ya jawo ya zaunar da ita hand raya ya jona saidaya busar mata da gashin ta tsaf, sannan ya taje mata tana zaune tana kallon ikon ALLAH.
Kamar mace haka ya ke mata gyaran gashi, rabashi biyu yayi tamkar baby haka ya daure matashi wasu bit me kyau ya dauka ya daure mata dasu.
Ita kanta kallon kanta takeyi yayi masifar kyau, tsananin kyawunta sake futowa yayi, duka abunnan da yakeyi fa face dinsa a hade take, cream ya shafa mata me matukar kamshi har pawda ya shafa mata tare da 💄 Imti binsa kawai take da kallo.
Wannan akwatin ya kara sawa password ya budeta gown ya dakko mata iya guiwa, sai jins har kasa zai kai intasa ka, sai pant kamar yadda batasa bra shima be dakko mata ba.
Ajiye kayan yayi, wajan ta ya kara dawowa janta ya sakeyi pant din yafara dauka akan guiwowinsa ya duka alamar ta daga kafar ta, hakan tayi gaba daya Ziyad ya gama kwance mata notikan kanta, tunanin ta ya dade da barin jikinta,jins din ya saka mata kwance towel din yayi yai kasa, saurin kauda kansa yayi gown din yasaka mata ba karamin kyau tayi tamkar Queen haka ta dawo sunyi mata kyau kayan sosai, bandana irinta yara yasaka mata aka.
Shikansa saidaya kalleta na sakanni kawar da kansa yayi yana tabe baki, duk abunda yayi mata saboda Ummee ne taci Albarka cinta 🤣🤣🤣kun yadda da hakan kuwa fans anya
Zaunar da ita yayi akan sofa mamakinsa ya kasheta azaune, kayan sa yadauka ya saka, jallabiya ce sabuwa dal ya bareta aledarta, order Abinci ya jawo ya bude sakwara ce da miyar kaji daya ledar ya jawo pizza ce da samosa, turawa gabanta yayi tare dayi mata alamun ta sakko, sakkowa tai turawa yayi gabanta ahakanli ya fara cin abincin sa cikin kwanciyar hankali.
Ya akai yasan tana mutuwar son sakwara, waya fada masa hakan, bata da amsa sa hannu tai tafara ci babu me magana acikin su, kadan yaci bata dameshi ba sam saboda ita dama ya siyo, pizza din yadanci ba laifi tea yake bukatar sha saidai babu anan din haka ya hakura tsam ya tashi daga wajan kan sofa ya koma ya kwanta.
Sosai taci Abincin ta dama yunwa takeji matuka bataiwa kanta fulako ba ta zage taci Abincin ta.
Tana gamaci tamike tattare kayan tayi ta kaisu gefe, bakin bed ta koma zamatai tana wasa da yatsun hannun ta, gaba daya jinta take atakure kwarjinsa yai mata yawa.
Zaman kurame sukai shi yanata danna waya ita babu wayar da zata danna, shiyasa ta zuba tagumi lokaci lokaci tana dagowa tadan kalleshi, seta kamashi shima ita yake kallo, kowa saiya bata rai ya basar.
🤣🤣🤣Anzo wajan
🤣🤣🤣 Mrs Baba Bello Abubakar
...... ✍️✍️✍️✍️
IMTINAN
Written and Narrates
By Kulsoom Ismail Idris
Page 50_51
Har kusan Magari ba suna zaune kamar wadanda aka daure awajan,babu abunda Imti keyi sai zazzare idanu,gaba daya bakinta ya mutu murus,babu batun rashin kunya,ba bakar magana,dama ance wargima waje yake samu.
Shine ya ja musu sallar magariba,haka sallar isha'i. Suna idarwa taga ya mike, kayan jikinsa ya sauya kafin ya maida mask din face dinsa. Uffan bece mata ba yafice baki bude tabishi da kallo,tana san sanin meyasa yake boye face dinsa,wai a takaicema wanene shi,ina ahalinsa suke,su ya kumbo suwane su agare shi,menene dalilin sa na zuwa gidan su matsayin talaka.
Dukkan tambayoyin nan bata dame amsa mata su,dan dole ta hau bed ta kwanta,batajin yunwa sam,gaba daya tunani ya cushe mata ciki,tana wannan sake saken har bacci ya dauke ta.
Ziyad be tashi da wowa ba sai kusan 12 yadda ya fita fuskarsa arufe haka ya dawo, suit din jikinsa ya cire yayi wulli da ita,kayan da yashigo dasu a leda ya ajiye, toilet ya fada ya shafe 30mnt kafin ya fito daure da towel.
Be tsaya wani shafe shafe ba ya dauki kayan baccin sa ya saka,suna da kausri saboda yanayin garin da aka fara busa sanyi,sai Lokacin ya kalli Imti data takure waje daya tana bacci,sai yamutsa face take,alamun ba wani jindadin baccin take ba,kan sofa yahau ya lafe kamar me bacci amma ba baccin yake ba,kome yake tunani oho.
Babu Masjid akusa da yake sa ba da tashi da wuri,karfe 4 dot ya farka,yadan jima akwance kafin ya mike, toilet ya fada alwala ya dauro,sàida yayi nafila ya jima azaune yana Addu'a kafin lokacin Sallar subhi ya shiga,mikewa yayi har inda take kwance,gaba daya gashin kanta ya tarwatse a face dinta,dan jim yayi kafin ya fara bubbuga kafarta ahankali.
Janye kafar tai da nufin sake gyara kwanci, girgiza ta ya sake yi batare da yayi magana ba, ahankali ta bude idanun ta rai bace da tunanin wane dan rainin wayo ke tashin ta,gaba daya ta manta a inda take 4 eyes sukai dashi harara ya watsa mata,da sauri ta rufe idanun ta yanzu sam tsoron kallon kwayar idanun sa takeyi.
Hannunta ya kama ya tasheta zaune,mikar da ita yayi saidaya tabbatar ta tsaya nuna mata hanyar toilet yayi,sunkuyar dakai tai kamar ba ita ba ko kanzil bata ce ba ta nufi hanyar da yake nuna matan,sàida ya tabbatar ta shiga kafin ya koma wajan zaman sa ya Zauna.
Dauro Alwala tai tukunna tafito kanta asunkuye,rannan a hade kamme zai tasheta, zumburo baki take ba tare da tasan tana yin hakan ba,batasan yazo inda takeba jitai ya dalle mata baki da yan yatsunsa,ba karamin zafi taji ba idanunta har cikowa sukai da hawaye,kawar da face dinsa yayi daga kallon ta,tabe baki yayi alamun ko ajikin sa.
Cikin kayan daya shigo dasu ya dakko mata hijab har kasa,ja Musu sallah yayi suna idarwa ta mike da nufin sake komawa,caraf ya rike hannunta batare daya kalle taba,kallon hannun nasa take da yake cikin nata,besake tan ba ya jawota saura kadan ta fado kansa yayi saurin gocewa,occch!! jinta dim akan carpet din dake malale a room din.
Harara ya sake watsa mata,batare da yace komai ba.Hisnul Muslim din hannun sa ya mika mata,kallon sa tai takalli azkar din hannun sa,yaushe rabon da tai azkar,tun tana js,sanda Ummee ke tursasata suyi tare,a lokacin tashayin kuka Ummee ta takura mata,ashe ba takura bace gata take mata.
Hannunta na rawa ta karbi Littafin kurawa rubutun idanu tai. Azkarussabahi wal masa'a,shekaru nawa bata tuna da wannan azkar din ba sake sunkuyar da kanta tai,saitaji tana jin Kunyar mahaliccin ta,ta manta da addinin ta,wace irin yar adamce ita kuwa,dabata tasbihi ga mahaliccinta,bataiwa Annabi Salati,tsahon shekaru dabatasan adadin su ba.
Ayau wanda take ganin makiyinta ne ya tunatar da ita,lallai shidin Masoyi ne agare ta,ba abokin gabarta bane,shidin meson cigabanta ne,dago idanu tai ta kalleshi,shima idanun sa na zube akanta,mayar da idanun ta kasa tai,hawaye na cikowa a idanun ta. Azkar dintake zuciyar ta na sake rauni,wata nutsuwa takeji wadda ta dade bata jita ba,hawaye ke kwarara a fuskarta,sam batasan suna zubaba,batasan kukan me takeba,tasan dai daga kasan zuciyarta yake fitowa.
Cikin mamaki yake kallon ta,kukan me takeyi haka,ko ya takura matane,ya shiga hakkinta,aganinsa wannan aiba takura bace. Littafin ya kalla gaba daya ta jikeshi da ruwan hawaye batare da tasan hakan ba,hannunsa ya mika da nufin jan Littafin sa,dafe hannun tai tana girgiza masa kai alamar ya barshi.
Zare hannun sa yayi daga nata,komawa yayi da baya ya jingina bayansa akan sofa, lumshe idanun sa yayi zuciyar sa na tsitstsinkewa,ya tsani kuka arayuwarsa,musamman kukan mace,yana raunata zuciyarsa.
Yadda take sauke ajiyar zuciya shiya sashi bude idanun sa,sosai ya ware su akanta dama haryanzu kukan take? to wai kukan me take ma?. Ahankali ya mike kasala na mamaye jini da tsokarsa,agabanta ya duka yana kallonta,dago habarta yayi yana karewa face dinta kallon,idanunta sun kumbura face dinta tai ja, tsabar kukan da tasha.
Zare Azkhar din hannun ta yayi ganin tana lumshe idanu alamun bacci yaci karfinta,sunyawa yayi gaba daya ya dauke ta,bed ya mayar da ita, duvet ya jamata shima baccinne a idanun sa,kusa da ita ya kwanta,dan danan bacci ya kwashe su gaba daya.
Be tashi farkawa ba sai kusan 9am, a hankali ya bude idanun sa har time din bacci bebar idanun sa ba,mikewa yayi ganin Lokaci yaja sosai,da azama ya fada toilet,bedau wani dogon lokaci ba yafito kugunsa daure da towel.Har time din Imti bacci take hankali kwance,ragowar ruwan hannusa ya yarfa mata a fuska,sanyin ruwanne ya sata bude idanu,da sauri ta mayar ta rufe danin ba kaya ajikin sa,tabe baki yayi munafuka ya ayyana aransa.
Oya tashi kiyi wanka ko natafi nabarki anan,jin abunda ya fada yasata saurin mikewa kanta akasa,binta da kallo yayi harta gama shigewa,Numfashi me zafi ya furzar agurguje ya shirya cikin suit farare tas,gashin kansa ya gyara ya shafe shi da mai sai kyalli yake da walwali.Ta kwashe kusan 40mnt dama sabon tane in tashiga wanka kamar wadda zata sake fata,sai jan tsaki yake yana kallon tsadaddan agogon dake daure a tsintsiyar hannun sa.
Mikewa yayi cike da takaici zai dubo ubamme takeyi a toilet kamar me nakuda kusan cin karo sukai yana kokarin jan door din tana ja itama da niyyar fitowa,harara ya watsa mata kamar idanunsa zasu fado,angaya miki banda aikinyi ne dazaki shige toilet kiyi zamanki kamar me bacci.
Batace mai komai ba ta sunkuyar da kanta kasa,gaba yayi yana sakin tsaki, karki yadda natafi nabarki, bazan sake waiwayarki ba, saidai kinsan inda dare yayi miki.
Kala batace masa ba gaban mirror ta tsaya,babu abunda ta shafa sai lipstick,gyara gashinta tayi,ya sake kwanciya luf gwanin birgewa,kayan da taga ya dakko mata ta dauka tasaka,gown ce me azabar kyau taji stone sai kyalkyali take,see green ce saita haska rigar sosai ta kwanta ajikin ta duk da bata kamata ba, rolling tai da mayafin rigar,ba karamin kyau tayi ba.
Agaban sa ta tsaya alamar ta gama,yadda batai masa magana ba shima be mata ba mask dinsa ya dauka ya mayar,kallon sa take kamar zatai magana sai dai tayi shiru,sake tamke Fuska yayi baya san wani dogon surutu,karamin akwati ya dauka hannun ta ya rike suka fice daga room din gaba daya,key yasa ya kulle.
Saida ya damka wa ma'ai katan hotel din key dinsu yajata sukai gaba.
Parking space suka nufa da ke cikin hotel din,yaran sa suna wajan,wasu a zaune wasu atsaye kayan jikinsu ma banbatane wannan karan ba kaya iri daya suka saka ba,suna hango shi sukai saurin mikewa. Imti da hankalinta baya wajan sam bata san dasu ba,gaban wata mota yaja ya tsaya.
Tsadaddiyar mota ce sai kyalkyali take tana daukar idanu, budemai back sit daya daga cikin guide din yayi,sai Lokacin Imti ta lura dasu, kallon su take tana Mamakin wadannan su wanene.Ziyad ta kalla daya rufe fuskar sa ruf, bazaka taba tantance ya ainihin kalar sa take ba,sam be kalleta ba,duk da yaji ajikinsa kallonsa takeyi.
Sàida suka daidaita zaman su amotar kafin driver yaja,wani irin ni'im taccen kamshi me tashi amotar,ga sanyin AC daya ratsa sassan jikin duk wanda ke cikin motar."Imti dai sai rarraba idanu takeyi kantafa ya fara daukar charge" ina kuma zasuje yanzu?bata dame amsa mata dan dole ta zubawa sarautar Allah idanu.
Nnamdi Azikiwe International Airport Airport in Abuja, nan sukaiwa dirar mikiya,saida ya mula yasha iska dan kansa har Imti ta fidda ran ko acikin motar zasu kwana,inkiya yayi wa driver da sauri ya fita,bude musu murfin motar yayi Imti ce ta fara fita tana shakar san sayyar iskar datake kadawa,yanayin nada matukar dadi,bataji sanda ya fito ba jin hannunta acikin nasa yasata saurin kallon hannun.
Jan hannunta kawai yayi batare daya ce uffan ba,matattakalar jirgi yake takawa da sassarfa yanayin yadda yake tafiya yasata kamar zata fadi,bata saba da irin wanann tafiyar ba,dan dakatawa yayi jin tana neman faduwa,rai hade ya shiga jirgin fasinja ne birjik aciki sai kawuna da kake hange maza da mata, number kujerar su ya duba suna daga can baya,sàida suka isa wajan zaman su tukunna ya saki hannun ta.
10mnt da hawan su aka sanar jirgi zai tashi kowa ya daura belt,nan fa ake yinta Imti sai kic kici take ta daura belt din amma ta kasa,duk abunda take yana kallon ta,saidaya tabbatar ta gama bawa kanta wahala,tunna ya rankwafo ya daura mata belt din,hada idanu sukai ya wurga mata harara,saurin runtse idanun ta tai,tana mamakin yadda ya iya harara kamar wata mace,bata face tai ta zumburo masa baki kamar zatai Kuka.
Basarwa yayi ya daidaita zamansa,sanda jirgi ya fara kokarin tashi ai Imti jitai kamar zata kifo daga kujerar ta,bata san sanda ta kankame hannayan sa ba,jitake kamar ana jujjuya wa da ita acikin jirgin,dan kallonta yayi ganin idanun ta arufe wani shegen murmushi ya saki,sai maida Numfashi take kamar wadda tai gudun tsere.
Saidata tabbatar Jirgin yayi landing asama, kafin ta cikashi ahankali, tana jingina bayanta ajikin kujera.
30mnt jirgin su yayi Landing akasa,a garin Lagos cunkus dakin tsimma,daya bayan daya kowa ya dinga fita, sune na kusan karshan fita,yadda kasan anzo tarar president haka Motoci suka ciki Airport din,tunda suka hango fitowar sa guide dinsa a hanzarce suka iso gare sa,sara mai sukai tare da kamewa,ko a fuska be nuna alamun yasan da wanzuwar su awajan ba.
Yadda Imti ke binsa abaya haka guiwowinta ke sanyaya,kamar bazata iya daukar gangar jikin ta ba,ta razana matuka da tarin guide din data gani abundaya daure mata kai zagaye sun da sukai kamar wadanda sukai kisan kai wani gumine yake tsatstsafo mata.
Mota aka sake bude masa again hannunta ya ruko,dukkan wata laka ajikinta ta saki sai idanu da take zazzarewa.Reras suka fara tafiya akan layi,cikin tsari suke sharara gudu akan titin Lagos,akalla sun shafe 1hour kafin su isa katafariyar Unguwa Victoria Island estate ne me girman gaske, tundaga farkon da zaka shiga estate din security birjik.
Get din farko baro baro aka akarubuta WELCOME TO THE ESTATE DARMA FAMILY. Karanta abinda ke rubuce da Imti tai, ya sanya jinin jikin ta daina gudu na wucin gadi, hankali tashe take kallon Ziyad,da ya nuna bema san me takeyi ba.
Yanzu ma wasan zai fara kubiyo ni danjin yadda zata kaya.
Mrs Baba Bello Abubakar
......✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 52_53
Jinintane yake neman karewa na tsananin kaduwa da tashin hankali,maimata sunan Darma take azuciyar ta,kamar zautacciya haka ta koma,ganin har wannaan time basu zo get na karshe ba,sun wuce get biyar sai ana shidan suka shiga asalin estate din,kamar yar kauye,ko wadda ta warke daga makanta haka Imti ta koma.
Parking space din estate din cike yake da motoci birjik,saika rantse sàida wajan sàida moto cine,kuma sam ba hakan bane,na mammalaka gidanne,gidajene reras iri daya iya ganin ka,duk da suke iri daya amma wannan yana wane wannan.
Akwai wani katafaran gida atsakiyar estate din yafi kowanne haduwa,tsari da birgewa tamkar ba akasata Nigeria kake ba, security na musamman a get din gidan. Lumshe idanun sa yayi ya tabbatar akwai abunda akeyi agidan yadda yaga parking space ya cika da Motocin yayan gidan da iyayan gidan,dan tsaki ya saki,wanda sàida Imti ta dago ta kalle shi.
Bude masa get akai ya kutsa hancin motarsa a wanann katafaran gidan,shiru harabar gidan sai iska me dadi da take kadawa,shukokine birjik iya ganin ka,jin drive dinsa ya tsaya ya tabbatar masa da sun iso,yakai 5mnt yana kishingide batare da yafito daga motar ba, saidaya ya mula ya zuki iska ya fesar,da sauri wani guide yazo ya bude musu kofa,shine ya fara fitowa kafin ya mikawa Imti hannu,kamar metsoron wani abu ta dora hannunta akan nasa.
Gaba daya jikinta rawa yake har wani Zazzabi takeji kamar zai kamata,dan kallon ta yayi ya tabe baki ko rawar me jikinta yake oho,dage kafadar sa yayi alamun ita tasani,yanayin yadda suke takawa saiya bada wani salo na daban, kamar da gayya suke wannan takun,a zahiri ba hakan bane kowa da tunanin da yake sakatar zuciyar sa,musamman Imti da zuciyarta ke wani irin tsalle kamar zata faso kirjinta.
Akofar wani kayataccen parlo ya tsaya password ya danna wanda bata san taka maimai meya danna ba taga kofar ta bude,kutsakai sukai cikin kayataccen parlon, parlour ne na gasken gaske ba muna parlo ba. Sofa set huduce a katafaran parlon wani kamshine me Matukar dadi da sanyi me shiga jiki,da sanya shauki atsakanin masoya.
Dan Lumshe idanun sa yayi sosai yanayin yake masa dadi,wata budurwa ce kyakykyawar gaske da bazata wuce sa'ar Imti ba ta fara taking steps sam bata lura da mutane a parlon ba,sàida tazo tsakiya tukunna ta lura da su. Ware idanun ta akan Ziyad da yake sakar mata murmushi,sakin hannun Imti yayi data daskare atsaye ita fa kanta yadau zafi matuka gaya.
Da gudu budurwar ta iso gare shi kafin ta rungume shi fuskarta da tsantsar farin ciki,shima rungume ta ya sakeyi yanajin farin cikin ganin ta,dagowa tai tana kallon sa,idanunta na cikowa da hawaye,hannunta na rawa take shafa face dinsa.Hamma D ta furta ahankali,dan ware idanun sa yayi akanta alamar ya amsa,kanta ya shafa Little, murmushi tadan saki.
Magana take shirin yi idanunta ya fada kan Imti data kafe su da idanu ganin kamar da sukai harta baci,kobata tambaya ba tasan wannan kanwar sace,maida kallonta tayi kansa alamar tambaya, wacece wannan Hamma gira ya dage,tare kuke daga mata kai yayi alamar eh,sakin sa tai ta karasa wajan Imti rungume ta tai face dinta dauke da fara'a welcome friend miko mata hannu tai alamun siyi musa baha,ita ma Imti hannun ta mika mata dadan murmushi akan face dinta.
Murmushi suka sakarwa junan su,yana tsaye yana kallon dukkan abunda su keyi,hannun sa Little ta ja wata siririyar hanya sukabi saigasu sun bullo wani katafaran parlo again,sai data sa password kafin kofar ta bude,gaba daya suka shige,shima parlourn ya hadu iya haduwa,babu kowa aciki sai karar AC.Abunda Imti ke ayyanawa iya wannan part din yayi girman gidan su,gaba daya saita kara raina kanta.
Ashe dama Dad dinta ba komaine da shiba saita tuna maganar Fauza,aduk ranar da kika shiga Darma Family ina tabbatar miki tamkar almajira haka zaki dawo, tabbas maganar Fauza gaskiya ce sai yanzu ta gasgata hakan.
Wani kayataccen daki suka shiga tsantsareran daki ne,wani makeken royal bed ne a dakin sai dressing miro sai wardrobe sam ba'a cikashi da tarkace ba,tana tsakiyar gadon akwance kamar yadda take ahakan dai take,ja sukai suka cake a kofar dakin zare hannun sa yayi daga na Little,yanayin takunsa yanayin yadda zuciyarsa take kara bugawa,jayayi ya tsaya aganbanta tamkar me bacci,babu wani abu dake motsawa ajikin ta bayan fitar Numfashinta.
Kamar yadda ya tsaya hakka suma suka tsaya agabanta,tsura mata idanu Imti tayi, kyakykyawar macece ajin farko farace tas hancinta tamkar biro,duk da yanayin da take ciki besa kyanta ya ragu ba,dogon gashin kanta anraba mata shi biyu tamkar karamar yarinya haka ta koma,tsugunnawa yayi agaban gadon hannayan ta gaba daya ya saka a cikin nata,hawaye na taruwa a idanunsa,sabanin Little hawaye gudu yake a kan kuncinta.
Momma ya furta a hankali tamkar mejin tsoron karya tasheta,jin tsayuwar na neman gagararta yasata sunkuyawa ita ma,harlokacin idanunta nakan Momma da batasan awace duniya take ba,batasan me yake wakana ba,in har ta canka dai dai wannan din mamar suce,to meyasa meta,bata da wannan amsar ko kadan, tausayin sune yayi matukar kamata,dama dukiya ba komai take siya ba,ta tabbatar inhar kudi na siyan lafiya da bataga wannan matar akwance ba.
Jitai hawaye ya cika idanun ta,tsam ya mike daga tsugunnan da yake, toilet ya wuce kafin ya fito dauke da wani dan karamin towel fari tas,sai wani bowel dan karami mekyau daya zubo ruwan dumi aciki,zama yayi agabanta.
Zuciyarta ce ta karye,ita da Mahaifiyarta ke kan kafafunta,sam tagaza gane irin ni'imar da Allah yayi mata,takasa kyautata mata dai dai darana daya,maganarta kadai zataji ba hidima zatai agare ta ba,amma ta kasa hakan,ga wasu agabanta,in kudine akwai,izzah daukaka duk suna dashi,amma fata suke,jira suke ranar da mahaifiyar su zata tashi,hidima suke agareta da dukkan kyautatawar su,da jin kansu ga Mahaifiyar su,duk da batasan suna hidima agare taba.
Ina ita data gagara yiwa Mahaifiyar ta hidima anya zataga daidai arayuwarta kuwa? batasan hawaye ke shatata a face dinta ba,imani takeji yana huda kirjinta nadama tana ruftowa agareta,dama dama take maimaitawa azuciyar ta dama baya zata dawo,ta kyautatawa Ummen ta,tanemi Albarkarta.
Jin ana share mata hawaye tadago da idanunta da sukai jajawur, little ce take share mata tana girgiza mata kai,tunaninta tausayin Momma sune yasata zubar da hawaye,batasan tunanin tata Mahaifiyar take ba,tinsanda ta fara kuka ya zuba mata rikitattun idanun sa,sarai yakarance ta ya karanto dukkan fatanta,da nadamarta,nakin hidima ga Mahaifiyar ta,hada idanu sukai ya kautar da kansa daga kallon ta.
Towel din yake kokarin tsomawa a bowel din tai saurin rike dukkan hannayan sa,sam batasan tai hakan ba,alamar ya bata taimata ta nuna masa cika mata yayi,gaba daya yamike ya fice daga room din,yana kokawa da abinda yakeji azuciyar sa,dama Imti zataji tausayin wani mahaluki,betaba zatan hakan daga gare taba sai ayau dinnan,fushinsa akanta saiyaji yana sauka,yana matukar san Momman sa,duk wanda ya sota tabbas masoyine agare shi,wanda ya kita bashi da makiyi tamkar sa.
Little sakin murmushi kawai take tana kallon Imti dadi makura taji shi na abun da takewa Momman ta,amma wacece ita,a ina Hammanta ya samota,shine tambayar da takeyiwa zuciyarta,tare sukaiwa Momma duk wata hidima daya kamace ta,sosai Imti ta goge mata jiki,sabbin kaya kal Little ta dakko,doguwar rigace simple mara nauyi,yanayin ramar datayi yasa basu sha wahalar sa mata kayanba,maida ita sukai suka kwantar kamar yadda take,lallai rayuwa abun tsoro ce abunda Imti ke ayyanawa kenan a zuciyarta.
Thanks you My Friend Little ta furta face dinta dauke da murmushi, murmushi itama Imti tai mata ba tare da tace komai ba.
Mrs Baba Bello Abubakar
.... ✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 54_55
Wani hadaddan building ya shiga ya hadu matukar haduwa wani katafaran parlo ne wanda yagaji da haduwa,kai tsaye bedroom ya wuce, toilet ya fada face dinsa dauke da damuwa, shower ya sakarwa kansa be damu daya cire kayan jikinsa ba,saukar da Numfashi yake ahankali kansa na dada zafafa,wane irin ciwo ne wannan yake damun Momma, babu kasar daba a fitar da ita ba amma ankasa samun bakin zaren.
Ya Allah ya furta cikin raunin zuciya,"ashe dai kowa ka ganshi da akwai abinda ya dameshi, Allah ka yaye mana dukkan damu wowin da suke damun mu"ya jima kafin ya fito shaf shaf,ya zura suit ash da alamu dai yafi ta ammali da ire iren kayan,ba karamin kyau kayan suka yi masa ba,yana cikin daura agogo wayar sa ta dauki tsuwwa,sunan daya gani akan screen din ya sashi dan dakatawa da abinda yakeyi.
Kamar yana gabansa haka ya rusinar da kansa,barka da rana Abba,cikin ladabi ya furta hakan, Murmushi me fadi Abbah ya saki barka Malam Ziyad,ina fatan bawata matsala kuna zaune lafiya kaida Aisha,um yadan murmusa tare da lumshe idanun sa,babu Abbah komai lafiya lau,toya tsofaffin naka suna lafiya,lafiyar su lau Abbah,ma sha Allah Abbah ya furta,Allah yayi Albarka Malam Ziyad kaci gaba da hakuri da halyayyar Aisha.
Bakomai Abbah Allah ya kara girma,Ameen sallama sukai cikin dattako da mutunta juna,ajiye wayar yayi yana sakin huci me zafi, phone din ya sake dauka cover shoe ash yasaka bakaramin kyau yayi ba balarabe sak haka ya fito,gaba daya fita yayi daga part din harabar gidan ya sake fitowa again,wani part ya sake shiga tunda ya doshi parlon yakejin tashin hayaniya,tsaki yaja mahaukatan sun hadu kenan wani siririn tsaki ya sake ja.
Kamshin turaransa ne kadai ya isar da sakon zuwansa,tsit sukai kamar ruwa yaci su,zubawa kofar shigowar idanu sukai ba manyan ba ba yaran ba,kowacce hasashenta ta ina D zai bullo,kare wa mutanan parlon kallo nai akalla sun haura su 50 ahakamma wasu basu hallara ba yawan gaske be dasu a estate din kamar kwari.
Face dinnan kamar hadari haka ya shigo,akasan mako shi yayi wata siririyar sallama wadda ba kowane zaiji meya fada ba.Koma dai sunjin babu wanda ya amsa Acikin su bayan idanu da suka zuba masa kamar zasu cinye shi,sake tamke fuskarsa yayi tamau,kusa da wata babbar mace anan yayi kansa matsuguni,kyawawan gaske ne kamar su sukai kansa Saboda tsabar kyau,naira ta zauna ajikin su,duk wadda kagani sutturar jikinta abar kallo ce.
Wasu hamshakan matane daga gefe,wajan zaman atsare yake,wajan iyaye daban yammata daban,maza daban, yaran mata da ban,sai samari suma wajan zaman su daban.
Wata hamshakiyar matace azaune tai shirim akan wata kujera ta alfarma,tunda ya shigo take wurgamai wata shegiyar harara da narasa ta mecece,tsaf yaga kallon datake masa amma ko da wasa be nuna ya gane hakan ba.Tabbatacce mara mutunci duk nan akwai sa'annin ka da bazaka gaishe damu ba,koda ba Uwar ka da Ubanka aciki,aiko babu su awajannan beci ace kamar ni yayar mahaifinka ba kashigo baka gaidani ba.
Ga kannan Ubankanan duk kana ganin su basu isheka kallo ba,in ya tanka mata kasar wajan ma ta tanka,abun ya matukar harzuka Hajiya yaya,cikin numfarfashi take ci gaba da balbala masifa kamar zata ari baki.Kiyi hakuri yaya wani daga cikin dattijan wajan ya fada,harara ta wullo masa,eh ai dole kabani hakuri tunda dan gold nake yiwa magana,in yayi laifi so kake mubarshi haka sakaka bazamu dinga tsawatar masa ba.
Shiru mutumin yayi dagani dai ransa abace yake,wani daga cikin dattawan ne again ya tabe baki cikin jin haushin Ziyad yake nuna shi da baki,ai kinganshi nan yaya in zaku bangaji juna ahanya bazai nuna ya sanka ba,sai shegen bakin hali da girman kai,gyada kai tayi kaji inda gaskiyar magana take,idan mutum Yayi ba daidai ba anuna masa kuskuran sa,hakkun yaya wani daga cikin su ya kara magana,yana hararar D a fakaice,kaf dinsu kar yake kallon su duk motsin da zakai yasan ma'anar daya sa kayi shi.
Tsagal wata tafara maganar nidai Yaya ayi abunda ya taramu awajannan,tunda wanda akai taron danshi yazo ayi abunda ya kamata,ke Karina banason rashin kunya da dibar Albarka kyabari ai dan karan kaina na zartar da abunda ya dace,ai banga kina shirin aiwatar wa bane shiyasa nai magana,danni time dina alissafe yake,ba zaman kashe zani nake ba,kullum ina jabe ina jiran amiko abani,ah to ni Zuciyata bata mutu ba.
Kowa kunshe bakinsa yayi dariya na cinsa sarai sunsan dawa take wannan maganar,kankance idanu yaya tai zatai magana suka hada idanu da wani hamshakin Alhaji,dagani yaci ya koshi yayiwa Talauci nisa me yawan gaske,da inu yayi mata alamar tai shiru da bakin ta,hadiye abunda tai niyyar fada tai,kafin ta maida kallon ta kan Ziyad dayake danne dannen wayarsa hankali kwance.
Kallon ta tamayar kan Ziyad,kai Ziyad kake kowa wannan zaman akan ka akayi shi,nagaji da wannan masifa,kullum yara na dambe akan ka,kowacce tana kai take jira tsahon lokacin,tunda duk mazan family dinnan ba maza suke kallon su ba,dama ai gida be koshiba bazakaje ka dakko na dawa ba,dan haka gasunan su hudu arana daya za'a Aura maka su,ruwan kane ku hade kanku,ruwan kune kuci gaba da fada atsakanin ku.
Tsayawa yayi da danna wayar da yakeyi,jin wani zance wanda bazai taba yiwuwa ba har abada,dago fararan idanun sa yayi ya zabasu akan yaya wadda itama shidin take kallo,eh kalle ni maganar dana fada haka take babu fashi babu canji,maida kallonta tayi kan wasu yammata da suka gaji da haduwa,waje daya suke zaune amma kowacce hararar yar uwarta takeyi.
Nuna su tai da hannunta ga sunan yan uwanka ne,dama ka sansu ba bare bane,balle kace baka so,ga sunan san kowa kin wanda be samu ba.Surayya,Husna,Safna,Samha kagansu reras dinnan rana daya za'a kawo maka su,sai muga ta karshan kinyin Aure. Ga Uncle din kanan babu kyashi ba komai suka ji suka gani zasu baka yayansu ka Aura,saboda soyayyar da suke maka.
Ga kuma iyayan su nan mata,Hajiya Maimuna,Hajiya Turai,Hajiya Kubrah,Hajiya Suwaiba dan haka saika juya kai musu Godiya,duk wanda ya baka dansa awannan zamanin ai abun ka gode masa ne,ka kuma jinjina masa.
Dago kansa yayi ya karewa wadanda aka lissafo masa daga iyayan nasu maza har matan,wani shegen murmushi ya saki,wanda ya sasu zuba masa idanu, murmushinsa na nufin abubuwa da dama,ko kadan basa son suga wanann mugun murmushin a face dinsa,kallon kallo suka kamayi atsakanin su,wannan dattijon daya fara magana afarko shima murmushin ya saki,yasan wanene D inyai murmushi yana nufin abubuwa da dama.
Gaku ga shinan haka dattijan ya ayyana aransa,kamar bazai ce komai ba,kowa ya zuba masa na majiya jiran cewar sa kawai sukeyi,cikin matukar kaguwa dajin amsar sa,hatta Yaya zuba masa idanu tai,tana mamakin dan iskan yaron nan dayake gara kowa a estate dinnan,yasa yayan su sun koma yan dambe duk adalilinsa,rai bace ta sake kallon sa,wai ya zaka mayar damu yan iska,dakayi magana da karkayi duk uwar su daya Uban su daya,bantaba zartar da hukunci wani ya ketare ba.
Ayanzumma dole kabi abunda nake so,dakatawa tai tana maida numfashi saboda yanayin jikin ta,ita kanta nauyi yake mata,shiyasa tana magana tana haki.Ni din ba kamar su bane akaf cikin ku babu wanda ya isa ya bani umarni nabi,banganshi ba, bakuma a haifeshi ba, har wannan lokacin cikin tsananin tsawa da fusata yake karshan maganarsa,kallon kallo suka farayi atsakanin su face dinsu da tsananin mamakin furucinsa,Musamman Yaya da Uncles din sa,idanun su tamkar zasu fado saboda sakonnin da suke isarwa agare shi.
Gyada musu kai yayi alamar tabbatawa,sai mutum daya shine wanda bazan iya take alfarmar saba, wannan dattijon ya kalla koda be furta ba sun san wanda yake Nufi,sai kuma mace daya wanda bazan take umarnin taba,wata mata yasake kallo,me matukar kamala baza'a kirata da tsohuwa ba amma tadan manyanta kadan,duk estate dinnan sune zan iya karbar alfarmar su,umar nin su,ashirye nake dana aikata komenene matukar daga gare sune.
Amma banda ku,gaba dayansu ya nuna su da hannunsa,cikin tsananin fushi da bacin rai,su Hajiya Kubrah ya kalla da tashin hankali ya bayyana afuskokin su,matukar kun shirya wa yayanku zaman zawarci,to ku aura munsu,nikuma na rantse aranar zanyi musu saki uku uku,bayan nayi kaca kaca da rayuwar su,mikewa yayi duk wanda beji gargadina ba ya aikata abunda yake so,nima ashirye nake na aikata masa abinda naga dama.
Bige rigarsa yayi cikin fusata ya fara tafiya da sassarfa kamar zai tashi sama,wani daga cikin samarinne ya mike afusace,ya kawowa D duka cikin zafin nama ya tare dukan,duka daya yayi masa a damtsen hannun sa ya zuba kara,rike hannun yayi yana me fashewa da kuka,kafarsa yasa yayi masa wani mugun harbi saidaya kusa zuwa karshan parlourn,tsallakeshi yayi yafice babu abunda ya dame shi.
Da gudu Hajiya Kubrah ta iso gareshi,gaba daya ta tattaro shi ta sashi ajikin ta,Kuka ta fashe dashi na bakin ciki da takaici,ya kashemun yaro wayyo na shiga uku,hannu ta dora duka biyun akanta,zagaye shi sukai gaba dayan su, tsananin azabar da yakeji ahannun sa kadai ta ishe shi,wllh yarona ya mutu bazan yadda ba sai munyi shari'a,bazan taba yadda ba,kamar sabon kamu haka Haj Kubrah ta koma.
Matasa sa'annin sane suka cicciboshi parking space suka fita dashi hankali tashe,aka nufi hospital dashi.
Safa da marwa take adakinta hannun ta goye abayan ta,surayya ta kalla da take rusa mata kukan ita sai D zata Aura,rai bace take kallonta,zanci Ubanki Surayya kinsan nawa naka she akan wanann yaron,kinsa gwagwalan danayi asara akan inne momiki soyayyar sa,ko kina ganin babu wani ko kari da nake miki akan haka eh, girgiza kai Surayya tayi nidan Mami ki sake wani ko karin,ni indai ba D ba bazan Auri kowa ba.
Dd dintane ya shigo fakan fakan kamar zai tashi sama ransa abace yake kallon Surayya,ke wai Autan mazane da zaki sa mutane agaba kidinga Kuka kamar ance iyayanki sun mutu,fada mata dai Dd abunda nake fada mata kenan amma taki yadda kamar susa nakeyi mata akunne,toki bude kunnan ki da kyau mungaji da daka tataki, kibarmu musha iska haka,sake fashewa tai da Kuka kamar zata shide,tsaki yaja ya fice yabarsu ita da haj Maimuna da takeji itama kamar ta fashe da kukan.
Uhm lallai akwai kura ana wata ga wata.
Mrs Baba Bello Abubakar
......✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 56_57
Samha kodai kimin shiru kidaina kuka ko na zabga miki mari wllh,duk mazan estate dinnan ki nacewa mutum daya, kamar Autan maza nagaji da bata lokaci na akan sa,ko ance miki saboda in wahalta akansa na duro duniya,cewar Haj Suwaiba kamar zata rufe Samha da duka,sakkowa daga kan gadon Samha tai rike kafafun Mom din ta tai,nidai Mom ina son shi ahaka,kefa kikamin alkawarin zaki samo min shi kota Halin kaka.
Kallonta Haj Suwaiba take kamar ta samu TV ayyanawa take wannan wace irin kaddara ce ta fadawa yarta,san makiyanta dan Momma makiyiya ce agare ta,ya isa haka Samha kiyi shiru indai kina sonsa babu abunda bazan yi miki ba,ko ina za'a je adawo babu wacce zai Aura saike,baki da Miji sai shi,kiyi shiru abinki babu inda bazan shiga ba wajan cikar burin ki,share hawayanta tayi tana sakin murmushin farin ciki.
Ransa bace ya koma part dinsa,zaiga wanda zai masa Auran acikin su,sai huci yake shikadai kamar zai hadiyi zuciya haka yakejin wani daci azuciyar sa,yasan duk me suke hari,kaf din su badan Allah suke son ya Auri yayan suba,dan dukiya ce,ya rasa ina zasukai kudi,me zasi dashi,duk abunda suke dashi sun raina abun hannun sa kadai suke hange,gaba daya basu da wadatar zuci,sunriga sun sawa zukatan su kwadayi.
Bude kofar da akai be sashi ya juyo ba, yasan babu wanda zai shigo wajansa sai su,suka daine suke da wannan lasisin,ahankali tatako gare shi,Hajiya Zainab kenan mace me dattako da sanin ya kamata,mace me wadatar zuci babu ruwanta da abun hannunka,mace me karamci da mutunci,mace me maida bare nata,mai taimakon wanda bashi dashi,iyakar iyawarta zata tsaya akan matsalolin ka.
Hannayansa gaba daya ta kama,dago idanun sa yayi da suka canza kala har wannan time din basu dawo dai dai ba, murmushi ta sakar masa cike da so da kauna,kulawa irin ta mahaifiya take bashi,zama tai akan sofa kusa da ita ta zaunar dashi.
D ahankali ta ambaci sunan sa,sake kwantar da kansa yayi akafadun ta,yanajinta kamar Momman sa,ita din me hidimace agare su,mesan ci gabansu ce akowane Lokaci,Mammi ya furta cikin so da kaunarta,dan murmushi ta sake saki,meyasa kake da saurin fushi,meyasa bazaka dunga danne zuciyar ka ba,sudinfa iyayan kane,kamar yadda muke iyaye agareka.
Yaya fa tanajin ciwo da dacin kinjin maganrta da kake,kadaure mana Ziyad,kadaure kayi musu biyayya zakaci riba agaba,dago kansa yayi yana kallon ta,gyada masa kai tayi alamar tabbatar da zancan ta,kasa yayi da idanun sa,inama zai iya daya furta mata abunda ke zuciyar sa,saidai bazai iya din ba,yana matukar Kunyar Mammi tana da wata daraja,girma da kima agare shi.
Sarai ta karance shi akwai magana abakinsa,amma miskilancinsa bazai sa ya furta hakan ba,nasani akwai ciwo amma kadaure Ziyad zakaci riba gaba kadan,suma dinga yan uwanka ne,kuma iyayanka bazasu zaba maka abunda zai cutar dakai ba,kallon ta ya karayi asanyaye,Mammi ya sake furtawa yana hadiye wani abu me matukar daci da ciwo a makoshinta.
Banda wannan alfarmar kifadi wata Mammi,kallonsa tai baze taba karbaba haka ta ayyana azuciyar ta,bakomai Ziyad bazan taba tirsasaka akan suba,kafini sanin su wanene su agare ka,kasake tunani da zuciyar ka,kabata space din da zata huta,kayi tunani mekyau dan Mammi, murmushi yadan saki, fushinsa na zagwanyewa kasantuwar sa da ita,nasashi afarin ciki,yana fata da buri Momma ta farka,tadawo lelensa,kamar yadda ya saba.
Kataso lunch is ready gyada mata kai yayi alamar zasu zo kamar yadda ta bukata, phone dinsa ya dauka number Little ya laluba,ring daya tadaga.Hammana sàida Imti taji kirjinta ya buga furta sunan sa kadai na razana duniyarta da jijjiga tunanin ta,is ok taji ta furta kallonta tayi ta sakar mata Murmushi,dan zaman da sukai da Imti ta tabbatar haka dabi'ar Little take baka taba ganin fushi ko bacinrai a face dinta,hannunta kawai taja batare data ce uffan ba.
Ficewa sukai daga part din Momma baki daya,wani part na daban taga sunnufa tana Matukar mamakin girman gidajan estate dinnan,kamar ba kudi akasa aka siya ba,girman nasu harya baci,akofar parlon suka tsaya password tasaka kafin kofar ta bude,abunda Imti ta lura dashi duk estate din haka yake kowace kofa saika saka password kafin ka shigeta.
Aljannar duniya Imti ta furta ahankali,shima hadaddan parlone kujeru set biyu ne a parlon royal sun masifar haduwa,ga wani kamshi me matukar dadi dayake tashi me kwantar da Zuciya,tunda suka shugo mammi ta zuba musu idanu,mamaki ne karara aface dinta wacece wannan,dan sam batasan da zuwan Imti cikin gidan ba,kallon Ziyad tayi wanda ya basar kamar besan abunda takeyi dinba.
Hakan da yayi ta tabbatar yasan da zuwanta yasan wacece,kallon Imti tai wadda taja ta tsaya tana wasa da yan yatsunta,ganin kallon da Mammi take mata,dan Murmushi Mammi ta saki taho mana, Little ce taja hannunta,gaba daya kafafunta rawa suke,ta rasa meyasa Ziyad yake mata kwarjini wanda ada beyi mata shiba,kamar me koyan tafiya haka tafinga bin little abaya,kujera ta jamata,kamar me tsoron wani abu haka ta zauna a darare.
Dan satar kallon sa tai,hankalinsa sam baya kanta,abunda bata sani ba tsaf yake ganin ta,tasake wanka acikin kayan Little tasaka pakistan ne pink color sun matukar karbar jikinta sosai sukai mata kyau,kamar ta Allah haka ya ayyana a zuciyar sa.Dad ne ya sakko daga sama idanunsa akan ta ya fada,wannan dattijan ne da Ziyad yake matukar ganin girman sa,Dd Yisuf kenan Miji ga Hajiya Zainab wato Mammi.
Kallinsa ya mayar kan Imti sam be santa awannan Estate dinba,kallonsa ya mayar kan Ziyad kansa na kasa balle yayi mai tambayar wacece,dan murmusawa yayi ya samu waje ya zauna,Barka da fitowa Dad Ziyad ya furta cikin girmamawa,bana bukata rike kayarka,dan kallonsa Ziyad yayi yadan murmusa,maida kallon sa yayi kan Imti da gaba daya takejin ta atakure jinta acikin mutanan da bata saba rayuwa ba,harshanta na rawa ta furta ina wuni.
Murmushi me fadi Dd Yusuf ya saki,lafiya lau Doughter dan kallon sa tai, Murmushi yayi mata,yana da kirki ta ayyana aranta,Mammi ta kalla da nufin gaisheta ina miko gaisuwa Mammi ta furta cikin yar Dariya,sai taji kunya ta kamata,na tundata zauna bata gaishe da ita ba, shiru tai tana wasa da yatsun hannun ta, Little ce tai serving din su.
Sam kasa cin abincin tai jinta take atakure,dan kallonta yayi cin abincin sa yake cikin kwamciyar hankali,yayi missing din girkin Mammi sosai,kasa yayi da murya inzakici kici Malama wane surukinki anan,babu wanda yaji abunda ya fada sai ita daya fada domin ta,dago idanu tai tadan kalle shi hada idanu yayi ya dage mata gira,saurin saukar da kanta kasa tayi,bata sake dagowa ba har suka kammala cin abincin.
Mikewa Little tai itama ta mike,ah ya zaku mike ina zakuje,year dariya Little tai nasamu abokiyar hira yanzu,rike haba Mammi tai au nizakiyiwa tawaye,zaki dawo kisameni inta tafi,nima alokacin zance bansan zan can ba,yar dariya Little tai a'ah Mammi muna tare ai,be kamata aji kammu dake ba,ai tunima anji,yar dariya suka saki hannun Imti taja suka fita.
Binsu da kallo Mammi tai kafin ta dawo da kallonta kan Ziyad,wacece wannan Ziyad,shiru yayi kamar beji tambayar da take masa ba,Dd ne ya kalleta sarkin tambaya Amanarsa ce to sai ki kulamai da ita yadda ya kamata,dan dagowa Ziyad yayi yanai masa kallon mamaki Amanarsa,kalmar yake maimaitawa,basarwa Dd yayi ya mike,tsam yabar wajan suka.bishi da kallo,kallon juna sukai kowa yana neman karin bayani,da sharhi akan maganar Dd Yusuf.
Sanin baida abunda zai gayawa Mammi tsam ya mike batare da yace uffan ba,barin part din yayi gaba daya binsa da kallo tai zuciyarta na shiga nazari,bata da zabin daya wuce tamike ita ma.
Tun daga wannan rana Imti ta daura niyyar kulawa da Momma,safe da rana da yamma bata gajiyawa da hidima agare ta,hakan saiyasa ta siye zukatansu batare da sun ankara da hakan ba,intanai wa momma hidima tanaji kamar Ummeen ta,hakan yana rage mata radadi dajin zafin zuciyarta da tuhumar da take yawan yiwa kanta,nakin tsayawa ta kyautatawa mahaifiyarta.
Da dukkan zuciyarta,jikinta da lafiyarta takewa Momma hidima,hatta ga Mammi da Dd Yusuf ta siye zukatansu,tamkar ba Imtinan dinnan ta baya ba,me tsananin girman kai da dagawa,me tsananin Alfahari da jiji dakai wannan wata sabuwar Imti ce,me Matukar tausayi dajin kai,mejin cewa talaka a yanzu shima mutum ne kuma abun a tausaya masa.
Takoyi abubuwa da dama awajan Mammi da Little,Mammi tana da ilimin Addini matuka,awajanta suke saukar karatu,tuni Imti ta sake tabbatarwa tai babban kuskure abaya,nakin zama tayi amfani da damarta, Little ma na koyar da ita abubuwan da bata sani ba,saigashi dan danan tazama wata mutum ta musamman, azkar baya wuce ta akowane hali harshanta baya rabo da ambaton Allah.
Wani zubin tanayi tana Kuka,ita ko wace Irin asara ta tafka abaya,intana karatun Alkur'ani Nishadi take ji,wanda bata taba jin makamancin Irin saba,yanzu hankalinta akwance yake tana waya da Ummeen ta da Dad dinta awayar Little,koda wane lokaci Ummee nasiha take mata ta kyautatawa mijinta,haka Dad ya sakko ya daina hure mata kunne ko da yaushe fatan Alkhairi yake agare ta.
Yau tsahon satinta 3 agidan batare da kowa yasan da zamanta a estate din ba,bata zuwa ko ina,haka Little dama bame san yawo bace,daga gida sai makaranta,yanzu ko ba zuwa take ba tana hutu.
Suna zaune bayan sun gama karatu,Imti anjima zaki rakani mugaisa da yaya,kallon ta Imti tayi wacece yaya,yayar Abban muce,bazani ba,kallonta Little tai meyasa,hakanan banason mutane da yawa,dan murmushi little tai aikuwa ya zama dole ki hadu dasu,gwarama kisaba dasu tun yanzu,harda yammatan Hamma acikin su wadanda ake shirin Aura masa kwanannan,batasan meyasa taji kirjinta ya doka da mugun karfi ba,kamar yana barazanar tsagewa,saidata dafe kirjin tatafi da baya ta zube akan bed,cikin mamaki Little ke kallonta menene, girgiza kai tayi amar ba komai,har Lokacin bata cika kirjinta ba.
Jitake kamar gobara ake acikin sa.
Uhm Uhm Uhm badai nayi shiru da bakina.
Mrs Baba Bello Abubakar
......✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail
Page 58_59
Rai bace Yayah take zagaye hadaddan palon ta,ranta na sake suya da kuna,wane irin yaro ne wannan da shegen kafurin taurin kai,shikadaine wanda yake ketare umarnin ta,tarasa yadda zatai dashi,yaro kamar aljani,kai tana tantamar ma in D mutum ne,takadirancin sa yayi yawa,ga tsaurin idanu kamar shine gaba da kowa a estate din.
Kallon su tayi kowa yayi shiru yana jiran ta cewar ta,Haj Kubrah,Haj Suwaiba,Haj Maimuna,Haj Turai,sai Dd Bashir,Dd Sa'id,Dd Idris,Dd Kabir,sune suka zuba mara idanu kowa ka ganshi ransa abace yake,kallon su ta sakeyi akaro na barka tai gaba daya kanta ya kulle kanta ya dauki charge.Haj Turai ce ta numfasa tare da muskutawa daurin dan kwalinta ta kawo gaban goshi,ni abunda nake so D ya Auri Safna dan itace tafi dacewa dashi,kuma yadda ban zauna da kishiya ba haka 'yata bazata zauna da kishiya ba,ba daya ba har Uku bazata sabuba,kare maganar tai tana watsawa sauran harara.
Wani banzan kallo suke watsawa Haj Turai,kallon baki isa ba kinyi kadan kinyi tsararo,haka mazan ma ki galla mata harara kamar zasu rufeta da duka dan jin takaicin maganar ta.Kwafa Haj Kubrah tai zancan banza kikeyi Turai duk nan ki kalle mu babu matsiyaci acikimmu,da kike cewa yarki bazata zauna da kishiyoyi ba ance miki muma kaunar hakan muke adai hadu ataimaki junane kawai.
Koba haka ba ta kalli sauran da suka zubo mata idanu,kwarai kuwa batun san rai ma babu shi,dole suma yaran su hade kansu su zauna Lafiya,fatammu dai asamu ayi wannan Auran,shine kwanciyar hankalimmu,cewar Haj Suwaiba da take hura hanci.
Shiru aikai na wani Lokaci.Numfasawa yaya tai dukkan ku naji kalamanku,kai kuma Bashir me zakace,gyara zaman sa yayi,aini yaya bani data cewa abunda kika yanke shine abunda kowa zaibi,murmushi ta saki tana matukar so taga ambata girmanta an damka mata wuka da nama yawwa to ananne fa zatai ma abunda kake so kaima.
Zasu sake magana kenan suka shigo Little ce agaba Imti na bayan ta,kamar ruwa ya cisu haka suka zubo musu idanu,ido bude suke kallon Imti da tunanin wacece wannan,sam bata lura dasu ba saidata zo tsakiyar parlourn,tukunna ta lura da mutanan parlourn.
Yaya ma ba'a barta abaya ba idanunta kamar zasu fado take kallontà,rigar shadda ce ajikin ta dark pink dinkin sinigal ba kara min kyau kayan sukai mata ba, Little ta kashe mata wani shegen dauri gashinta na tsakiyar daurin yana reto,sarka da dan kunne makale a kunnan ta hannuwanta sanye suke da zube da awarwaro Masu matukar tsada,duk a yan sakanni sukai mata wannan kallon.
Kallon kallo suke atsakanin su,zuciyoyin su fal tambaya wacece ita? basu da zabi bayan suka maida kallon su kan Little da take sakin murmushi,dan ita sam bata lura da kallon da sukewa Imti ba kamar sun sami TV.Tana tsaye tana wasa da yatsun hannun ta da suka sha rani,duk adazu Little tai mata.
Ta tsani kallo matuka kuwa tsaf ta dinke fuskarta,kamar bata taba dariya ba,kamo hannun ta Little tai suka rasa kan sofa,barka da yammaci yaya, Little ta ambata babu wata damuwa a face dinta da wuya kaga bacin rai a face dinta,da kyar yaya ta hadiye wani abu me tauri daya tsaye mata amakoshi,duk adalilin ganin Imti,da kyar ta amsa da yawwa,juyawa tai kansu Haj ta gaida su haka Uncles din ta dake wajan.
Kallon Imti tai da bata da alamun gaida su cikin rada take fada mata sis kigaida Uncles dimmu,dagowa tai still ita suke kallo,dan murmushi ta sakar musu yan yatsanta biyu ta daga Hiii ta furta kamar ba itace tai furucin ba,yau munga shegiyar Yarinya yaya take ayyanawa a zuciyarta,ke Little wacece wannan din da hatta shigo estate dinnan ba tare dana sani ba.
Dan murmushi Little ta saki Hamma ne ya kawo ta,dif wuta ta dauke musu na wucin gadi,Dd Kabir ne cikin kaguwa yake fadin kina nufin D ne ya kawo ta,gyada musu kai tayi alamar tabbatar wa,sake zuba mata idanu sukai kirjinsu na lugudan faduwa da suka rasa ko namene.
Cike da takaici Haj Turai take kallon su,Aidole yaki yadda yayi Aure tunda ya aje me biya masa bukata,ina kuwa zaiyi Aure,zuba mata idanu sukai suna auna zancanta a ma'auni na hankali da tunani,tabbas haka zancan ta yake,gidan ubanwa ya samo wannan tsaleliyar budurwar, Little datai sak tana kallon su rarraba zantukan su takeyi,medebe masa kewa me suke nufi,kallon Imti tayi da ranta yayi matukar baci da abunda suke alakantata dashi.
Dago idanunta tai ta zubesu akan Haj Turai data gama Numfarfashi yanzu, idanun ta har wani maiko sune saboda bacin rai,kalleni mara kunyar yarinya koba gaskiya na fada ba,shakka babu babu ma wata tambaya abokiyar hutawar sace,shiyasa gakinan ko ina ya cika bul bul ajikinki.Tundata fara magana Imti ke kallonta,inama zata iya data maida mata da martani,amma bazata iyaba.
Datasan hakane da bata biyo Little ba Shiyasa tun farko taji zuwan be kwanta mata ba,ashe cin mutuncinta za'a yi harda mummunan kazafi,kamar an kirasu suka dinga shigowa daya bayan daya,idanun su baya sauka akan kowa sai Imti wadda ta sunkuyar dakai harwata kallar bakin ciki ce ta taru a idanunta.
Gaba daya yammatan kallon ta suke,da wani irin yanayi dasu kansu basu sani ba,hakanan sukaji sunajin zafinta matuka gaya tunkan su san wacece ita,iyayan su mata suka kalla danneman karin bayani,ajiyar D ce kafa da kafa ya kawota estate dinnan tsabar rashin gaskiya babu wanda yasan da ita,sai yanzu da Allah yayi tonuwar asirin su tafito muka ganta.
Cikin jin zafi Haj Maimuna takai karshan maganar ta,zuba mata idanu suka sakeyi wutar masifa da kishi na ruruwa azukatansu,ganin irin hadaddiyar yarinyar dake gabansu wai D din sune yazo da ita,tashin hankali ma kenan,harwani daci suke ji azukatansu,musamman Surayya datake da azababban kishi,zuciyarta har tururi take.
Tana zaune a inda take ko motsawa batai ba dago idanun ta tai dasukai azabar ja sabo da bacin rai,zubasu tai akan jama'ar parlon da batasan sun taru hakaba,akalla sunkai su 30,kuma kowannen su idanun sa na kanta,sake tsuke face tai.
Kamshin sane ya sanar da su zuwansa,saida gabanta ya fadi aduk sanda zataji wannan kamshin,tasan yana daf da zuwa inda take,suma sak sukai suna kare masa kallo,yaci kananan kaya sun matukar amsar sa,sunfito da kyawunsa matuka,shanyayyun idanun sa yakebin mutanan parlourn da kallo,idanun sane ya fada akan ta tayi masifar yi masa kyau ba kadan ba,ta matukar tafiya dashi,amma bazaka taba gane ita din yake kallo ba.
Maida kallon sa yayi kansu Yayah da suka zuba masa idanu da ganin yadda zaiyi dan ankamashi dumu dumu,amma me babu wata damuwa a face dinsa,takowa ya farayi har tsakiyar parlourn sai dayaje tsakiya yadan dakata ya zuki iska ya fesar,ya mula dan kansa.Kallon su ya karayi sun masifar bashi dariya ko motsi basa son yi kamar wadan suke kallon namun daji,yadda in sun motsa za'a wuce wani wajen ba tare da sun gani ba, haka suke kallon sa sai su kalli Imti.
Yana kara kusantota zuciyarta na sake karfin bugu, kamar yadda zukatan su ke dokawa aduk sanda ya kara taku zuwa gareta,kai tsaye wajanta ya nufa batare da kowa ne tunani ba ya duka agabanta da lallausan murmushi akan face dinsa wanda ya narka zuciyar Imti,yasa taji kanta ya kara wani irin girma,wani kambu take ganowa akanta an rubuta QUEEN (uhm kunjifa Imti tana neman ruftawa da yawa).
Gaba daya hannayansa ya zube akan cinyoyin ta,jinin jikintane ya nemi daina aiki,har dan runtse idanun ta tai abazata hakan yazo agareta,kai hatta little bude idanunta tai akan Yayan nata,da tunanin anya shine.
Basu gama shan mamaki da shiga rudani ba saida yajuya alamu yayi mata tahau ya goyata,wani kallo tai masa wanda ita kanta batasan ta iya ba,kallo ne menarka zuciyar wanda akayiwa,tako ci nasara ba kadan ba.Dago idanunta tai ta kalli mutanan parlourn kamar an dasa su haka suke tsaye kamar sun rasa tunanin su na wani Lokaci,kodan ta bakanta musu rai,ta sake dilmiya su atashin hankali daraf ta dare bayan Ziyad, murmushi ya saki ganin wasan sa zai tafi yadda ya kamata, tunda 'yar wasan ta bada hadin kai.
Tabashi Mamaki matuka gaya,tayi matukar birgeshi yadda tai saurin amsar tayinsa,ba tare data yar fashi ba.
Zagaye hannayan ta tai a wuyansa,mikewa yayi kamar wanda yake tsoron karta fado daga bayansa,sake kankame shi tai hankalinta kwance,rufe idanun ta tai dan tabbas tasan kallon da zata fuskanta matukar ta bude idanun ta,hannu ya mikawa Little datai mutuwar zaune kamar sokuwa haka tasa hannun ta anasa, mikewa tai ya jata suka fara takawa dan barin parlourn.
Tashin hankali hatta Yayah mikewa tai tsaye dan ganin wannan tabargaza da aika aika,su Safna kuwa ai zuciyoyin su tsayawa sukai da aiki,dan bude idanun ta tai daidai sun kawo wajan su Safna,ido daya ta kashe musu cike da tsokana,gira ta dage musu alamar yadai,kara kashe musu ido tai tana sakin wani mugun murmushi sake kwantar da kanta abayan sa.Tamkar jaririyar datai kuka tanemi taimakon mamanta haka ta sake lafewa ajikinsa.
Idanun su akan su har suka bacewa ganin su,tabbas D yayi matukar shammatar su,ya dagargaza zukatan su,yayi wasa da tunanin su,yayi fata fata da kwanciyar hankalin su,ya dasa musu razani da dimauta wadda basu taba zatan zasu shiga adalilin sa ba,sun doku iya dokuwa mazan su da matansu,hannayan su dafe da kirjin su kamar wadanda wata larura ta kama.
🤣🤣🤣Anayi munajin dadi lallai D ya cika Namijin Duniyah.
Wasan ya matukar kayar dani lallai Imti kanta ya fara kawo wuta.
Fans sainaga comment dinku, da sharhin ku, akan wanann page din.
Taku ko yaushe.
Oum Nihla
......✍️✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 60_61
Yadda ya tafi ya barsu haka sukaci gaba da tsaiwa kamar andasa su,abin ya masifar dukan zuciyar su,ya shammace su,ya goge musu hadda iya guga,jabar yaya takoma ta zauna,gumin tashin hankali na tsatstsafo mata,wace shegiyar yarinya ce wannan,koma yar gidan Uban wanene dole ne tadauki mataki akanta,tana daf da cika burinta tana neman bata mata aiki.
🤔🤔🤔Tofa wane buri Yaya take dashi ita kuwa.
Kukan Surayya ne ya dawo dasu suman wucin gadin da sukai,kallon su suka mayar kanta,kamar zata shide take rusar Kuka,babu kakkautawa,ko wace yar iskace wannan taci alwashin saita bar estate dinnan,babu wanda yace mata kala kowa ransa ajagule yake.
Haj Kareema ce ta buge zanin ta tare da jan wani dogon tsaki,ni bamga abun tada hankali ba,rayuwar sace fa,kowa yana da right din zabar Abunda yaga ya fiye masa,amma dan jarabar naci lallai sai kun cusa masa yayan ku,nina rasa wannan masifa da bala'i,kwadayi dai mabudin wahala, kyalkyale wa tai da dariya ranta fes ita wannnan abu Yayi mata dadi ba kadan ba.
Afusace Dd Bashir ya mike yana nuna ta da dan yatsa cike da bacin rai kamar zai kifa mata mari, Kareema ki shiga hankalin ki,nagaya miki kishiga taitayinki,kinsanni sarai bani da kyau zakiyi ta igiyar Auran ki yanxu,tsaki taja me mugun tsayi,to Bashir danka sakeni sai akayi me,jinake in mazane ga sunan suna yawo akan titi,masu wadatar zuci ma,bakai wanda baida Godiyar Allah ba,wllh kar nake kallon ka,kabini ahankali matukar baso kake kwabarka tai ruwa ba.
Nafika tashan ci,nafika rashin mutunci,yadda asirinka yake lullube kabarshi ayadda yake,Jayayya da Kareema dai dai yake da futowar ka rana sintir wllh,harara ta watsa masa,bagazan bagazan tafice daga parlon baki daya,binta sukai da kallo,kafin su maido da kansu kan Dd Bashir dayake ta muzurai.
Waskewa yayi ya zauna,yana tsinewa Kareema azuciyar sa,dole yadauki mataki akanta,bazai zuba mata idanu tanai masa cin kashi ba,na sallami ko wannen ku,Yayah ta ambata zuciyar ta na tafar fasa kamar zata babbake dan bacin rai,daya bayan daya suka dinga fita kowa zuciyar sa babu dadi,hannun Surayya Haj Maimuna taja ranta amatukar bace.
Sake lafewa tai abayan sa,har wani bacci taji yana neman daukarta,tsakanin part din Yayah da part din su dayar tafiya,kamar be dauki komai ba haka yake jinta abayan sa, Little dai ambata aiki saita kalli Imti,sai juyo ta kalli D ganin tayi Landing abayansa babu Abinda ya dameta kamarma bacci takeyi,bakin ta fal yake da Magana amma babu damar yinta,Hamma ya dinke face tsaf kamar bashine yagama sakin murmushi ba.
A parloun farko ya sauketa akan sofa,da gaskefa Imti bacci takeyi saidaya direta yasan da baccin gaske takeyi,sake gyara kwanciyar ta tai tana sauke numfashi ahankali,sam kin hada idanu yayi da Little yasan tana da tarin question be shirya amsa mata ko daya daga cikin su ba,barin wajan yayi gaba daya tabishi da kallo,maida kallon ta tai kan Imti da take baccinta hankali kwance,tsura mata idanu tai tinani barkatai yana cika zuciyar ta.
Da kyar yakai kansa daki yana dana sànin goyata,gaba daya jinta da yayi abayansa ya matukar motsashi,ya barowa kansa aiki babba,tsaki yakeja tanacan babu Abinda yadameta,ashe taimakon ta yayi ma dama bacci takeji,ya taimaketa shi kuma ya cuci kansa, wardrobe din jikin bed dinsa ya janyo,magani ya balla ya kora da ruwa ko zaiji relief din Abinda yake damun sa.
Baya yayi ya kwanta yana sauke ajiyar zuciya,dan murmushi ya saki sànin bom din daya hada agidan,ya tabbatar ya katse musu jin dadin yau,babu wadda zatai walwala daga mazan har matan,yau ya koyar dasu darasin da basu taba zatan ya kware akai ba.Ya canka dai dai kuwa dan har yamma babu wanda ya iya kora koda ruwane a makoshin sa,bayan rigima ta tashin hankali da yayan su sukasasu gaba sunayi,ga damuwar su ta karan kansu da take damun su.
Wanann fa shine ana wata ga wata,idanun Husna sun masifar kumbura tsabar kukan da tasha kamar ance uwarta da Ubanta sun hadu sun mutu arana daya, Haj Kubrah ta kasa zaune ta kasa tsaye bacin ranta sake hauhawa yake akowace dakika,karar bude kofar ne ya ankarar dasu akwai me san shigowa room din,zubawa kofar idanu sukai suna kallon kofar,hannun sa nannade da bandeji an rataye mai hannu a wuyan sa,kaida ganin sa kasan yana jin jiki.
Zuba masa idanu tai tsanar D na sake samun gurbi azuciyarta,da kyar ya zauna yana kallon Mom din tasu, ahankali tatako inda yake zaunen Amar ta ambata kamar zata fashe da Kuka,kallontà yake cikin jin zafi da radadin ciwo,kautar da idanunta yayi daga kanta yana hadiye wani abu medaci da kuna azuciyar sa,tsanar Ziyad kara ruruwa tai a zuciyar sa sanadin karya shin daya sake yi,gaba daya ya tsayar masa da rayuwa ya hanashi walwala.(matashin daya kawowa D duka ya murde hannun na tabbatar yanzu kun gane shi).
Mom bazan taba barin saba,saina rama fiye da Abunda ya yimin,taya kenan Amar tayaya zaka Iya karawa da D bakaga irin lahanin da yayi maka ba,sanadin sa fa kake azaune,tsahon 3weeks baka zuwa ko ina,wanda yayi ma wannan raunin kana tunanin zai barka ne inka sake shiga gonar sa,shiru tai zuciyar ta na tafarfasa,dan murmushi Amar ya saki ni zan iya Mom zanyi masa Abunda harya mutu bazai goge daga zuciyar saba.
Zuba masa idanu sukai suna mamakin me zaiwa D haka,kallon sa Husna tai karka sake ka tabamun miji bazakaji ta dadi ba,kasan Allah wani abu yasame shi kai zannuna,harbi ya kawo mata da kafa da sauri Haj Kubrah ta tare, àah ya zaka huce haushinka akan yarinya ta,kuje can ku karata kaida D din amma karka sake dukarmun yarinya.Shiru yayi be besake tanka musa.
Kafin dare yayi jikin Yayah ya dumame da zazzabi me zafi,saboda yadda ta sawa ranta damuwa,ta hana zuciyarta sakat da tunani,yadda tashiga tashin hankali sai jinin yayi mummunan hawa,Abunda yasa su kara daukar dumi kenan,suka kara kullatar D da Imti,wadanda basu ma san sunayi ba,saida akayi mata allurar bacci kirjinta sama da kasa yakeyi kamar wadda zata shide.
Su Haj Kubrah iyayan cusa kai sune agaba,duk sanyin AC nan harwata firfita suke sake yimata,tare da fadar bakaken maganganu akan D din, Mammi koda taje dubo Yayah tasha bakar magana da habaici,duk da batasan musababbin ciwon ba saida taje tatsinci labarin awajan su,shiru tai ba tare data tanka musu ba,dan bata da abun fade din,bata da lokacin da zata bata akan su,tasan halin su ciki da waje.
Haj Kareema ce tashiga fadan cike dajin zafin su,duk da ba dasawa suke da Mamma ba,amma basa zaman gaba atsakanin su,suna matukar girmama junan su,shiyasa tasu tazo daya da Haj Kareema macece wadda bata son raini,batason wargi ko kadan,duk wanda ya takata saita tatakashi,shiyasa suke matukar jin shakkarta,ba suba hatta Yayah najin shakar Haj Kareema,abun ko ba karamin bata mata yake ba.
Atsarin Yayah tafi so ka bita kamar rakumi da akala,duk inda tajaka kabita kawai,yawwa anannne zaka zamo na hannun damanta,Abunda su Haj Kubrah suka gane kenan suka bita yadda take so,sai suma take musu abunda suke so.
Mrs Baba Bello ABUBAKAR
.......✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 62_63
Saida Yaya tai kwana Uku tana jinya,jinyar jiki data Zuciya,da sakawa da kwancewa,har wannan kwanakin babu wanda ya sake ganin koda inuwar Imti ne babu ita babu uban gayyar dif bakajin motsin su,abunda ya sake harzuka su kenan,ya ja musu matsala ya zare hannun sa alamun babu ruwansa,ta mutu kota rayu wannan ba damuwar sa bane, balle kuma aje kan Yaya da abun ya tsaye mata arai,ganin tana neman kassara rayuwar ta yasanya ta watsar da lamarinsa,saita sarara tasha iska kafin ta sake waiwayar sa.
Bangaran Imti kuwa babu abunda ya dameta rayuwar ta take aiwatar wa san ranta,watayawa take tamkar agidan su,kulawar Mamma sai abunda ya karu sosai ta zage damtse wajan lura da ita,duk da wannan kwanakin basu hadu da D ba amma tanajin shige da ficansa,saiya tabbatar da bata tare da Momma yake shiga wajan ya duba Momman sa.
Atakai ce sai wasan yar buya suke yi atsakanin su,shi bayaso ya ganta saboda halin dayake tsintar kansa,ita kuma tanajin kunyar goyon da yayi mata shine dalilinta.Wata sabuwar gulma su Haj Suwaiba suka samu kullum kafar su na part din Momma da zammar dubiya suka zoyi,bayan abaya sai su shafe wata daya batare da sun waiwayeta ba,ba tare da sunsan halin da take ciki ba,sarai yana sane da sintirin da suke yi tsaf kuma ya karance su.
Sakon harara ke hada su da Imti babu damar ta dago kanta sai taga wani na hararar ta,shiyasa da sunzo take daukar glass dinta no respect ta dana shi a face dinta,ta tsuke dan karamin bakinta,abun ba karamin bata musu rai yake ba, Little tasan sarai da gayya take saka wannan glass din saidai taita kunshe dariya tana kallon su,aciki kuma anrasa wanda zai tanka,saboda shakkar D inya fitar dakai daga estate dinnan har abada kaida shigowa cikin sa,sàidai ka hangoshi daga nesa.
Shiyasa suke kama kansu suke iya takunsu zadai su biyo ta wata hanyar amma banda magana ta fatar baki.
Dukkan wani motsinta sun karance shi,abinda sam bata lura da hakan ba harkar gabanta kawai takeyi,kaya take sawa na kece raini kunsan Imti badai daukar wanka ba, baza'a gaya mata wannan ba,abinda ya sake dunguzuma hankalin su kenan,ganin tana neman tafi yayansu ji da gayu,kyau da zati duk takerewa yayan nasu,shiri suke gagarumi akan su,tamkar wadanda zasu yaki duniya suka hada karfi da karfe wajan cimma nasarar su.
Sam basu san target din da suke akan su ba,rayuwar su suke babu kowa azuciyar su,hatta yammatan nan suka bari wajan firar su,habaici kam Imti na shansa,tun tana jin ciwo harta saba da hakan ko kadan abun yadaina damunta, little ce abokiyar hirar ta, Mammi abokiyar shawarar ta,kullum tana makale da waya ita da Ummeen ta shakuwa ce megirma tashiga tsakanin su,duk da har time din Imti batasanar da ita wanene Ziyad ba,tayi shiru da bakin ta.
Cikin masu shirin harda Amar shine shugaban su,dan ya dauki Alwashin saiya rama abunda D yayi masa,sai duniya tasan wanene shi,ayau ne kuma suka gama shirin su tsaf dan aiwatar da kudurin su.
Kamar yadda yake al'adar sa,duk daren duniya saiya sha coffee, Little ce ke kaimasa sakamakon bata da lafiya ta roki Imti ta taimaka ta hada masa,yar harara ta watsa mata,marairaice face tai please sis,kauda kanta tayi daga kallon ta,sam batason zuwa wajan sa,kwarjinnsa nayi mata yawa matuka gaya,kamar bazata mike ba Little taci gaba da rokon ta,tashi tayi ahankali gaban ta na tsanan ta faduwa,tamkar ta juya haka take ji,amma ta dake bazata iya watsi da alfarmar Little ba.
Tun sanda Momma ta kwanta ciwo,gaba daya ya sallami ma'aikatan gidan,saboda be yadda da kowa ba,akan wannan hukuncin na D ankai ruwa rana,ya badawa idanun sa toka duk wadda bazatai aikinta da kanta ba,ko yayanta suyi mata,saidai ta zauna da yunwa,aiko yasha tsinuwa kwando kwando,matan estate din sai suka kara kullatar sa.
Kamarsu,ace su shiga kiching suna fama da tukunya,sundade suna ciwon rai kafin su saba,babu yadda suka iya dan mazajan suma basu isaba balle su,duk abinda sukai yanajin su,amma yayi biris dasu,ya watsar da lamarin su,shirunsa na nufin komai shiyasa suka shafawa kansu ruwa,dan dole suka rungumi gas da tukunya.🤣🤣
Abun dariya sai gashi suna layin tafiya koyar girki,ko dan su tsira da mutuncin su,da barazanar kara Aure da mazajan su sukai musu, dole uwar naki saiga ahakin Darma sun bazama neman ilmin girki.😁😁ko banza ya taimake su lol.
Maine parlo tafito babu kowa shiru,kusan karfe 9pm dama zakaji gidan ya dauki shiru, koda da ranane balle dare.Kiching ta wuce sam batajin dadin jikin ta,gas ta kunna butar tea ta dakko yar karama ta dora,jin kamar ana taba kofa ta fita tadan dudduba sam bata ga kowa ba, kiching din ta dawo lokacin ya tafasa yadda taga Little na hada coffee din haka ta hada.
Gaba daya ta juye awani cup me matukar kyau da tsari,tana tunkarar part dinsa kirjinta na dokawa,harsai data dan dakata wajan dafe kirjin ta, password ta sawa kofar kamar yadda ayanzu ta haddace kowane password na bangaran Momma,ahankali ta tura kofar ta shige, parlon tsif kamar babu wani me numfashi acikin sa,kamar ta juya haka taji amma ta daure ta kutsa kanta bedroom din.
Yana zaune sanye da kayan bacci, laptop ce akan cinyar sa,aiki yake cikin kwazo da kwarewa yake daddana key board din,sam be dago ba sànin wanda ta shigo din,jin shiru beji surutunta ba yasashi dago idanun sa,wadanda suke cike da gajiya,zube su yayi akan ta kamar ranar ya soma ganinta,kayan bacci ne ajikinta masu taushi farare tas,duk da basu fito da surar jikinta ba amma sun matukar yi mata kyau.
Dauke kansa yayi daga kallon ta,a hankali ta matso har gaban sa,wani dan table ta janyo da yake gabansa dorawa tai batare datace masa uffan ba,shima bece mata uffan ba ahankali ta juya yabita da kallo harta bacewa ganin sa,harta shigar daki ta dafe goshinta tunawa da tayi bata sa masa sugar aciki ba,dan tsaki taja ta kalli little tare da hararar ta duk itace ta jawo mata wannan wahalar.
Kamar tashare sai taji sam hakan be dace ba,taya zata kai masa abu ba sugar ba spoon sai time din ta tuna da shi,mikewa ta sakeyi cikin kasa da baccin daya rufe mata idanu, kiching din ta sake komawa kwalin sugar ta dauka gaba daya sai spoon din data zara kamar zata fadi haka yakeji saboda bacci.
Anasa bangaran kurba daya yayiwa tea din yaji ba sugar dan tsaki yaja baya son kuma ya huce,yasan tana sane ta kawo masa hakan dan karyasha ne,haka ya dauka yana kurba duk da ba dadinsa yakeji ba,dan yaji dumi acikin sa haka ya daure yana kurba kadan kadan,duk kurba daya yanajin yanayin sa na canzawa,bekawo komai aransa ba yaci gaba da shan tea dinsa.
Wani irin gumine ya fara tsatstsafo masa jin abunda be taba jiba arayuwar sa gaba daya jikinsa rawa ya kamayi na tashin hankali,hannun sa na rawa ya jawo wardrobe dinsa da kyar ya balli maganin sa yasha amma abanza kamar ya karawa wuta fetur,tuni jijiyoyin kansa sukai rado rado,wani irin sarawa kansa keyi na tsananin azaba,wani irin karfi yake ji wanda be tabajin kamar sa ba,jiyake kamar zai rasa rayuwar sa jida ganin sa gaba daya dauke wa sukai.
Tsananin azaba ya sashi wulli da Laptop dinsa batare da ya sani ba,sam ya kasa control din kansa,gaba daya ya fiddarai da rayuwa a wannan lokacin,dai dai lokacin Imti ta shigo ko ganin gabanta batayi fatanta ta kaimasa takoma ta kwanta, Numfashinsa ne yayi mata welcome,turus taja ta tsaya tana kara kasa kunnan ta,da yar sassarfa ta shiga bedroom din,wanwar ta hangoshi akasa yana malelekuwa ta tsananin azaba.
Yarda kayan hannunta tayi ta karasa gare shi hankalinta tashe,neman agaji yake dama,neman mafaka yake,duk da halin d yake ciki be hana ya tantance wacece agaban saba,tambayarsa take me ya sameshi ina baya jinta sam,idanunsa sun rufe kunnuwansa sun toshe,fuzgota yayi tafado kansa,saidatai wata yar kara,jin yadda hakarkarinta ya amsa tsam ya rungume ta akirjinsa,wahalallan Numfashi yake saukewa.
Soyake yayi control din kansa,matukar yace zai sauke bukatar sa akanta,yana da tabbacin inbe kashe taba zai mata mummunar illah,shiyasa ya zabi ya rungumeta ko zaiji sassauci,azaba tayiwa Imti yawa yadda kasan me matsar kuli kuli haka ya matse ta,kukan ma kasawa tai saboda azabar matsar da take sha, jijiyoyin kanta sunfito rada rada gaba daya jitai Numfashinta baya fita yadda ya kamata.
Azaba jikin ta kemata duk yadda taso ya cikata abun ya faskara,wata irin rawa jikinsa keyi wadda ke sake fadada hauhawar tsoranta,meyasa meshi,bata dame bata amsa. Yasaketa ya sanar da ita me ya sameshi amma ya kasa,fuskarsa ta kalla hawaye ke sauka daga idanunsa,shikadai yasan masifar da yake ciki,shiyasan azabar dayake karba,zare idanu tai ganin hawaye a idanun Ziyad yau Ziyad ne ke Kuka, lallai ba karamin jin jiki yakeyi.
Jinin jikinsa tafasa yake zabalbala yake kamar ana rura wuta adukkan sassan jikin sa,da kyar ya mike akan kafafun sa cikin tsananin jarumta,tana kwakume ajikinsa, toilet ya jata dama bathtub dinsa cike yake da ruwa janta yayi suka fada ciki,shiru tai tana sakin numfashi koba komai taji sassauci ajikin ta,jin sanyin ruwan na ratsata,sunkai 30mnt acikin bathtub din Ahankali jikinsa ya rage rawar da yake yi ba kamar daba.
Wani bacci ne ya fara fusgar idanun ta,ahankali take Lumshe kyawawan idanun ta,tsurawa face dinta idanu yayi da jajayan idanun sa, numfashi yake saki na wahala,yana cikin wani irin yanayi dashi kansa bazai iya tantancewa ba.
A hankali ya mike yana tangadi kamar dan maye,wani irin duhu yake gani agaban sa,tsaida ita yayi akan kafafunta,amma baccin idanunta ya hanata tsayuwa sake kwanciya tai ajikin sa,tana tsayen ya zare kayan jikin ta saboda kartai mura,kayan sa ya zare shima kan yadauki towel ya daura cikin karfin hali yake wannan aikin,daura mata towel ita ma yayi kafin ya dakko ta da kyar yana hada hanya.
Kan bed dinsa ya kwantar da ita,daidai lokacin da towel din jikin ta ya kwance, shanyayyun idanun sa ya zuba mata,wani abu na sake dawo masa,sam bazai iya rike akansa ba,matukar zaiyi hakan kuwa zai cutu,cutuwar da bayajin zai iya moruwa anan gaba.
Jin bakon yanayin dake ziyartarta, tun tana tunanin mafarki take har taji abun ya wuce gona da iri, afirgice ta farka tana ture shi daga jikin ta,ina Ziyad baya jinta baya Duniyar ma gaba daya dan Momma yayi nisan da bazai iya dawowa ba.
😢😢😢😢😢
Mrs Baba Bello Abubakar.
......✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 64_65
Duk yadda take rokon sa sam bayajin ta,fatan sa ya isa duniyar sa,duniyar daya dade yana mafarkin ta,duniyar dayayi shekaru yana fatan shigarta,taya zai juyo da baya alokacin dayake daf da cikar burin sa,duka da yakushi Ziyad ya shasu amma besan tana yima ba,tayi kiran Ummee dan neman ceto agare ta,kiran Little dan tuhuma agare ta,da hadin bakinta akan turota datai wajan yayanta,tayi kiran Dad ya ceceta, Mammi tasha kira awannan dare,kai hatta ya kumbo sàida Imti tai roko ta kawo mata dauki.
Hinde da Dije Malam okasha Yahuza babu wanda bata tuna awannan lokaci ba mecike da azaba agare ta,me ciki da wahalar wa aduniyar ta, tun tana Kuka har Numfashin ya tsaya cak daga gangar jikinta,sam abunda ke zagaye da jininsa ya hanashi yaji tausayinta,ya hanashi yaji kanta,ya hanashi ya tuna ya tantance wacece ita,baya ji baya gani yashiga wata duniya wadda besan da ita ba sai ayau din,yadda take Kuka haka yake Kuka da kiran Momman sa tazo ta cece shi.
Jida ganin sa gaba daya daukewa sukai yadda ta suma haka shima ya suma.
Karfe 6am ya farko daga dogon suman daya tafi kansa na azabar sarawa kamar zai rabe biyu,jinsa awani abu me taushi ya sashi daga kansa dan ganin menene,idanunsane ya fada akanta,tsura mata idanu yayi cikin mamakin ganin ta adakin sa,hawaye da majina sun gama yayin su sun bushe afuskarta,idanunta sun kumbura sumtum duk da arufe suke,lebanta sun bushe kamar ta shekara tana cuta.
Kansa ya dafe da tariyo abunda ya faru jiya,dama ba mafarki yakeyi ba, ahankali ya mirgina daga jikin ta,cikin mutuwar jiki da kasala,yakai 5mnt kafin ya tashi zaune da kyar,towel dinsa ya dauka ya daura,ahankali ya dawo inda take kwance,yaye bargon jikin ta yayi da sauri ya mayar ganin irin aika aikar da yayi mata,gaba dayanta ya dauketa ya dorata akan cinyarsa, rungume ta yayi,so da kaunarta na sake huda zuciyar sa,girmanta da kimarta na dada yaduwa aruhinsa.
"Kaunarta ta mamaye jinin jikinsa,idanun sane ya tara kwalla ganin ko matsi batayi tashi yayi da ita ajikinsa"
Kai tsaye toilet ya wuce da ita,ruwa ya tara medumi sata yayi aciki,ajiyar zuciya ta sauke me karfi,kafin ta zabura cikin jin azabar radadin yadda zafin ruwan ke ratsata. Kokarin fita take daga ruwan jin kamar ana yayyankata da wuka, rungumeta yayi ajikin sa,cikin tsananin tausayin ta, bubbuga bayan ta yake kamar baby,Kuka take mara sauti dan wahala ma takasa barinta tai kukan.
Ta wahala iya wahala ahannunsa,shi kansa yasani beje da wasa ba,kansa ya matukar daukar charge,meya sha haka,menene ya jawo mai shiga wannan halin,furzar da hucin bakinsa yayi,maida hankalin sa yayi kanta,duk wani tai mako da zaibata ya bata,amma still tana narke ajikin sa,koyaya bata so tai motsi,kai babu inda baya ciwo ajikin ta,hatta keyarta azabar ciwo take mata.
Iya damuwa ya damu, rarrashin ta yake amma kamar sake tunzurata yake,mikewa yayi da ita ajikinsa gaba daya kansa ya kulle,tawace hanya zai taimaketa,maida ita bed yayi, phone dinsa ya dauka, Ring biyu tadaga kiran,maganar 1mnt yayi ya datse kiran,jallabiyar ya dauka ya saka parlo ya koma gaba daya ransa ajagule.
Kai tsaye ta shigo room din,kallon sa take daga sama harkasa,tana sake tsuke fusatacciyar fuskarta,kamar idanunta zasu fado dan hararar sa, Dariya yake kokawa da ita,hanyar bedroom dinsa ya nuna mata,cike da rashin fahimta take kallon sa,kauda idanunsa yayi daga kanta,kamar gurguwa haka take takawa zuwa bedroom din,duk taku daya kirjinta dokawa yake.
Idanunta akanta ya fada,Zuciyarta barazanar tsagewa take,jinin jikinta tafasa yake,jin jiri na daukarta tatafi dabar ta zauna akan bed din,lallai D ya shammaceta ita zai kirawo ta tabbatar da zargin su akan sa,ita zai ciwa mutunci,ita zai tozarta,ita din,wasu hawaye ne suka fara kwarara akuncinta,hannunsa ya nade yana kallon ta,Murmushin gefan baki ya saki,yau Yayah na Kuka da idanun ta ya tabbatar abun ya daki Zuciyarta.
Cikin wani irin yanayi take kallon sa,kallon ka ciceni kaci amanata,kallon ka ha'ince ni,kallon kaci nasara akaina,mikewa tai duk nauyin jikinta batajinsa,ayanzu jitake kamar iska zata kayar da ita,Zuciyarta daci take kuna take ruruwa take,lalli tayi babban kuskure takashe maciji bata sare kansa ba,me akai kenan anyi ba'aiba.
Tare hanyar fitar yayi kallon ta yake daga sama har kasa,wani malalacin murmushi ya saki ina zakije Yayah bayan baki aikin daya kawo kiba,ko kin manta duk gidan nan kece babba,shiyasa na baki girmanki amatsayin ki na wadda taga jiya taga yau ke kadai zaki iya gyara barnar da danki ya aikata.
Hannayanta ya ruko gaba daya,ko kinmanta dan nan nakine dakika sha kiran takadirine shi,da lasisin ki fa komai ya faru,ke kika bada gudummawa me karfin gaske, nagode Yayah babu abunda zance miki sai Godiya,kin matukar saukakemin hanya,hanyar dana jima ina marmarin binta kin nunamin hanya alokacin da bankawo hakan ba,kin bada gudummar da bazan manta dake ba,matukar najefa kwallo araga karki mamakin in macece bazan sa sunan kiba.
Kalamansa sake tafasata sukeyi idanun ta kamar garwashi haka suka koma tsabar bacin rai, Numfashi ya saki kafin ya dora da fadin mezesa bazaki karasa ladanki ba Yayah, come back yayata,cike da shakiyan ci ya rungume Yayah yana sakin Murmushi.
Wani karfine yazo mata fusge hannayanta tayi daga nasa,bata ganin gabanta haka tabar part din binta yayi da kallo,harta bacewa ganin sa,hada hanya take na tashin hankali,wace irin bakar ranace wannan agare ta,wai wacece wannan din,tana bukatar amsa da gaggawa tun kafin Zuciyarta ta buga,tafiyata zata fadi cikin azama ya taro ta tunfitowar ta yake kallon ta,mamakin sa meyakaita part din D duk da nauyin ta haka ya jure da kyar ya maidata part dinta.
Tuni tafara kokawa da numfashin ta,kallon ta yake kamar ya samu TV Numfashi ya sauke ko yaushe mutanan estate dinnan zasu canza,dage kafadar sa yayi ko waiwayowa be sakeyi ba,yabarta a wajan dan bashi da taimakon dazai mata,part din Mammi ya nufa,sai Lokacin na lura wanene shidin Sir Ayub,dama suna da alaka da D kayataccen parlon Mammi ya shiga,tana zaune tana azkar dago da kanta tayi,face dinta dauke da murmushi take kallon dan nata.
Ahankali ya tako gabanta kan guiwowinsa ya tsugunna agabanta,cikin farin cikin ganin ta,Mammi ya furta idanunsa na kanta,shafa kansa tayi cikin tsananin kaunar sa,sonsa da kewar sa.Ayub ta furta tana sake fadada fara'ar ta, please Mammi kallon sa tai for what,part din D akwai damuwa kije Mammi kallon sa tai nawasu yan sakanni,damuwa ta maimaita a Zuciyarta,mikewa tai batason banzatar da maganar sa.
Yana tsaye a parloun tashiga gaba daya ya hargitse gashin kansa,idanun sane ya fada akanta,cikin sauri ya sunkuyar da kansa kasa,kunyarta yakeji sam bayason hada idanu da ita,karantar sa takeyi tabbas akwai wani abu dake damun sa,dan murmushi tasaki na karfafa masa guiwa,hannayan sa ruko.
Zatai Magana kenan taji Kuka daga bedroom,kasa kunnuwanta tai tabbas daganan kukan ke futowa,tsura masa idanu tai da alamar tuhuma agare shi,sake sunkuyar da jansa yayi cikin sanyin jiki dana zuciya,sam be so hakan ba,amma ya zaiyi,mikewa tai batare data ce masa komai ba, Ahankali tataka zuwa dakin,daga bakin kofa ta tsaya tana kare mata kallo,kallo daya tai mata tagane halin da take ciki,dan runtse idanun ta tai,tuno Maganar da sukai da Dd Yusuf hakan ya karfafa mata zuciyar ta.
Ya matukar shammatar ta,bataso bashi Imti ahakanba,saitayi mata gyaran dazai gigita Duniyar sa,saita sauke masa duk wani girman kansa,saiya zama rakumi da akala,bawan Imti,megudun bacin ranta,amma kash yarigata,amma hakanma bata makara ba,zata shayar dashi mamaki,karasawa tai cike da tausayawa take kallonta,sam bata hayya cinta,azaba take karba tako ina,hatta da idanunta ta kasa budewa.
Duk wani taimako tayi matashi,duk dakiya irinta zuciyarta saidata zubar da hawaye, zuciyarta ta matukar zafafa da aika aikar dayayiwa Imti,taci alwashin saiya biya bashin wahalar daya bata.Sabon bedsheet ta canzawa bed din,kafin ta kwantar da Imti,wadda tausayinta yagama zagaye jini da zuciyarta.
Tsam ya mike yafice gaba daya, Kukan ta kara zafafa masa zuciya yake,tunanin sa me yasameshi,wani Zazzabi yakeji acikin jikinsa,idanun sa sun canza matuka,part din Mammi ya nufa,dakin ya bude cike da rashin kazari, zazzafan Zazzabi ne ajikinsa,dago idanunsa yayi yana kallon sa,kauda kansa yayi yana kunshe Dariyar sa.
Sir Ayub kenan dayake ko kawa da Dariyar dake cinsa,duk halin daya ke ciki be hana shi watsa masa harara ba,uffan bece masa ba ya wuce bedroom dinsa,binsa da kallo yayi yana sakin Murmushi,cike da tsokana ya bishi dakin,tokarewa yayi akofa yana kallon sa.
Yadai Malam badai a toilet dina zaka wanken najasar jikin kaba,ko kallon sa beba ya wuce shi ya fada toilet din,yar dariya ya saki yana girgiza kansa.
Cikin tashin hankali ta zuba masa wani gigitaccen mari,cikin huci take kallon sa,Amar ina wayata take,kasan muhimman abubuwan dake cikin ta,yanzu ka fadan maganar banza wai baka ganta ba,kenan abunda muka shirya ya tashi abanza,kana nufin Video din bamu samu nasarar samun saba!!! Cikin tsawa ta karashe karshan maganar ta,jikinta har rawa yake na tashin hankali.
Kallonta yake dafe da kuncin sa,firgicin dayake ciki ya ninka nata,tashin hankalinsa yafi karfin ya furta,Haj Kubrah tamkar zata tada aljanu, tambayar su wanene ya dauki wayar da sukai kyakykyawan shiri da boyo babu tayadda zaka gane akwai wani abu da aka aje awajan,amma lokaci daya su nema su rasa,hannu duka biyu Haj Suwaiba ta dora aka ta fashe da kuka,kun cucemu kun bamu gurguwar shawara,cikin kuka take wannan maganar.
🤣🤣Sunyi abun yasha musu kai warrr.
Anyi ba'ai ba, maimakon su samu kwanciyar hankali,sun karara gigita Duniyar su.
To waima shin dame suke shirin aikatawa,wanene ya dauki ajiyar da sukadan babu wanda yasan da ita.
Tuku har kullum
Mrs Baba Bello Abubakar
......✍️✍️✍️
💕💕IMTINAN💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 66_67
Cikin rishin kuka take fadin wllh babu hannuna aciki,tunda dama ba wayata bace kuje can ku kurata keda dannaki,mikewa tai da nufin barin dakin,afusace Haj Kubrah ta shako wuyanta,ke kimma isa tare dawa aka hada plan din,shine saida abu ya kwabe zakice ba hannun ki,wllh baki isa ba,babu wadda ta isa tazare kanta awannan aikin.
Haj Maimuna data kasa magana tsabar bacin rai,ba biyan bukata ga gararin da suka jefa kansu,tsaki taja,ai kamar yadda Suwaiba ta fada ne kece aciki keda danki,babu ta yadda za'ai akamamu da laifin nan,tako wace hanya baki da shaida,kinga Kuwa kune aruwa,nima nazare hannuna,tunda abunda nake san kasan tuwarsa naga ba samuwa zaiba,abu yana neman zamemin bala'i.
Balle kuma ni Haj Turai data turo daurin dan kwalinta gaban goshi,dan wllh ko za'a tashi yakin Duniya a estate dinnan bazan taba nuna koda wasa nasan maganar nan ba,babu hannuna aciki,rashin hankali ba'a samasa rana,kallon da Haj Kubrah ke musu kenan,ashe za'ai yaki agidannan,kwance daurin dan kwalinta tai taci dammara,to wllh kuwa koni ko ku,bakisan wacece Kubrah ba ko shedan yasan da zamana wajan hada tuggu da makirci,kuje a kuncire hannun ku amma ni guguwar masifar da zan kunto muku bazakuji da dadi ba.
Kedin banza da zaki kwanto mana masifa,to fitina dai akwance take duk wanda ya tada ita Allah ya tsine masa Haj Maimuna ke wannan maganar,fashewa Haj Kubrah tai da wata muguwar Dariya,oh Maimuna ashe kin san Allah ni bantaba zatamma kin taba zuwa islamiyya ba,sai yau,to ki ajiye dan guntun wa'azinki ke zaiwa amfani ni daku mu zuba mugani.
Gimine ya fara tsatstsafo wa ko waccen su,wani busashshen yawu suke hafiyewa da kyar,sai kallon kallo suke atsakanin su,an rasa wadda zata tanka bakin tsanya ya mutu murus,kallon su tai daya bayan daya ta sake sakin dariyar mugunta,kodai kuzo aci gaba da tafiya kamar yadda aka saba ko kuma tafashe halin kowa ya bayyana a bainar nasi,numfasawa tai tana sake kallon su.
Haj Suwaiba ce ta muskata munji bayanin ki,amma ke kanki kinsan in har yar tone tone za'ai wllh namu bekai naki ba,amma tunda hakane ataru arufawa juna asiri,koya kukace ta kalli su Haj Turai kamar wadanda ruwa ya cisu,gyada kai sukai kamar kadan garu,hakane bakomai aci gaba da tafiya,cikin amana da yardar juna,kun samowa kanku maslaha,duk bayanin da ake agaban Amar sukai komai,cike da Mamaki yake kallon su da tunanin me suke aikatawa ba tare da kowa ya sani ba.
Jijjiga kansa yayi jikinsa na sanyi akan lamarin su,wane abune da kowaccen su bata fatan abankado asirin ta, jiyayi yana dana sanin shiga tim din su yazama dole yayi gaggawar fita daga cikin su,koma mene suke kullawa suje can su karata.
Mammi tasha matukar wuya kafin Imti ta fara dan samuwa,tea me zafi ta hado ta bata da kyar take sha hawaye na kwarara a idanun ta,yau ta tabbatar D baya kaunarta,nayadda ya kasa tausaya mata,dukko da magiyar data dingayi agare shi,amma yayi bris da bukatar sa,rauni sosai ya jimata dole sai anyi zaman jinyarta an kula da ita,mikewa Mammi tai zata fita daga room din,da azama Imti ta kankame ta,fashewa tai da kuka,dan bata marmarin ko amafarki ta kara shigowa part din D.
Juyowa Mammi tai tana kallon ta,dan Allah Mammi karki barni kitafi dani,kallon ta tai cikin tausayi da zallar kaunarta,kiyi hakuri Imti ba barinki zanyi ba,amma kinsan bazaki iya tafiya ba,shida yayi barnar shi zaizo ya dakko ki,kiyi shiru kinji,shiru tai badan zuciyar ta ta aminta da maganar Mammi ba,fita tai daga dakin,kamar jiran fitarta yake,taji ansake turo kofa.
Dago kumburarrun idanun ta tai da tunanin Mammi ce ta dawo,ido biyu sukai da shi,yasha wanka sai baza kamshi yake,fuskarsa sai fitar da wani shirtaccen annuri take,da sauri tai kasa da kanta,cikin tsananin tsoronsa, ahankali take kokarin tashi ta samawa kanta wajan buya,saidai sam kafarta taki bata damar hakan,gangar jikinta yaki bata hadin kai,fashewatai da Kuka tana sake kallon sa, tsoron sa me girma ya gano Acikin idanun ta.
Wani irin yanayi yakeji ajikin sa,kaunarta na fusgarsa,santa na sake shigarsa,kimarta na karuwa a idanun sa,tashayar dashi mamaki,ta tabbatar masa itadin me tarbiyya ce,ta bashi abunda be taba zata daga gareta ba.
Idanun sa da suka fara canza launi ya zuba akanta shauki yake ji,inama da kari daya sake ziyartar ta,amma yadan hakan bame yiwuwa bane yana tsananin tausayinta,inya sake nemar wani abu daga gareta yatabbata meson Zuciyar sa,dole ya jure ya maze,amma ya zama dole ya koyar da ita wanene shi ta shirya ta tabbatar da mijin nata gwarzo ne.
Takawa ya farayi dan isa gareta,karfin kukanta na sake karuwa,ruwan hawayanta na sake gudana,duk waye daya jinsa yake kamar dalma take diga masa azuciya,wai duk shine silar zubar hawayan ta,saiyaji yana tuhumar kansa,saboda shine take zubar da hawayan ta.
Hade hannayan ta tayi alamar ruko,ta kasa motsawa ko kadan, illah hawayan dake ambaliya a kuncin ta,jiki da zuciyar sa ciwo suke,a hankali ya duka agaban ta,cikin wani irin sanyin jiki da tarin kauna agare ta,kukan tane ya tsaya cak tanai masa kallon mamaki,tsugunnan me yakeyi agaban ta.
Hannayan ta duka biyun ya kama Aish ya ambata cikin wani irin salo, lumshe idanunta tai cikin wani yanayi data kasa tan tancewa,zuba masa idanun ta tai wadanda suke sake ragargaxar zuciyar sa,mikewa yayi ya zauna a kusanta,face dinta ya rike atafun hannun,harshan sa yasa cikin wani irin salo yake lashe hawayan nata,cikin tarin mamaki da al ajabi take kallon sa,anya Ziyad ne wannan agaban ta,anya shine D dinnan me cike da izzah.
Zagaye hannayan sa yayi abayan ta,bugun zuciyoyin su karuwa yayi,samun kanta tayi da sake lafewa ajikin sa,jiyake inama su dawwa ma ahaka.Kin shayar dani zumar dadi Aish,saurin runtse inun ta tai ganin babu wata da kuwa ko kunya aface din sa,lallai Namiji bashi da kunya ya ayyana aranta,kalamai yake furta mata wanda besan ya iya su ba,besan a ina ya koye su ba,daga can cikin zuciyarsa suke futowa.
Wata irin narkewa tai ajikin sa,laifukansa na gogewa agare ta,wani shaukine yake fusgarta,batare data ankara ba Murmushi ya dinga subuce mata,tuni D ya kara susucewa,yakara sukurkucewa,burinsa ya koma Duniyar sa,duniyai daya shigeta wadda besan da rabinta ba,ya kalu balanci kansa,da tun tuni be wuce wajan ba,datasan hakane da tun yana 20 years zaiyi Aure amma ya cuci kansa.
Kukan tane ya dawo dashi hayyacin sa,ya tuna da jinya ce ta kawo shi,sake rungume ta yayi kirjinsa na harbawa,a hankali ta fara ko karin raba jikinsa da nata,sake kankameta yayi baya fatan tai nesa dashi,baya fatan ta motsa nanda can.
Dago idanun ta tayi tadan kalle shi,wani narkakken kallo taga yanayi mata,da sauri ta rufe idanun da tafukan hannayan ta,wata irin kunyar sa takeji hade da tsoronsa,murmushi yayi me fadi wanda hartaji sautin fitar sa.Wata magana ya rada mata akunnenta wadda nikaina bansan me yafada mataba,boye kanta tayi a faffadan kirkin sa,jinwata kunya na sake lullube ta.
Bude kofartai ta shigo batare da tasan yana ciki ba,harara ta wurga masa saurin sunkuyar da kansa Yayi yana shafa keyarsa,kokarin zamewa tafarayi daga jikin sa,cikin jin kunyar Mammi sam bataso tazo tasame su ahakan ba,maida kallon ta tayi kan Imti da take faman sunkuyar dakai,au bana koma tunda kin warke se kije kici gaba da biye masa,idanun tane ya ciko da kwalla,kiyi hakuri Mammi banice na kirashi ba,tabe baki Mammi tai ke kika sani.
Juyowa tai tafice inkaga dama ka dakko ta kakawon ita,kallon tashin fahimta yake yimata,ina zataje Mammi,wajena zata koma,kamar zaiyi Kuka yake kallon ta,ni kumafa,juyowa tai ta fasa fitar datai niyya,kaikuma fa,tambayata ma kakeyi,koda tare kuke kwana kafita daga idanuna D sunkuyar da kansa yayi kamar zai fashe da Kuka dan takaici,tashi ki wuce mutafi kafata kafarki.
Zan kawota ya furta ransa a cunkushe,karma ka kawo ta fita tayi daga part din baki daya,kallon Imti yai datai tsuru tana zare idanu,kokarin mikewa takeyi,lallai so take ma tatafi ta barshi,ko da dai dama ba sonsa take ba,hakanan yaji wani daci a zuciyar sa,mikewa yayi ya tako har gaban ta,yadda ake daukar jarirai haka ya dauke ta,runtse idanun ta tayi tana kara kwanciya ajikin sa.
Suna zaune a parlon Momma ko wacce tasha kwalliya ta kece raini,fatan su su samu shiga,babu me kallon yar uwarta,ba karamin zafin juna suke jiba,kowaccen su najin da ita kadai ce da yanzu ta samu nasarar mallakar D,amma sun zo sunyi kaka gida ana neman ayi mutuwar kasko.
Tunda suka juyo kamshin turaransa kowacce ta sake gyara face dinta,kayane ajikinsu masu matukar fidda surar su,fatan su su janyo ra'ayin sa,murmushin kan face dinsune ya dauke dif dalilin mummunan ganin da sukai,zukatansu tsalle suke,lugudan duka suke na tsananin kaduwa.Face dinsa adinke take tsaf sarai yasan da wanzuwar su,dan bude idanun ta tayi caraf kallontà ya fada akan su,mamaki yasasu mikewa batare da sun sani ba.
Kamar anda sasu awajan haka suke kallon su,mamaki zane akan fuskokin su,sake narkewa tai ajikin sa,wash dear ta furta cike da tsokana,kallon ta yayi cikin matukar kulawa,da tarai raya,sake kan kameshi tayi muzauna,inda ta nuna masa ya kalla,cikin mamakin ta,murmushin gefen baki ya saki,kamar yadda ta nema samun sofa yayi ya lafe da ita ajikinsa.
Sofar da take facing din su babu babu abunda basa kallo,jinin jikinsu nema yake ya kafe kaf,wata mika Imti tayi wadda tai masifar motsa D gaba daya ta gama kunno shi,sam ya manta da mutanan dake parlo,hade bakin su yayi yanai mara wani kiss wanda ya gigita Duniyar ta,sake damke harshan sa tayi cikin fitar hayyaci da shaukin da basu san zasu shiga cikin saba.
Ganin yana nemana wuce gona da iri Imti ta samai kukan shagwaba,kukanne ya dawo dashi tunanin sa,jajayan idanun sa ya dora akanta,wani narkakken kallo tabishi dashi,sam Safna kasa tsayuwa tai akan kafafunta,zubewa tai akan guiwowinta kuka ta fashe dashi me azabar zafi da ciwo,zafafan hawaye ke kwarara a idanun ta,su Husna wutar dakeci a kirjin su bazama su iya kukan ba.
Babu wata damuwa a face dinsa ya sake daukar babynsa,anan suka barsu bayan sun manna musu dan karamin hauka.
Uhm Abun na manya ne,salon ba irin nasu bane.
Mrs Baba Bello Abubakar.
.......✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 68_69
Tamkar zasu tashi sama suka bace daga part din baki daya anan sukabar Safna azube akasa,sam batajin zata iya tsayawa akan kafafunta,wani irin so takewa D wanda batasan sanda ya shiga zuciyarta ba.Kowannen direct wajan mamarsa ya nufa,cikin fitar hayyaci da tashin hankali,ko ganin gaban su basayi,fatansu su isa ga iyayan su.
Suna tare a parlon yaya ana cigaba da tattaunawa akan mutane biyu rak, D da Imti wadanda suka gigitasu cikin 3weeks suna wasa da tunanin su,zubawa yaran nasu idanu sukai cikin Mamakin abunda ya hargitsa su,kowacce jikin Mahaifiyar ta ta kwanta,ajiyar zuciya suke saki,idanun su kamas sai azabar suya da kirjin su ke musu.
Kai mene haka zaku samu agaba kuna zazzare idanu kamar wadanda sukai gamo,sai Lokacin Kuka ya kufcewa Surayya wani irin Kuka take tundaga kasan zuciyar ta,mun shiga uku Mami annoba ta shigo mana gida,ai gwara ace gamo mukai da kasurgumin aljani da dai idanun mu ya hasko mana mummunan gani,wanda ya gusar da duk wani fatammu,muradimmu,yayi kaca kaca da walwalar mu.
Taya zancire son D Mami dan ALLAH ki sanar dani ko zan cire shi araina na hakura dashi,Kuka ta sake fashewa dashi,sai Lokacin suka san akan wa yayan su suka firgice haka,yazama dole sukadauki mataki,ciki kuwa har kisa zasu iyayi akan cikar muradan yayan su.
Husna Hah Kubrah ta kalla nidai Mom wllh inakan bakata babu wata shegiya da zata firgitani,babu gudu baja da baya akan bukatata,haryanzu ban karaya ba Mom,kuma kece karfin guiwata,rushewa tai da kukan bakin ciki wani irin tsanar Imti ke dasuwa azuka tansu,kota tsiya kota arziki saita bar estate dinnan.
Samha tana jikin Hah Suwaiba Kuka take kashirban magana sam ta gagare ta,san D ya zame mata masifa,babu laifin wadanda take gani illa iyayan su,tunkan su mallaki hankalin kansu ta karfi da yaji suka cusa musu son D,da kwadaituwa da dukiyar sa,abunda ko waccen su ta bada himma kenan ba tare da yar uwarta tasan huduba iri daya suka dinga yiwa yayan ba.
Sun taso da sonsa da kaunar sa,ranar da kowacce ta gano abu daya suke so ba karamin tashin hankali sukai ba,dambe sukai kamar zasu kashe kawunan su,abunda ya tashi hankalin estate din baki daya,iyayan su mata sun shiga alhini,sai alokacin kowaccen su ta gano huduba iri daya sukaiwa yayan su,bacin rai ya sauka azukatan su,amma da yake gogaggin yan duniya ne babu Wadda ta nuna bata son yarta ta Auri D sai suka hadu suka dun kule amanufa guda daya.
Matukar yayan su suka samu nasarar Auran sa baki daya,zasu fantama su shakata,darajar suce zata karayin sama,matsayin su na surukan D,duk wadatar da Allah yayi musu basu gode ba harin matsayi da daukaka suke uwa Uba dukiya.
Babu Wadda ta tanka acikin su gudun kar siyi subul da baka agaban yayan su,rarrashin su sukai da kalamai masu kwantar da hankali,haj Turai da kanta taje tataho da Safna Wadda Zazzabi yayi mata rufdugu,yayi mata kwaf daya,abunda ya kara dunguzuma hankalin su kenan,akan wata mutum daya yayan su na shirin shekawa barzahu.
Shiri na Musamman suka fara,kowacce taci alwashin saita samowa yarta muradin ranta kota wace hanya ce kuwa,gari ya gari kasa ya kasa Haj Maimuna tai tattaki har India wajan wasu kasurguman matsafa tatafi kudi ta narkar dasu kamar bata san zafin suba,awajan aka tabbatar mata Imti Mata D ce da igiyoyi Uku kwarara akan ta,sumane kawai Haj Maimuna batai ba,wannan bakin Labari ya dugunzuma hankalin ta.
Gumi ta dinga sharcewa cikin tsananin kaduwa take maimaita kalmar Matar sa,tabdi jam ashe ma tai makon su sukayi,suka kara hade su suka zamo abu guda,ashe sunyi basi ba,wani daci takeji azuciyar ta,inama basi wanann gangancin ba,dam kirjinta ya buga idan kuma Imti ta samu ciki fa,shikenan dan shine zai cinye gadon D.
Hankalifa ya tashi tunani ya gushe,cikar buri kawai take nema,aiki me suna aiki tasa aimata akansu,da nufin ayi musu farraku,aka tabbatar mata bazasu taba rabuwa ba mutuwa ce zata rabasu,duk wata hanya da tasan zatabi anbita amma babu nasara,nasarar da aka samu ta hana Imti haihuwa ce tako wani hali kar abari ta haihu,sannan asamu D ya Auri yarta adasa masa matsanan ciyar soyayyar Surayya.
Sauran abokan takarar ta ahanasu cikar burin su ita dai yarta ta Auri D in yaso bayan Surayya tashiga kissa da makirci zaisa su kori Imti,akarshe tanema akulle mahaifar su Husnah Safnah Samha,kamar yadda ta bukata hakan akai,bayan matsafin ya nemi saiya kwanta da ita na tsahon kwana uku,babu wata damu tartare da ita ta amince da bukatar sa(Allah ka tsare mana imanin mu). Kwanan ta biyar ta juyo cikin tsananin farin ciki da dakon kammaluwar aikin ta.
Abunda bata sani ba kowaccen su bazaba tai,kasa kasa haka sukai tattaki kowacce da boyayyan matsafinta,kamar sun hada baki kowaccen su bukata iri daya suka nema,kuma an tabbatar musu zasuga aiki,kamar yadda aka sanar da Haj Maimuna Imti matar D ce suma haka aka sanar musu,babu wadda ta nunawa yar uwarta akwai wani waje da taje,kowacce taja bakin ta ta tsuke,babu wadda ta budewa wa wata sirrin ta.
Bangaran Imti kulawa take samu ta musamman wajan Mammi cikin sati daya ta warware kamar ba itaba,gyara na Musamman Mammi ke mata dan danan saigashi ta kara wani fresh tayi kyau matukar kyau duk inda ta gifta kamshi ke tashi ajikin ta,duk yadda D yaso ya ganta Mammi hanawa tayi ta shafawa idanun ta toka,da sun shigo zata kasa ta tsare a parlo,kamar zai hauka haka yake kewar matar sa.
Imti kuwa hankalin ta kwance,take shakatawar ta,duk da tana kewar sa,tana mararin ganin sa,amma bata nunawa Mammi hakan ba.
Kulawar Momma hannun Little ta kara komawa tin tana mitar Imti ta dawo harta gaji ta kyale ta,takaicin abunda Mammi ke masa ya shi tattarawa yayi tafiya,ko sallama beyi mata ba,yace tajika Imtin ta shanye,ita ma zatazo hannun sa,saiya fanshe duk wata wahala da Mammi ta bashi.
Yayah ma tanacan bakin ciki na neman zautar da ita,tayi tunanin duk hanyar data biyo saitaga bazata bulle mata ba.
Yauma tana zaune a bedroom dinta,tayi zurfi cikin tunanin ta,harya shigo batasan da wanzuwar saba,dan tafi yayi a daidai saitin fuskarta,firgigit tadawo daga tunanin data lula,kallon sa take daga sama har kasa.Wata dokakkiyar shaddace ajikin sa yaci babbar riga da yar ciki,kawar da face dinta tayi tana sakin Numfashi.
Akamme kike wanann tunanin Yaya,batare da tace komai ba take kara kallon sa,hawaye yagani kwance a idanun ta,ware idanun sa yayi akan ta,nafara nadamar abunda na aikata Sani na fara nadama fashewa tai da Kuka me tsanani zuciyarta akuntace take,tun sanda ta aikata takasa samun nutsuwa da sukuni arayuwar ta,mugayan mafarkai sun Aure ta,ya zatayi ta gyara kuskuranta.
Ana wata ga wata me Yayah ta aikata data fara Nadamar sa.
Mrs Baba Bello Abubakar
.......✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 70_71
Kallon ta yakeyi cikin bacin rai da bakin ciki,me kike fade Zuwaira kina nufin kice wai tona mana asiri zakiyi,wllh kinji na rantse daga ranar da kika bankado asirimmu,daga ranar bazaki kara Numfashi a duniyar nan ba,har yaushe imani ya sauka azuciyar ki,kinsan da hakan lokacin bakiji tsoron aikatawa ba,zuciyar ki ta bushe ta kekashe da san abun Duniya,sàida aka gama raba ganima dake zaki dawo da baya kice àah baki isaba Zuwaira!!! Cikin tsawa ya karasa fadar hakan.
Sai data razana dajin sound din muryar sa,babbar rigarsa ya bude wata shegiyar bindiga ya dakko yar karama,ba karamar razana Yayah taiba,gaba daya hawaye ne yake rige rigen a Fuskarta,cikin rawar harshe take fadin yanzu Sani sai ka iya kasheni,wata muguwar Dariya ya saki, Zuwaira kenan kina mamakine,karka manta uwarmu daya ubanmu daya,Wani mugun tsaki yaja,intakai ce miki magana Zuwaira iyayammu nina kashe su balle wata ke banza abanza.
Ayanzu ma zan iya datse miki rayuwa,saidai kash bazan yi hakan ayanzu ba,ba yanzu nake son mutuwar kiba,saina gama amfanar ki yayata,bindigar hannun sa ya shafi Fuskar yaya da ita,sam jida ganinta sun dauke kalmar nina kashe iyayammu nayi mata kururuwa adodon kunne,fitsari ta dade da sakin sa a zaune,dama akwai wanda ya shanye ta azunubi,dama da zai iya kashe iyayan sa,me sukai masa,tambayar da takeyi azuciyar ta kenan.
Dago rinannun idanun ta tayi tana kallon sa,wani irin tsoronsa ne me girma ya shiga zuciyarta,jikinta rawa yake,dana sani da tarin Nadamane azuciyar ta,wani irin Kuka ta fashe dashi me tsananin daci da kuna,kukan kaico take kukan ta cuci kanta,dama amfani yayi da ita danya sata Acikin masifa? Kwadayi da buri ne ya jawo mata gashi ta kasa samun kwanciyar hankalin data zata zata samu,gadai dukayar nan tana cinta,amma hankalin ta ya gaza kwanciya.
Wayyo ni Zuwaira na cuci kaina,duka hannayan ta biyu ta dora aka,wata dariya ya kara saki kukanta ba karamin Nishadi yake bashi ba,tsaf na kare masa kallo babban mutumne cikin kayan kamala farine tas yana tsananin kama da ahalin gidan musamman D saika rantse shiya haifeshi,saboda tsananin kamannin su.
Zuwaira Zuwaira wakiliyar shedan kin manta kirarin da kike yiwa kanki,ko alahira ga kujerar shedan ga taki,shine na taimaka miki dan ki cika burin ki,amma menene Abun kuka,zuwai zuwai yar Mama cikin matukar tsokana yake furta hakan agareta,zuciyar Yaya kamar zata fashe tsanar dan uwanta na samun wajan zama azuciyar ta,tana matukar kaunar iyayan su,ashe shine ya kashe su.
Mikewa yayi bari nadan fita ko zakisha Iska kiyi tunani kafin ki yanke abunda zuciyar ki ke sanar dake,ko baki furtaba nasan kina tunanin tona mun asiri ne,bazan hanaki ba Zuwaira amma kitabbatar duk ranar da kikai yunkurin hakan saidai kiwayi gari akiyama gaki ga uban gidanki shedan,wata muguwar Dariya ya saki tare da sara mata,cikin takun kamala ya fice daga parlon,binsa tayi da kallo kamar zautacciya.
Yana fita daga part dinta motocin D na shigowa tare da guide dinsa,fadada murmushin sa Alhaji Sani yayi na farin cikin ganin sa,tundaga nesa D ya hangoshi, murmushi ya sakar masa shima, ahankali ya fito cikin takunnan nasa na ingarman Namiji,cikin girmamawa yake kokarin dukawa ya gaisheshi,da sauri Alhaji Sani ya ruko shi,zamu bata fa Darma,ruke hannayan sa yayi suka fara takawa har zuwa part dinsa.
Cikin kulawa yake tambayar sa harko kin sa,bashi amsa yake daki daki yana gyada kai kamar kadan gare.Maine parlor suka shige Haj Maimuna an kashe dauri dan ya sanar da ita dawowarsa,cikin kwarkwasa ta mike tanai masa sannu da zuwa,ganin sa tare da D saiya kara sa hauhawar farin cikin ta,sai fara'a take da Addu'ar cimma nasarar ta,bakin ta har rawa yake wajan kwallawa Surayya kira,fitowa tai cikin riga da wando iya guiwa.
Kallon D take ckin shork din ganin sa,kallon Dad dinta da Mom dinta tayi cikin farin cikin ganin D a part din su,da gudu ta juya ta fada toilet dole tayi wanka na musamman,kallon juna sukai Alhaji Sani da Haj Maimuna murmushi suka saki,kafin su maida kallon su kan D dasam hankalinsa baya kansu, saika dauka bacci yakeyi,ya lafe akan sofa,tunanin Habibiyar sa na kara ragargaza tunanin sa yaci alwashin yau saiya ganta,kai gaba daya ma saiya kwamushe ta ya tafi part dinsa da ita.
Cikin Kulawa Alhaji Sani ya kalle shi, taso son food is ready, girgiza kansa yayi alamar baya bukata,dan bata face Alhaji Sani yayi ai baka isaba saikazo kaci,ruko hannun sa yayi,babu yadda zaiyi shiyasa ya bishi,cikin takun kasaita Surayya ta futo tasha wasu fitinannun kaya sai tashin kamshi takeyi, murmushi take saki ayau ji take kanta ya kara girma,yau D a part dinsa wayyo dadi,alama Haj Maimuna tai mata tazo tai serving din su,cikin kwarkwasa da gwalli tatura plate gaban D.
Tun daga idanu abincin beyi masa ba,frid rice ce tasha curry nama zuku zuku,kadan yadan ci ya she spoon din hannun sa,mikewa yayi batare da yace uffan ba,gaba daya hankalin sa nakan Imti,fatansa da zumudin sa ya isa gareta,binsa sukai da kallo,sàida yaje kofar parlon ya daga musu hannu alamar byee,sosai guy dinnan ya sake tafiya da Surayya jitai ina bazata iya asarar santalelen saurayin nan ba.
Part din Mammi ya wuce kai tsaye babu kowa a maine parlo sai karar AC,dan jim yayi yana canki cankar ina zai ganta,wani daki dake lungu ya shige,sanyi ne da kamshi medadi ya daki hancin sa,ko beganta ba yasan tana ciki,wannan kamshin ita kadai ya sani dashi,maida kofar yayi tare da murza mata key,karar ruwan da yaji shiya tabbatar masa tana ciki,bed din ya fada yana sauke numfashi.
Daga ita sai towel da kadan ya wuce kugunta,hankalinta kwance ta futo dan tasan babu wanda zai shigo mata daki,kamshinsa ta zuka cikin wani yanayi ta lumshe idanun ta,ta tabbatar mafarkin da take yawan yine akansa,basarwa tai ta ja kujera ta zauna agaban mirror,janye gashin fuskarta tayi da nufin gyarashi,ido hudu sukai dashi kamar tsohon maye haka yake binta da wani malalacin kallo.
Saidata furgita ta ina ya shigo yaushe ya shigo batare data sani ba, bangaran D tunda ta fito yake kokawa da numfashin sa,wata irin kasalace take sakko masa,kallon kasan idanu yake mata,gaba daya kunya ta gama da baibayeta,sai jan towel din jikinta take waiko zai kara tsayi amma ina yaki karawa.
Ahankali ya taso daga kan bed din idanun sa har Lokacin na kanta,ta bayanta ya tsayi ya sunkuyo da kansa daidai gefan wuyanta,kamshin ta yake shaka me azabar dadi, Numfashin da yake sauke mata ya sanya mata wata irin kasala,ta mudubi yake kare mata kallo sunyi matukar facewa da juna,kallon da take mata ya girmi tunanin ta da sauri ta runtse idanun ta,saboda kwarjini da yayi mata,wani munafikin murmushi ya saki na gefan baki.
Kara bude idanunta tayi ahankali,caraf ya kara fadawa nasa,wana kama,ya furta asaitin kunnan ta,kin gama guje gujen da boye boyen yaudai kinzo hannun Ziyad,zanga wanda zai kwace ki,raurau tayi da idanunta,cikin matukar kaduwa da kalaman sa,hawayene ya fara sauka akuncin ta,kayi hakuri ta furta cikin kuka,bata mance azabar data sha a hannun sa,gaba daya hankalinta ya gama dugunzuma.
Yar karamar Dariya ya saki,mene abun kuka ba mafaka Mammi ta baki ba,ni tunda bani da gata niya kamata nayi kuka ma,harara ta watsa masa ba tare da tasan tai hakan ba,dan ware idanunsa yayi cikin sigar tsokana,lalala ni kike harara,surin girgiza kai tayi alamar àah,aida maganar farko ake amfani,kan tayi magana gaba daya ya sunkuceta,wutsil wutsil ta farayi da kafafunta.
Saidaya direta akan bed din ya dungure mata kai matsoraciya kawai,murginawa tai tana boye fuskarta,cakul kul ya farayi mata,dariya takeyi jin yadda yake matsa mata ciki,abun ba karamin nishadi ya bashi ba,daga wanann wasa ya canza salo saiga me Dariya ta bige da Kuka,yauma tasha kuka banbancin sa da wancan kadanne,rungume ta yayi yana rarrashin ta,dagaya mata kalamai masu kwantar da hankali,wata irin narkewa ta sakeyi ajikin sa,tabara take zuba masa,gogan kuwa ya kara susucewa Imti ta gama sace zuciyar sa tsaf.
Mrs Baba Bello Abubakar
.......✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 72_73
A rayuwar sa yana son mace me shagwaba,hade da kissa da sangarta,sai gashi ya samu saiya kara zama rakumi da akala awajan ta,tagama da zuciyar sa wani irin linkaya take a kalbinsa,ita kadai take shawagin ta.
Tun daga wannan rana sukai wata irin dinkewa da babu mejin kansu,gaba daya ya dawo part din Mammi biris tayi kamar batasan me suke yiba,sai ya tabbatar Mammi ta kwanta,zai salallaba ya fada dakin matar sa, bangaran Imti wani irin so take yiwa D wanda ita kanta bata san adadin sa ba,bata taba kawowa ko da wasa zata so shiba,ayadda takejin sa azuciyar ta ashirye take ta sadaukar da rayuwar ta akansa.
Tana yawan tuna maganar Ummee,data ce da sannu zataji rayuwar tama zata iya sadaukar wa asabo dashi,gashi yanzu ta gasgata hakan,ta kara tabbatar wa Ummee me kaunarta ce duk duniya bubu wanda zai so mata Alkhairi sama da Ummeen ta.
Kalaman da batasan ta iya suba su take furtawa D dinta,abun kaunarta,alfaharin ta,ya zame mata kamar yaron goye,sai yadda tai dashi,ita kejan ragamar sa, Mammi ganin zasu makantata ta tattarawa Imti kayan ta korasu part din D tayi,cikin kunya Imti ta kasa kallon ta,kayan gyara na musamman ta hada mata,sanda take mata bayanin kowannen su,kasa kallon Mammi tayi wata irin kunya ke rifto mata,duka Mammi ta daka mata,gulmar banza,wai ni kikejin kunya jinake binsa kike kamar bindi,da gudu ta mike tafice tana dariya,itama Mammi dariya ta saka,tana jin kaunar yarinyar azuciyarta.
A parlo ta hange su,idanu abude take kallon sa,ko shekaru nawane bazata manta dashi ba,shima zuba mata idanu yayi yana kallon ta,kauda kansa yayi yana dan sakin murmushi,abayan kujera ta buya jikinta narawa,sai yarfe gumi take, hankalin ta yayi matukar tashi,sai lokacin ta hango tsantsar kamannin su da D,dan Uwansa ne kenan,ras taji gabanta ya fadi,D ne ya kalli sir Ayub harara ya watsa masa, ahankali ya mike ya isa gare ta,tana bayan kujera ta kasa kwakwkwaran motsi.
Jin kamshin sa ya tabbatar mata ya daf da ita,bude idanun ta tayi ya fada kansa,hawaye ya gani jage jage a idanun ta,dariya taso bashi amma ya gimtse kayar sa,hannu ya miko mata alamun ta kama,da kyar tasa hannun ta anasa,gaba daya ta kasa sukuni,har inda yake zaune ya jata,abayan D ta boye fuskarta,gaba daya kunyar kallon sa take,inta tuna abubuwan data aikata masa.
Amaryarmu ya furta cike da dariyar tsokana,wata kunya ce ta kara kamata,cikin sanyin jiki dana Zuciya,ta kara tabbatar wa kanta,da zuciyarta,koya dan adam yake ba abun wulakantawa bane,yanzu da wane ido zata kalle shi,dawani baki zata furta kalamar hakuri agareshi,har wani gumi ke tsatstsafo mata,dan kallon D tayi da yake kallon ta,tabashi matukar dariya da tausayi,ya tabbatar wannan ba Imtin baya bace,wannan wata sabuwar Imtinan ce Allaha ya bashi.
Yayi kokarin yaki da zuciyar sa,dan daina tunanin baya,amma haryanzu yana jin kishinta,nayadda wasu garadan banza suka kalle masa mata,kauda kansa yayi daga kanta,kafin yamaida kallonsa kan sir Ayub,bakinta na rawa take kokarin magana,daga mata hannu yayi murmushi dauke a face dinsa,karku ce komai Imti,ni bantaba rikeki araina ba,komai ya riga ya wuce,dama ba aikina bane,wanda ya sani aikin na kammala masa,harya faracin amfanin gonarsa,gira ya dagawa D dayake sakar masa hararar gargadi,nakar ya fallasa masa asirin zuciyarsa.
Har dariya Sir ya saki,gaba daya Imti bata gane kalamansa ba,illa na yayi mata afuwa wanann kadai ya isheta,sakin fuskarta tayi,nagode ta furta tana wasa da hannun ta,tab lallai su Imti anyi laushi,sir Ayub ya ayyana azuciyar sa.Mikewa tai ta taka ahankali tana barin parlon,binta yayi da kallo santa na kara shigarsa,dukan kafadar sa yayi,kai dan iska,ka bar yarinyar mutane ta huta,na sanka inka kama abu daya ka tayi kenan.
Dan tsaki D yaja to in fitsari abun banzane kaza tayi mana,kaima kaje kasa taka matar adaki,ku shekara aciki ma,au ni kake ciwa mutunci saboda kasamu Allah ya baka asama shine kake hura mun hanci,dan tsaki yaja sai kuma kayi tashi yayi yabar sir Ayub yana dariyar shakiyan ci.
Dakin ta bude ahankali Little na zaune hannayan ta rike dana Momma,tana fata da dokin yaushe zata farka,yaushe zata kira sunan ta,yaushe zataga murmushin ta, yaushe zatai mata kirarin Auta datake mata,sam batasan ranar ba,hawayen face dinta take sharewa,hartakarasa gabanta,bata san da shigowar taba,tsugunnawa tai agabanta,kafin ta dafa kafadar ta,dagowa tayi da jajayan idanun ta,Kuka ta sake fashewa dashi ta rungume Imti.
Sister yaushe Momma na zata tashi,ina fatan ganinta akan kafafun ta,ina mararin jin muryarta,tsawon shekaru Biyar banji hakan daga gareta ba,ina so ko yayane naga motsin ta,shekaru biyar Hammana na fafutuka akan ta,zuwanki rayuwar mu muka fara walwala,kedin wata haske ce agaremu,wani bangone abun jinginar mu, nagode da kika zamo mata ga Hammana,dif wuta ta daukewa Imti,kallonta take da Mamakin wa yasanar da ita,awajan wa taji hakan.
Baki Little ta turo gaba,eh dankin ki gayamin kin san akwai masu fadamin,ni bantaba zatan akwai abunda zaki boye munba,in dai Momma ta samu sauki za'ai gagarumin bikin da ba'a taba yin sa akaf garin Lagos ba,sai duniya tasan cewa Hammana ya samu Sarauniya,yayi sa'ar mata,ya kerewa mazaje,yayi musu rata me tarin yawa,sainayi rawa najuya,sainayi kwalliyar da bantaba yiba,saikin zama tauraruwa,ke tsokanar idanun makiya,baki bude Imti ke kallon Little dama kina surutu haka.
Yar Dariya ta saki kamar ba itace ta gama kuka yanzu ba,nima jinai ina zuba,amma duk kece kika koyamun magana,ni karkimin sharri Hajiya,saura hajijiya, Little ta fada cikin Dariya,yar dariya sukai baki dayan su.
Kulawar Momma sake da wowa hannun ta tayi,sosai take mata addu'a a yanzu,tasan abubuwa masu tarin yawa,kullum Magani ake wa Momma babu wani cigaba,hakan yasa tazauna tai zurfin tunani tabbas tatabajin Ummee tace ana iya yiwa mutum sihiri kuma maganinsa Addu'a,hakan yasa ta dage dayiwa Momma badare ba rana,ruwan zam zam ashi take tofa addu'a tana shafawa Momma,saitaji zuciyarta ta gamsu da hakan,ta samu nutsuwa fiye da yadda doctor ke sintiri akan ta.
Yau tun sassafe ta mike tagaji da ganin Momma awaje daya,gaba daya ta dauke ta daga kan bed dinta,sam bata da nauyi kamar baby haka ta koma, bedroom dinsu ta maida ita ta kwantar da ita,rike kugutai tana tunanin ta inda zata fara,yaye bedsheet din tayi ta aje agefe,cikin jarumta ta fara kici kici fa katifar Momma alallai saita daga ta sharo har karkashin bed din,amma abun ya faskara,gefe ta koma tana sakin Numfashi.
Little ce ta futo daga toilet,cikin mamaki take kallon ta,me kikeyi hakan,hararar ta Imti tai me idanun ki ya gane miki,gyarawa Momma dakin ta zanyi,yar dariya Little tasaki amma wllh ke muguwar wahalalliya ce,yanzu taya zaki baro mana wannan aikin,ke kikaga aiki ni banganshi ba,malama zoki kamamun mu daga katifar nan,dafe kirji little tai,kema dai kinsan bazan iya daga wannan muguwar katifar ba,saidai akira Hamma shine zai iya,kamar zatai Kuka take kallon Little nidai karki mirawo shi.
Ai kinsan school zan tafi taya zan zauna sharar karkashin bed,da gudu Little tai hanyar waje Imti ta bita akokarinta na kamota saidai tariga tai mata nisa,cije yatsa tayi zakizo ki samani,kai tsaye part din Hamman ta tanufa,yana kwance akan sofa tunanin gimbiyar sa ya hanashi shukuni,daga cewa bataje tatadawo shine ta gudu dama wayo tai masa.
Kallon Little yayi datake haki,dan hararar ta yayi yadai,zumbura baki tayi matarka ke kiramka kazo kuyi sharar karkashin bed,kallonta yake yi da tunanin me take cewa haka,wane bed din,na Momma wai sharewa Momman zatai,ni kuma school zantafi dan Allah kazo kuyi tare please Hamma,shi abunma dariya ya bashi wai sharar kasan gado,kafadar sa ya dage gaskiya nagaji bacci nake ji.
Ayya Hamma ka taimaka,hannun sa tarike tanaja alamar ya tashi,dan dole ya tashi,amma fa saiya hukunta Imti abunda tamai jiya,tana jikin gadon sanda suka shiga sai kici kici take da katifar,kamar me kokawa da sa,sai uban nishi take tana hada gumi,amma tsabar naci taki hakura,harde hannun sa yayi yana kallonta,bakaramar dariya ta bashi ba,tayi wujiga wujiga gashi har yanzu babu biyan bukata,sai wahalar da kanta takeyi.
Kallon su tayi cike dajin haushin sun tsaya suna kallonta,babu wanda yayi kokarin taimaka mata,Kuka tasaka tana bubbuga kafafunta,dariya suka saka mata, Little ce ta riketa akunnan ta ta rada mata,ke sis Matukar kinason aikinnan ya yiwu kidaina hakan agaban Hamma dan yanzu zaki kwance masa notikan dake rike dashi,yar dariya sukasa batare da yasan abunda suka tattauna ba.
Kamar ko yadda Little ta fada hakanne,wani abu yaji tana tsirga masa,gaba daya tagama kunno shi,idanunsa harsun canza kala,Imti ce ta kalleshi tare da kashemai ido daya,cike da tsokana rai masa gwalo,nuna kansa yayi alamar dashi take,daga masa gira tai tare da murguda masa baki,dan murmushi ya saki yana shafa keyarsa,alama yayi mata zakizo hannuna,dage kafadar ta tayi alamar nazo din,uhmm ya furta.
Takowa yayi har gaban bed din kama katifar yayi saigashi kamar ya dauki tsinke haka ya dage ta,kallon sa suke da mamakin ta yadda ya iya dage katifar nan cikin sauki,sunyi tunanin sai sun kakkamata an hada karfi da karfe kafin a iya dagata,saigashi ya dauke ta shikadai,daga musu gira yayi yayadai, Little ce ta saki Numfashi gaskiya Hammana kai jarumi ne,aiyafi haka Indai wannan yayan naki ne,Imti ta ayyana tana kada masa idanu.
Kauda kansa yayi yarinyar nan ta gane lagonsa,gwara ya daina kallon ta,tsaf zai manta da wata Little awajan ya kasa control din kansa.Bag dinta ta dauka nidai kunga tafiya ta bye ta daga musu hannu asha aiki lafiya ta fada tana yar dariya, murmushi kawai sukai suna daga mata hannu.
Kallon juna suka tsaya suna yi ganin irin kallon da D kemata ya sata saurin shigewa tsakiyar bed din,babu ragar gado wasu irin karafane masu sheki da walwali suke rike da kafifar,babu komai a kasan bed din sai kura,harta sanya kafarta zata futo idanun ta ya sauka kan wata kyakykyawar tukunya,me kyawun gaski,se kura data rufeta shine dalilin da yasa bata gantaba tunda wuri.
Cike da karambani Irin nata ta nufi tukunyar,yana tsaye yana kallon ta,bakin tukunyar arufe yake da wani net karkade tukunyar tayi,harta fara tunanin ta samu wadda zatana zuba ruwa aciki tana sha,dan a kauyen su ya Kumbo ruwan randa yana matukar yi mata dadi.
Harzai magana ya kyaleta,yana tunanin menene Acikin tukunyar shidai be taba ganin ta a gidan ba,cikin san wasa ta nude net din dake rufe abakin tukunyar,leka kanta tayi dan ganin menene aciki arikece tai wulli da tukunyar wata kara tasaka,luuu tatafi zata fadi sam babu numfashi tattare da ita,cikin zafin nama ya tarota,gaba daya tafado kansa.
🙆🙆🙆Me Imti ta ganowa kanta.
Menene Acikin tukunyar daya gigita Rayuwar ta har yayi sanadin suman ta.
Shin ajiyar danwa akayi ta.
Duk ku biyoni danjin yadda zata kaya.
Oum Nihla
......✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 74_75
Cikin tashin hankali yake bubbuga fuskarta Aish Imti Imtinan gaba daya yarikce cak ya dakko ta ya ajeta akan sofa,nishin da yakeji akasan gadon shi ya janyo hankalin sa,ahankali ya tako har bakin bed din,saidaya ja da baya zuciyar na wata irin bugawa,wata irin halittace me matukar muni,kallon ta kadai zai Iya sawa zuciyarka ta buga, jajawur take idanunta kwala kwala,gaba daya jikinta alluraine akalla sunkai guda 30 abun yayi matukar jijjigashi,taya abun yake numfashi duk Wannan azabar da aka gana masa.
Bega laifin Imti data sume ba,shikansa jarumtace da dakakkkiyar zuciya, tukunyar da yake ciki tuni ta tarwatse tayi daidai,wani ruwa me shegen wari da doyine Acikin ta,saurin toshe hancinsa yayi,kansa ya kulle matuka yaya zaiyi wa wannan halittar.
Abun tambayar ma wanene ya ajiyeta,idanun sane ya kawo kwallah dan tuno wadda aka aje abun domin ta,Momma ya furta hawayan face dinsa na gangarowa,dama tsahon Lokaci abunda akai wa Momma kenan,meta tsarewa wani,me tai musu,meta tare musu,suka zabi su cutar da mahaifiyar sa,wata irin tsana yayiwa ahalinsa,yana da tabbacin su dinne,me suke nema agare su,bazai taba lamunta ba,kamar yadda basa kaunar su,zai nuna musu shima baya kaunar su.
Hawayan fuskarsa ya share tunawa da Aminin Kakan sa babban malamine,agarin Kano,wayar sa ya dakko ya danna kiransa,saidata katse ya kara kira kafin adaga,cikin da shashshiyar muryarsa yayi sallama,dan murmushi tsohon ya saki,cikin kamala da dattako,Ziyad ya furta cikin yanayin muryar sa ta Girma,barka da Safiya Malam Babba,barka dai munsameku lpy,lafiya kau Malam dan jim Ziyad yayi,ina jinka Ziyadu,numfashi ya saki kafin yayi masa bayanin dalilin kiransa.
Dan jim Malam Babba yayi,yanzu abunda zakai karka taba shi da hannun ka,ka dauke shi da wani abu ka sanyashi Acikin abunda ka tabbatar bazai mutu ba,Inda zaisha iska,ayau basai gobeba,ka tabbatar kakawo mun shi cikin aminci,mutuwar sa daidai take da tsayawar Numfashin mahaifiyar ka,abunda aka shirya kenan,cikin tashin hankali yake sauraron maganar Malam Babba,kallon halittar yayi da yake jujjuya idanu yana nan zaune inda Imti ta yar dashi.
Acikin me zai sashi kenan, kiching ya shiga ya dakko kwali,bubbula kwalin yayi,faka ya dakko ciki dakiya ya dauko shi ya sashi acikin kwalin kafin ya rufeshi yabar masa wajan da zai dinga shan iska.wayar sa ya dauka ya kira guide dinsa ashirya masa tafiya Kano ajiye wayar yayi ya sunkuci Imti gaba daya yabar part din da ita ya nufi nashi,kwantar da ita yayi akan bed dinsa,ahanzarce ya kara futa jikin sa har rawa yake saboda bacin rai,Momma yaje ya dakko tana nan yadda take,part dinsa ya kaita daki daban ya sanya ta aciki.
Tsugunnawa yayi agabanta tausayin ta na mamaye ilahirin zuciyar sa,me tayiwa wani,meta tsare wa wani da aka zabi akawo karshan rayuwar ta,duk wanda ya kama da wanann laifin bazai taba barin saba.Wajan Imti ya koma tana kwance sam bata Numfashi ruwa me sanyi ya dauko ya zuba mata, ahankali ta sauke ajiyar zuciya,kanta tadan dafe dayake sara mata,zabura tai zata mike cikin fitar hayyaci tare da fashewa da Kuka,gaba daya ta firgice kamar zararriya haka tako masa.
Duk yadda yake kokarin riketa abun ya faskara,wanann halittar take gani a idanun ta,Kuka take tana karawa gaba daya kan D ya dau charge, rungume ta yayi gaba daya ajikin sa, zuciyar sa ta matukar karaya shima kukan ya fashe dashi, abubuwa sun masa yawa,kansa azabar ciwo yake,yanajin tsoron ko wani abu ya sameta,bazai taba yafewa kansa ba,bazai samu nutsuwa ba saiyaga nutsuwar ta.
Addu'a ya fara tofa mata, ahankali nutsuwa ta fara zuwa jikin ta,kankamesa ta sakeyi,bata fata ya matsa daga gareta,wani irin tsoro takeji,tsoro me girma daya cika zuciyarta da ruhin ta,bude idanun ta tayi dan kauracewa daga kallon wannan halittar takasa barin cikin idanun ta,daukarta yayi ya nufi toilet da ita wanka yayi mata ko zataji sassauci ajikin ta,tako ji dadin hakan,kaya marasa nauyi ya saka mata,wani bacci ke ziyartar idanunta.
Rarrashin ta yake da kalaman godiya agareta,itadin haske ce agare su,ta haska masa hanyar da sam be taba tunanin taba,wani irin kaunarta ke sake nunkuwa azuciyar sa,sam bashi da tamkar ta,tunda taso Mahaifiyar sa tagama masa komai.
Dan Lumshe idanunsa yayi yana hadiye wani abu me mugun tauri,da daci a makoshin sa,tunani yake barkatai,yarasa wane kalar tunani zaiyi akan danginsa. Ahankali ya zareta daga jikin sa, toilet ya fada ya sakarwa kansa shower ya jima aciki kafin ya futo, shape shape ya shirya cikin manyan kaya,yana cikin daura agogo ta farka,karewa dakin kallo tai ganin ba adakin Momma take ba hankalinta yadan kwanta.
Hangoshi agaban mirror ya sata saukowa da hanzari,sam besan da tashin taba,jinta kawai yayi ta kwanta abayansa,gaba daya hannunta tasa ta zagayeshi dasu,tana sakin ajiyar zuciya,har Lokaci bata gama dawowa daidai ba,zagayo da ita yayi gaban sa,idanunta cike da kwalla take kallon sa,har Lokacin tsoro bebar zuciyar ta ba.
Hannun ta ya kamo cikin sanyi da tausayawa agare ta,bakin bed ya jata kafin ya dorata akan cinyar sa,shafa kanta yake dan ya rasa me zai cemata,kiyi hakuri Aish,daga kanta tayi alamar to,dan jim yayi kafin ya sake kallon ta,zanje kano amma yau zan dawo,tun kai yakai karshan maganar sa ta kankame shi,fashewa tai da kuka tsoronta na dawowa sabo,katafi dani dan Allah,sake kankamesa take Sam bazata yadda yatafi ya barta ba,waccan dodon data gani ya fito ya cinyeta.
Furzar da iskar bakin sa yayi,duk yadda yaso ya fahimtar da ita fur taki yadda,Kuka take rusa masa akan bazata zauna ba,zuwa lokacin Zazzabi me zafi ya sauka ajikin ta,bata taba ganin abunda ya furgitata ba irin wannan halittar,kama hannayan ta yayi gaba daya suka fice daga part din nasa,part din Mammi suka nufa,tana zaune a parlo ita da sir Ayub suka shigo har Lokacin kuka take ya rasa yadda zaiyi da ita.
Da sauri Mammi ta mike cikin damuwa take tambayar me akai mata,meyasa meta,hannu ta mikamata cikin sanyi ta isa gareta,jikinta ta jata tana bubbuga bayanta alamar rarrashi,sir Ayub kallon D yake da alamar tambaya akan face dinsa,zama sukai kamar kurame sai ajiyar zuciyar da Imti ke saki akai akai,kallon sa Mammi tayi kabarmu aduhu Ziyad ka sanar damu abinda ya sameta.
Zazzafan huci ya fitar idanun sa na sake canza launi,bayanin Abunda suka gani yayiwa Mammi babu wanda be razana acikin suba,cikin kaguwa da mamaki suke kallon juna,kallon Imti sukai jin soyayyar ta na karuwa azukatan su,itace tsanin datai musu jagora tsahon Lokaci suna lalube sun kasa nemo hanya,sai gashi zuwanta suna ganin haske,acikin dukkan abunda ya shige musu duhu abaya.
Alhmdlh abunda Mammi take furtawa,share hawayan face dinta take,Allah ya kawo mana karshan wahala,in sha Allah ina ji ajikina Aisha ta kusa tashi,ta kusa tsayawa akan kafafunta,duk wadda ya nufeta da wannan sharrin in sha Allah saiya koma kansa,saiya girbi abunda ya shuka.
Babu me magana acikin su kowa jimami ya hanashi magana,zata zauna awajan ki Mammi,mikewa yayi sir Ayub ya mike shima dan uwa tare zami wannan tafiyar,dan murmushi kawai D ya saki ya daki kafadar sa,cikin san dan Uwansa kuma Aminin sa,futa sukai daga part din Mammi tanai musu Addu'ar samun nasara,kai tsaye part din Momma suka koma yana nan acikin kwali inda ya barshi,shikansa sir Ayub saidaya razana.
Lallai ya jinjinawa Imti data farfado daga suman datai cikin kan kanin Lokaci,ta boyayyar hanya suka bi babu ta yadda za'ai jama'ar gidan su gansu,yaransa ashirye suke tsaf shikadai suke jira,a but ya saka dodon kafin su shige back sit drive ya jasu zuwa airport.
Allah sarki rayuwa Allah ka rabamu da sharrin makiya da mahassada.Ameen
Mrs Baba Bello Abubakar
......✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 76_77
Aminu Kano International airport nan jirgin su ya sauka,mask dinsa ne a face dinsa,shine agaba dauke da kwalin ahannu sai Ayub dake bayan sa,mota daya ce tazo daukar su,kai tsaye Aisami suka nufa gani yake kamar ba sauri suke ba,daidai layin Alhaji Auwal me dan kwali anan motar su ta faka,saboda yanayin gidan a lungu yake dole sai sun taka da kafafun su.
Yana dakin sa na soro a zaune Malam Babba kenan,tsohone sosai amma yana gane komai kansa be rikirkice ba,kallon su yake da murmushi a face dinsa,lale lale Ziyad dan murmusa yayi kafin ya cire mask din face din sa,cikin girmamawa suke gaishe shi,kwalin da suka ajiye ya zubawa idanu,lallai akwai marasa imani a duniyar nan.
Mikewa yayi dan abun ba nazama bane matukar aka bari wanann abun ya mutu akwai gagarumar matsala,Kubiyo ni Malam Babba ya nemi hakan,sake dakko shi yayi suka fito tare,cikin gidan sa suka nufa akwai wani dan gini da yake ganawa da mara sa lafiya nan ya kaisu,arammomi abokansa ya kira akalla sunkai su goma,zama akai na musamman suka zagaye halittar bayan sun fito dashi,babu wanda zuciyar sa bata tsinke ba, tsananin tausayin wadda akaiwa hakan ya kamasu.
Kowa shawara yake bayarwa ta yadda za akarya sihiri jikin sa,sàida aka gama hada shawarar kowa,su Ziyad na gefe suna ganin ikon Allah gumine yake keto masa tako ina, Addu'a yake ALLAH ya tashi kafadar Momman sa.
Wani ruwa a cup Malam Babba ya dauka,watsawa halittar yayi wani hayaki ne yake tashi daga jikin sa,wata kara yayi cikin azabar data gauraye jikin sa,cigaba yayi da watsa masa sàida hayakin ya daina fitowa daga jikin sa,lokacin tuni ya galabaita kukamma ya kasa yin sa, Addu'a suka ci gaba da karantawa wata kara yasaki saiga wata laya ta fito daga bakin sa.
Alhmdlh suka fara ambata gaba dayansu tabbas da alamar nasara tunda ya fara amayo abunda aka dura masa,babu wani tsoro Malam Babba ya jawo shi gaban sa,alluran jikinsa ya dinga zatewa daya bayan daya,duk sanda aka cire allura daya sai yayi Kuka,sàida ya zare gaba daya alluran jikin sa,shiru yayi akwance yana jin salama ajikin sa,ahankali jikinsa ya fara rikida,saigashi ya dawo siffar kunkuru,shine saboda tsabar zalinci aka canza mai kamannin sa.
Yana gama dawowa ainihin halittar sa ya mimmike alamar rai yayi halinsa,Allahu akhbar suka dauki kabbbara dukkan binsu,wani hawaye D yaji yanabin kumatun sa,tsoran ALLAH ne ya sake kamashi,ganin yadda dabba take mata guguwa wajan zarar ranta,balle kai dan Adam me tarin zunubi.
Sosai sukai wa Malam Babba Godiya,magunguna ya hada musu tare da Addu'a wadda za'a dinga karanta mata,in sha Allah cikin kwanaki kalilan zata farka,aranar suka juyo cike da zumudin yadda aka samu nasara.
Sanda suka dawo La'asar tayi,tsayawa sukai a masjid sukai sallah,suna dakin da Momma take sun zagate ta,ganin yadda ayau take motsa hannayan ta, Little sai sharar hawaye take sboda tsabar farin ciki,a hankali suka tako dakin Momma suka zubawa idanu da yan yatsunta ke motsawa kadan kadan,hamdala sukeyiwa Allah da mika Godiyar su agare shi.
Su biyar suka kasan ce adakin,Mammi, Imti, Little, D, sir Ayub,sukadai suka raba farin cikin su,babu wanda suka sanar da cigaban da aka samu na jikin Momma,kamar yadda malam babba ya sanar dashi yadda zaai da maganin daya basu,haka yasanar da Mammi,babu bata lokaci ta farayi mata amfani dashi,cikin kwanaki uku jikinta ya fara kyau,duk da bata farka ba har Lokacin amma wasu sassa najikinta sun fara motsawa.
Tsahon kwana uku kenan anai mata amfani da magungunan.
Imti ce zaune agaban ta ta zuba mata idanu face dinta cike da damuwa,tunanin ta sai yaushe Mammi zata farka,idanun ta taga ya fara motsi kamar amafarki,sake kura mata ido tayi ko kiftawa babu,fuskarta dauke da murmushi da jindadi, ahankali taci gaba da kokarin budewa,duhu take gani dindim maida idanun tayi ta lumshe,kafin ta fara gani dishi dishi.
Hawayene yake kwarara a face din Imti,na tsananin farin ciki,koba komai masoyanta zasiyi farin ciki,tasan wannan babbar ranace agare su,farin cikin su shine nata,sake budewa tai ta dora kallon ta akan Imti,tsayawa tai tana kallon ta,tana san tuno abubuwa da dama,amma ta kasa hakan tunaninta yaki daidaita.Mommah Imti ta furta ahankali,tsura mata idanu Momma tayi tabbas kamar tasan wannan sunan ayaushe,wacece Momma.
Hannayan Momma ta rike gaba daya acikin nata,tanajin tsananin Kaunarta,tun sanda ta fara dora idanu akanta,taji tsananin tausayin ta,jitake kamar Ummeen ta, ahankali Momma ta kara lumshe idanun ta, ahankali tafara tariyo baya,tunanin ta kodai mutuwa tayi ta dawo,amma ai ba'a mutuwa a dawo,jinta take kamar ba sauran tsoka ajikin ta,wani irin kashine ke sukarta,da azama Imti ta mike dan yin albishir agare su,cikin sanyi Momma ta ruko hannun ta,wanda ya koma kamar sillan kara.
Tsayawa Imti tayi ta juyo gareta,koma wacece wannan ta tabbatar ba acikin ahalin gidan take ba,bazata iya bude bakinta ba,data sanar da ita bata bukatar kowa daga ahalin estate din,gaba daya bata fatan ta sake ganin su,bata fatan ta kara tabar su,bata fatan susan warke warta,amma babu damar magana,runtse idanun ta tayi,wasu zafafan hawaye ke kwarara a idanun Momma,wanda ita kadai tasan me yake damun zuciyar ta.
Dawowa tai ta tsugunna agaban ta,mekike so Momma,aduk lokacin data ambaci sunan ta tanaji,kamar D dinta,kamar Little dinta,suna ina shine tambayar da takewa zuciyar ta,share mata hawaye Imti keyi, murmushi da hawaye dauke a face dinta,sarai ta karance ta,bata son ahalin gidan su san da wanzuwar samuwar lafiyar ta,to me yasa,bata dame bata amsa.
Cikin takunnan nasa,ya bude kofar tunda ya shigo take kallon sa,kauna da so irin na Uwa akan yayanta,wani farin ciki takeji a karkashin zuciyarta,cak ya tsaya dajin cewa akwai wanda yake kallon sa,dago kansa yayi idanun sa ya fada cikin na Momma,wani shork ne ya ziyar ce shi,sake bude idanun sa yayi,tabbas ita ce, Momman sace,tsahon shekaru yayi missing din kallon ta,muryarta,Albarkarta,nasiharta,jin kanta,ayau gashi ta dawo,wace irin babbar ranace agaresa.
Zuba masa idanu Imti tai,ganin kamar baya hayyacin sa, ahankali tataso farin ciki ya mamaye zuciyar sa,zuciyar sa zullo take dan isa gare ta,hannayan sa ta kamo ta fara jansa,kamar rakumi haka ya bita,agaban Momma ta tsayar dashi,kasa tsaiwa yayi da kafafun sa,dukawa yayi agaban Momma,hawaye ke gudu a face dinsa,hannun sa na rawa yake shafa Fuskar Momma,ita ma hawaye ke shatata afuskar ta.
First Love ya furta cikin tuna wasu lokuta da suka shude,inya fada mata takan yi dariya tace ALLAH ya barmin kai Ziyad dina,Allah ya.karemin kai da karewar sa,Allah karka bari 'yayana su zama marayu,wannan Addu'ar ce ko yaushe abakin Momma.
Little ce tashigo da duba Momman ta,kamar amafarki take kallon su,Momman ta take gani kallon Little take cike da kewarta,inama zata iya data tashi ta rungume 'yayan ta,da gudu tataho fadawa jikin D murna tasa tarasa inda zata saka kanta,sauka tai daga jikin sa,gabas ta kalla tai sujjada,dan ta nuna Godiyar ta da Allah ya nufi Momman ta da shi,fashewa tai da Kuka tanaiwa Allah kirari da sunayansa 99 tana ta wassali da Annabi Muhammad sallallahu Alaihi wasallam.
Zuba mata idanu sukai gaba dayan su,mikewa tai gaban Momma ta tsugunna kafin ta rungume ta,tana sanya kukan farin ciki.
Allah sarki Allah ya sakawa iyayammu da mafificin Alkhairi.
Ni kaina nataya D da Little farin cikn warkewar Mommah.
Mrs Baba Bello Abubakar
........✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 78_79
Babu wanda suka sanar da samuwar lafiyar ta,kulawa suke bata tamkar kwai,kowannen su fatansa ya faranta mata,Imti da Little har rige rigen yimata hidima suke, password D ya canza babu ta yadda zasui su Iya shigowa ba tare da ansan da zuwan suba,zuwa wannan lokacin ta fahimci wacece Imti,Mammi da kanta ta sanar da Momma matar D dinta ce,ranar har kukan farin ciki tayi,kaunar Imti ta dasu azuciyar ta,ganin yadda ta damu da lamarin ta.
Tsahon wata 1 suna jinyarta,tun tana zama har suka fara koya mata tafiya,ranar datadan fara takawa da kanta,bakaramin farin ciki sukai ba,sunyi murna har wata kwarya kwaryar walima suka hada atsakanin su,sunci sunsha sun godewa Allah. Awannan time duk wanda yasan D yasan ya canza ko yaushe face dinsa dauke da Murmushi me kayatar wa,bakin aljihu ya bude mabukata ya dinga rabawa sadaka.
Haka gidan marayun sa ya kara wadata su da abubuwan more rayuwa,yaransa kansu da yawansu sunyi kudi ta dalilin alherin D,shiyasa sukeji zasu Iya bada rayukan su akan su fanshi tasa,tako wane hali yaki suke da magautan sa,ba dare ba rana hari ake kawo masa naban mamaki,sam D be damu da yasan suwanene masu farautar rayuwar saba,ya sawa ransa basu isa su cutar dashiba face Allah ya kaddaro hakan gare shi.
Rayuwa fa tayiwa Yayah tsanani lafiya taki samuwa agareta,kullum Kuka take wanda aka rasa gane kansa,jininta ya sake mummunan hawa gaf take da kamuwa da ciwon barin jiki,matukar bata sakawa ranta dangana da hakuri akan koma menene yake damun taba,babu yadda basi da ita ba kanta sanar dasu damuwarta amma ina Yayah ta kasa fadar matsalar ta,kullum damuwa cin zuciyar ta take,ga barazanar Alhaji Sani da kullum sai yayi mata zazzafan gargadi akan rufe asirin sa.
Su Haj Kubrah hankali ya kara dugunzuma,me yi musu yakin gata akwance ba lafiya,duk wata kulawa da suke bata ada sai suka daina bata,suka bawa banza ajiyar ta,tunda dama badan Allah ake zaune da juna ba,moreni in morekane,to yanzu sunga ta daina mora musu shiyasa suma sukai watsi da lamarinta,abunka da mara yaya tunda take bata taba haihuwa ba,saita sake tagayyara ta futo rana,babu me taimakon ta,kowa yayi biris da ita,hmm rayuwa kenan.
Wannan abun ya sake sanyata adamuwa,tayi kukan rashin haihuwa fiye da wanda tayi abaya,da ace tana da yayanta ta tabbatar bazasu guje taba,ashe dama badan Allah kowa yake binta ba,ashe dama akwai ranar da zasu juya mata baya,ina wannan girmamawar da suke bata,ina wannan tsoron nata da sukeji,duk wannan ya kau daga gare su,fashewa tayi da Kuka mecin rai da kuna,Allah natuba ta daga hannayan ta da suke matukar rawa.
Zuwa wannan Lokacin su Haj Turai hankalin su ya tashi matuka,ganin haryanzu babu wani ci gaba da suke gani,saima aikin su da yake dada lalacewa,a yanzu sai su shafe satittika basuji duriyar D ba,ga su Safna da suka sako su agaba da koke koke,komai saiya sake tsaya musu,kowaccen su takara tashi tsaye dan ganin ta samu cikar burin ta.
Momma jiki saidai ace Alhmdlh yanzu taji sauki sosai,sai tunanin Mijinta daya addabeta,saidai ta buya tayi Kuka ta bishi da Addu'ar samun Rahama,tabbas tayi asarar samun miji gwarzo kamar sa,kaf kayanta D ya kwashe su sabbin kaya ya dinka mata yan gaske,kwalliya Momma kesha yar gaske daga ita sai yayanta,sai Mammi saiko Imti da takeshan gata tako wane bangare.
Yau gaba dayan su suna zaune aparlo,kowaccen su dakaga face dinta kasan akwai damuwa tattare da ita,amma kowaccen su basarwa take kamar bakomai,kamar babu wani abu daya ke damunta.Yayah ce tashigo ta rame kamar ba ita ba,babu wanda ya dago kai ya kalleta yanzu yayin ta ya wuce,taurarin ta sun daina haskawa,gaba daya jikinta saiyayi wani Irin sanyi,hawaye taji yana taruwa a idanun ta,kujerar ta takalla Haj Maimuna ce ta kame ta cokalo wani shegen dauri face dinnan tasha fenti kafa daya kan daya take girgiza kafafunta.
Gaba daya mutanan parlourn zubowa Yayah idanu sukai dan ganin yadda zata dauki lamarin,sunyi zatan za'a kwashi yan kallo,amma Abunda ya basu Mamaki ko kadan basuga wani yanayi a Fuskar Yayah,abunda basu sani ba ita yanzu komai ya sire mata,duniyar tayi mata zafi,bata neman wani mulki da mukami babban burinta ta gyara kura kuranta na baya,shine kwanciyar Hankalin ta.
Samun wajan zama tai ita kadai bata bukatar ko wace irin damuwa,wata Dariya su Haj Turai suka saka, Yayah manyan kasa kin masifar burgeni da kika san daidai matsayinki ayanzu,amma zan miki adalci guda daya na nadaki matai makiya ta,koba haka ba yan uwa,dariya suka sake saki cike da tsokana da rashin kunya,ko kanzil bata ce musu yanzu kam bata da lokacin su,zasu sake magana kenan sukaji karar takun takalma alamun za'a shigo.
Shiru sukai suka zubawa kofar ido jin kamshi mabanbanta a hancin su,sun gaza gane kowanene ke yunkurin shigowa.
Imti ce agaba tasha wanka harta gaji,ba karamin kyau ta karaba kamar ma saceta ka gudu,wani tsadaddan material ne ajikinta, peach color yayi mata kyau matuka,kunsan dai Imti fagen kwalliya ba baya bace kwalliya ta tsantsara a face dinta,hannu da wuya gold ne ke walwali ajikin ta,face dinta dauke da murmushi wani irin taku take kamar Sarauniya, Little ce abayan ta kayansu kala daya kamar yan biyu haka suka tashi.
Zuba musu idanu su Husnah sukai jin wani bacin rai yana taso musu,jin kishin IMTINAN suke a zukatansu bana wasa ba,tamkar su tashi su rufeta da duka haka sukeji,ga wannan shegen murmushin da take sakar musu,Momma ce akarshe cikin shiga ta alfarma, swiss Less ne ajikin ta dark blue yayi mata kyau matuka,da gayya Imti ta zauna ta kashe mata dauri saita dawo tamkar wata matashiya,meji da kuruciya mecin zamaninta,agigice suka mike da sake murza idanun su.
Wani murmushi Momma ke saki wanda yake kara ragargaza zaukatan su,hannun su na rawa suke nunata,hatta Yayah kallonta take cikin tsananin mamaki da al,ajabi,dakyar ta fusgo maganar data makale mata acikin makoshi Aisha ke nake gani kece akan kafafun ki,gyada kai Momma tai eh nice Yayah,komawa tai dabar ta zauna tana kara girmama hukuncin Allah,koda wasa bata taba kawowa aranta momma zata warke ba,saigata atsaye akan kafafunta.
Su Haj Turai sun kasa magana gaba daya ilahirin jikinsu rawa yake,kallon juna suke atsakanin su wanda narasa na menene,gumene ke yanko musu,duk sanyi AC ba jinta suke ba,cikin dauriya da dakiya Haj Kubrah ta kakalo murmushin dole muna murna da rashinki Aisha,dan murmushi Momma ta sake saki nagode Khadija.
Ganin kowa ya zubo musu idanu dan dole suka daidaita nutsuwar su,su Husnah cike da iyayi suke gaishe da Momma da nuna Farin cikin su na warke warta,fuskarta asake take amsa musu,cikin halin girma da dattako irin nata.
Daya bayan daya su Haj Maimuna suka dinga barin parlon,cikin tsananin tashin hankali,duk abunda suke Momma na kallan su, girgiza kai kawai tai batare da tace komai ba,da rarrafe Haj Turai ta kara sa bedroom dinta,wani irin murdawa cikin ta keyi wanda be shirya ba,tuni Hawaye ya gama jike mata Fuskarta,bayan ta fito daga toilet bajewa tai a kasa tashin hankali take ji yana rufto mata.
Fashewa tai da Kuka kamar ranta zai fita,hannayanta duka ta dora akan ta,Samha ce ta shigo da sauri tundaga parlo kana juyo kukan da Haj Suwaiba keyi,agabanta ta durkusa Mom meyasa meki meyasaki Kuka,cikin damuwa take tambayar Mom din nata,banza tai mata taci gaba da kukan ta kamar Allah ya aiko ta baji ba gani,damunta tai da tambaya aharxike tamike zaune Ubankine ya sameni kaji mayyar yarinya lallai saikinji abunda yake damuna,tashi kifita cikin razana Samha ta mike,Mom dinta bata taba yimata tsawa irin wanann ba.
Jikinta asanyaye ta fuce tana wai wayan ta,rarumar wayar ta tayi kamar mara hankali, dealing wata number tai,kamar jira take adaga cikin huci ta fara babbaka masifa,yaron Malam haka mukayi dakai wane irin cin amanane wannan kasan aikin nan akwai ranar da zai warware amma tun farko baka sanar damu ba,yanzu gashi ka samu a masifa,ga matsiyar can da kafafunta kyau da kwarjini tamkar kara mata shi akai,kasa munyi asarar time dimmu.
Cikin kwantar da murya yake bata hakuri ido rufe take kare masa tanadi da zagi na tsamar nama,babu abunda yake sai bata baki akan za'a shawo kan lamarin,kit takashe wayar tana huci,ina wllh bata shirya mutuwa ba dole ayi me yiwuwa yanzuma ta fara jindadin rayuwar ta yanzune take cin Lokacin ta.
Hmmm duniya budurwar wawa.
Mrs Baba Bello Abubakar
.......✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 80_81
Momma bata jima a maine parlo dinba suka mike, Yayah kallon ta take kamar taga sabuwar halitta,wasu daga ciki sun nuna farin warkewar azahiri kamar irin su Haj Kareema ta nuna jindadinta matuka,wadanda basu ji dadinba sun barwa zukatan su amma basu nuna akan fuskokin su ba.
Kamar yadda Haj Suwaiba ta shiga matsanan cin tashin hankali haka su haj Turai suka shiga, meeting na gaggawa suka shiga,sun shafe akalla 2hours suna tattaunawa,kafin su cimma matsaya kome suka tattauna oho,dunguma sukai suka fice amota daya basu dauki driver ba Haj Maimuna ce take tuki suka fice daga estate din gaba daya ko ina zasuje su suka sani.
Yau hakanan takejin kewar Ummeen ta, messing dinsu take ba kadan ba,sam batasan da shigowar saba,kamshin sane kadai ya isar da ita zuwansa gareta,durkusawa yayi agabanta, kyawawan idanun sa ya dora akanta,runtse idanun ta tai saboda kwarjinin sa,haryau ta kasa sabawa da kallon sa,kunyar sa tananan manne a jikinta,gira ya daga mata alamar yadai,raurau tayi da idanun ta, ahankali hawayan face dinta ya fara gangarowa akan kuncin ta.
Tsura mata idanu yayi yanajin kukan ta na taba shi,me akai mata,hannayan ta ya ruko gaba daya ya tasheta, ahankali suke takawa kai tsaye part dinsa yayi da ita,tana manne ajikinsa,hawayanta na sake nunkuwa akan da,kewa takeji matuka tayi matukar kokari shekara 1 da wani abu bataga dangin ta ba,zaunar da ita yayi akan sofa kafin shima ya zauna agabanta.
Tankwashe kafafunsa yayi yana kallonta,cikin sanyi yake dubanta,why Aish kingaji da zama atare danine, lumshe idanun ta tayi,tare da girgiza masa kai alamar àah, menene damuwar ki,shiru tai kamar bazata tanka ba,ina son ganin Ummee da Dad dina,dan murmushi ya saki,kan wannan kike kuka,gyada masa kai tayi alamar eh,ko kinmanta Abba yace sai kinyi hankali zan kaiki,saikin amsa sunan ki na matar Aure,kallon sa tayi cike da rashin fahimta,ido ya kanne mata alamar eh.
Ai dama da hankali na cike da jin haushi ta fada tana hararar sa,yar karamar Dariya ya saki,haryau baki amsa sunan kiba Hajiya,yadda ake kula da Miji sam baki iya ba,dan haka saikin koya zan kaiki,saukowa tai daga kan sofa kwanciya tai ajikinsa tana zubamai sangarta da kukan shagwaba,tuni D ya hau Network birkicewa yayi baki dayan sa,daganan suka lula Duniyar soyayya.
Sàida suka gama shan Love din su,shida kansa ya shirya ta,cikin wata arabiyan gown tayi mata kyau matuka rolling yayi mata tafito das,kananan kasa ya saka sosai suka bada kala,sai murna take yau zasu fita susha iska,yayi mata Alkawarin yau zai fita da ita ta wataya,wajan Momma suka wuce sallama sukai mata, little rigima tasa saita bisu, Momma ce ta harare ina zikije babu Inda zaki bisu kuyi tafiyar ku.
Dafa kan Imti tai da takewa Little gwalo intaga Momma bata kallon ta,sarai Momma raga ni dariya kawai tayi kamar bataga tsokanar da takewa Little ba,Allah yayi Albarka saikun dawo,mikewa sukai tare da ficewa daga parlon Momma,dagashi sai hubbinsa duka fice be yarda guide ko daya ya bishi ba,yakaita gurare da dama har bakin ruwa sedaya kaita,sosai take farin ciki da anna shuwa,garin Lagos ba ruwan wani da wani kowa harkar gaban sa yake yi.
Shopping sukayo sosai kowa da tsarabar sa hatta Mammi da Dad Yusuf sir Ayub babu wanda basuyo masa tsara ba,tafiya suke suna Nishadin su cikin kwarewa yake tukinsa,canza hanya yayi dan Imti ta kara ganin gari yadda ya kamata,titin shirune babu yalwar Jama'a, Imti na gefansa da robar Ice cream ahanun ta,lura da wata mota dakin binsa shine dalilin dayasa ya kara sauri,dan kaucewa koma wane,badan komai ba sai dan Imti baya fatan wani abu ko kadan ya sameta.
Sam bata lura da yadda hankalin sa ke tashe ba labarai kawai take bashi,yadda ya take motar da mugun speed shine yaja Hankalin dan ta kusan hantsilawa,goshinta ya hadu da glass din motar,cikin zafin nama ya taro ta,amugun firgice ta dafe kirjin ta,tuni Ice cream dinta ya kama gabansa,cikin tsoro take kallon motocin da suke bayansu,akokarin su na cimma motar su,wani irin murdawa cikin ta yayi,fashewa tai da kuka shikenan zasu mutu ita da D dinta.
Cikin kwarewa yake zillewa harin su,amma yadda suke da yawa sai hakan ya fara gagarar sa,dan daga mota daya sun kai Motoci biyar yanzu,babban burinsa ya tseratar da Imti,ganin wankin hula zai kaisu dare suka fara harbi a kokarin su na harbin tayar motar sa,hakamma gagara yayi,sun shafe 30mnt suna zagaye amma daya ya kasa cin nasara aka daya, badan da Imti a motar ba tabbas zai tare sune ayi gaba da gaba saidai ayi mutuwar kasko.
Wata bakar motace ta ta falfalo da azababban gudu fit ta tsirewa motar D taka wani mahaukacin birki tayi,kafin ta shawo kwana aguje, bullet aka harbo daga cikin motar gadan gadan bullet din ya tunkaro glass din motar su,idanun Imti nakan bullet din tabbas kan D zai dira,hakan na nufin zai rasa rayuwar sa,cikin ba zata da zafin nama gaba daya ta birkito kansa rungume shi tayi daidai lokacin bullet ya shiga jikin ta.
Mahaukacin birki D ya taka amma ina sakamakon ya kure motar sam kin tsayuwa tayi,atunanin su D suka harba da hanzari suka bace daga titin bat kamar masu layar bata,da kyar ya samu motar ta tsaya,cikin razani yake jijjigata,tare da kiran sunan ta amma ina batajin sa,babu numfashi tattare da ita,jinin daya gani yana kwarara ajikin ta ya kara daga masa hankali, rungume ta ya sakeyi,haba Aish me yasa zaki tare kaddarata,dama kinamin son da zaki Iya bada rayuwar ki asaboda tawa,kuka yake yana sambatu da alamun ya zauce baya cikin hayyacin sa.
Jiniyar motar sojoji ce ta karade ilahirin titin sai guide dinsa da suka take musu baya,zuwa lokacin D baya gane komai da kowa numfashinsa ya tsaya cak zuciyar sa ta kasa dauka,rasa Imti tamkar rasa rayuwar sane,a hanzarce suka fito dasu dan mikasu hospital.
Lagos irland general hospital nan aka mika su cikin gagggawa,tiyata room aka wuce da Imti,babban asibiti ne akwai kwararrin Doctors dan danan suka fara aikin su dan ceto rayuwar su musamman Imti wadda bullet ya shigewa kafada,sàida suka shafe awa uku kafin su fito suna sharce zufa,asibitin cike yake da jami'an tsaro,ko ina ya dauka ankaiwa Darma hari bakowane yasan akwai wata acikin motar ba dan babu wanda yasan Auran sa.
A hankali ya fara bude jigatattun idanunsa,wadanda sukai masa azabar nauyi, kallon room din da yake yayi,tabbas nan ba gida bane tunawa da Abinda ya faru ya mike da azama,jin wani irin zafi ahannunsa shiyasa shi kallon hannun,drip ne daure ahannunsa tsige ruwan yayi,saiga jini ya fara bin hannun sam be tsaya ya lura da hakan ba,fatansa kawai ya ganta,yayi tozali da ita,ya tabbatar cewa da Numfashi a gangar jikin ta.
Da sauri Doctor Obi yayi niyyar da katar dashi kallon da D yayi masa shiyasa shi saurin bashi hanya,ficewa yayi gaba daya ransa ajagule zuciyar sa na kuna,azaune ya hango Momma idanunta yayi jajawur alamar tasha kuka harta godewa Allah. Little ce akusa da ita idanu sun kumbura sumtum,sai Mammi da Dad Yusuf,sai Yayah dake gefe da zungureren carbin ta,"oh rayuwa wai Yayah ce take jan carbi uhm".
Sai su Dd Bashir dasu Alhaji Sani suma suna tsaye curko curko,sai group din su Haj Kubrah karkace fa wai ahautsine suka taho hospital din, àah kowaccen su suttura ce ta kece raini kaibazaka ce akwai wani abu mara dadi daya faru a family dinba,kaini idan idanuna ma ya ganar mun daidai harda wadanda suka fente face dinsu, ba'a barin kowa ya shigo hospital sanin su wanene su yasa akabar su sukai wannan cukowar.
Kowa da fatan dakeyi azuciyar su,musamman su Haj Turai babbar Addu'ar su kar Imti ta farka saga dogon suman datai,fatansu ko zata farka sàidai alahira wannan basu da case da ita,sabanin Momma da takejin wani irin ciwo da daci azuciyar ta, Addu'ar ta daya kar wani abu ya sameta.Allah ya tashi kafadunta,haka little da Mammi fatan da suke kenan hankalin su yayi masifar tashi.
Kallo daya ya yayi musu ya kauda kansa,face dinnan tamkar betaba sanin wani abu waishi dariya ba,tasowa sukai dan ganin fitowar sa,babu wanda ya kalla ya tsaya ya saurara acikin su.
I C U ya wuce anan aka kwantar da Imti ta glass ya hangota har Lokacin kayan da akai mata operation ne ba acanza mata ba,tana kwance kamar gawa sai oxygen dake manne ahancin ta, ahankali ya bude dakin zuciyar sa tana kara karyewa,sonta yana kara narka zuciyar sa,agabanta ya tsugunna idanun sa harwani yaji yake saboda azabar kuna.
Sunzo daidai wajan da bazai iya barin su ba,dole ne wannan karan ya maida martani,bazai taba yadda su taba rayuwar makusan tansa ba,in sun taba shi ya kyale akan wannan bazai kyaleba,mikewa yayi afusace yabar room din baki daya,duk da yadda yakejin jikinsa amma zuciyar sa bazata huta ba face ya binciko masu bibiyar rayuwar sa,saiya gurfanar dasu agaban sa,baya bukatar hukuncin kowa shida kansa zai yanke musu hukunci dai dai da abunda suka jima suna aikatawa agareshi.
Guide dinsa ne suka rufa masa baya,mota aka bude mai ya fada yana maida Numfashi,yana fita yan jarida sukayo masa caaa dasan sanin suwane suka kawo masa hari ayau din,babu wanda ya cewa kala sai yaransa da yayiwa inkiya suwuce a guje suka fisgi Motocin suka hau kan titi.
Lumshe idanun sa yayi yana tuno rayuwar sa tabaya.
Wanene Ziyad Muhammad Muhammad Darma? Kubiyoni a page na gaba danjin wanene shi.
Mrs Baba Bello Abubakar
.......✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 82_83
Asalin iyayan sa 'yan garin jemeta ne fulanine asul,Allah ya yiwa kakan sa Alhaji Muhammad Darma Arziki,yana da gonaki da shanu wanda shi kansa besan iya adadin sa ba,matan sa guda biyu Hajja Mairo da Hajja Zulai.
Hajja Zulai ita ce uwar gida Hajja Mairo Amarya,suna zaman lafiya atsakanin su babu mejin kansu,Hajja Zulai wadda suke kira da Hajja Umma ita ce me yara manya Agidan,yayanta goma cif Zuwaira itace Babba sai Sani,Bashir,Sa'id, Idris,Kabir,Yusuf,Musa,Yahaya,sai Halima.
Sai Hajja Mairo wadda suke kira Mama,danta daya Muhammad data wannan lokacin bata kara haihuwa ba,tsananin son da yake yiwa Mama shine silar da yasa sunan sa data haifi namiji,sosai yakeji da takwaran sa wanda suke kira Baba karami,tun wannan Lokacin su Sani da Zuwaira suka kullace shi ganin shine karami amma yazo yafi kowa fawa Agidan,basa taba nuna kiyayyar su akan sa agaban iyayan su sàidai abayan idanun su.
Nan ya fara fuskantar tsangwama da kyara awajan yan uwan nasa, Mahaifiyar sa Mama tasan Abinda yake faruwa amma koda wasa bata taba nuna cewar tasan basa kaunar danta ba,kullum nasiha takeyi masa akan yaso yan Uwansa ya jasu ajiki wataran Zasu soshi,yana matukar amsar magarta dajin fata aransa inama wataran yan Uwansa zasu kaunace shi,kamar yadda yake kaunar su,yasha warewa shikadai yayi Kuka ya share hawayan sa.
Koda aka sakashi a Makarantar da suke zuwa fir suka hanashi karatu,da yaje makarantar zasu daukeshi akwai wani toilet da babu wanda yake shiga nan suke kulle shi yayi ta kuka,dan dai kawaii karya fisu kokari,amma abanza duka da haka shiyake zuwa first class wannan abu ya kara bakan ta Musu rai,musamman Yayah da takejin cewa ita ce Babba ita yakamata ace komai itace asama,tafi kowa Zuciyar mugunta sai Sani dayake mara mata baya.
Halima tasha tunasar dasu shimafa dan uwan sune amma karshe sai su hada har ita siyi Musu shegen duka,sai dai suyi Kuka su share basu taba gayawa kowa ba,haka rayuwa ta dinga tafiya soyayyar da Alhaji Darma yake yiwa Muhammad tana kara girmama,bayan sun gama primary tsadaddiyar makaranta ya saka su sani,amma shi saboda kokarin sa gwamnati ta dauki nauyin karatun sa zuwa India.
Wayyo ina wuta su Zuwaira su saka shi har kukan bakin ciki sukai sun so ace sune awannan matakin,wannan ya kara taimakawa wajan karuwar ruruwar kiyayyar su akan sa,da kyar Alhaji Darma ya barshi sam baya son rabuwa da dansa,har Airport suka rakashi harda kukan su,Sani da Zuwaira dai kukan bakin ciki suke bawai kukan rabuwa ba,haka suka hakura rayuwa taci gaba da gangarawa,suna kammala secondary school Alhaji Darma yace Aure zai Musu.
Yayan dangin sa su ya Aurawa Yayah wadda sam bataso wannan Auran ba,ita sam bayanzu tayi niyyar yin Aure ba amma babu yadda zatayi.Saidaya kammala University kafin ya tattaro ya dawo gida da tsaleliyar matar sa Aisha,babu wanda yasan Alhaji Darma yayi masa Aure iyayan sune kadai sukasan da maganar banda yayan gidan,ai tunda sani ya kyalla ido yaga Momma yaji kaf Duniya babu wadda yake so kamar ta.
Har zuwa yake ya labe in tana shara ko wani aiki Agidan iyayan su,bangare guda aka ware aka gina mata wajan da zata zauna,hakanan Sani zai kwashi kafa ya tafi ya gaida matar dan Uwansa,ganin abun yayi yawa Alhaji Darma ya taka masa burki,wannan Abu ya sake bata masa rai ganin an katsemai hanyar da take rage zafi da zugin radadin sonta,ita ma gakan yayi mata dadi dan bakaramin takura mata yake da kallo ba, hakanan taji tatsane shi.
Haifaffiyar garin Adamawa ce bafulata ce futuk suna da alaka ta jini atsakanin su shiyasa ma ba'a sha wata wahala ba suka daura Musu Aure itama karatune ya kaita,'yar gatace gaba da baya su biyar iyayan su suka haifa,ita ce Auta shiyasa ake lelenta tako ina.
Momma macece me sanin ya kamata kyautatawar da take yiwa surukanta saita kara siye zukatan su,a Lokacin ne aka yiwa dukkan Mazan Auren hadi babu wanda yace yana so suka wayi gari ammusu Auran dangi,sun masifar shiga bacin rai musamman Sani daya kwallafa rai saiya kashewa Momma Aure ya Aure ta,tunda akace mai Maimuna ce matar sa ya kara fusata,tabbas an cucesa arasa abunda za'a Aura masa sai ragowa.
Sarai yasan wacece ita dan tare dashi suke watsewar su babu wanda yasan abunda suke aikatawa,sai gashi reshe ya juye da mujiya an aura masa ita,abangaran ta ba karamun farin ciki tayi ba dan dama shiya fara lalatata,duk da dama idanunta abude yake ga shegen san kudi kamar tayi sata,satar ma baza'a rasa awajan ta ba,nan zaman lafiya yayi kaura atsakanin su,har yana ikirarin saiya saketa,magana har gaban Alhaji Darma nan ya kafa masa doka matukar ya saki Maimuna bashi bashi,nan ran Sani ya kara baci ya kullaci mahaifinsa.
Dad Yusuf hannu biyu ya karbi batar sa Zainab dama can yana jin sonta furtawa ne Kawai beba sai gashi Allah ya mallaka masa ita,itama abangaran Mammi bata da wata matsala tayi farin ciki da Auran sa,dan mutumne adali me sanin ya kamata,sai sukayi luf babu mejin kansu,suka ci gaba da cin soyayyar su.
Kowanne Agidan aka gina masa inda zai zauna gidane gari guda kaf dangi ne acikin sa babu wani bare da zaka nuna,da wuya kaga sun Auri bare sedai atsakanin su,ganin yadda Momma ta samu farin jini awajan surukanta yasa su Haj Turai suka kullace ta,dan su sam bazasu iya bautar da takewa su Mama ba hauka suke ma dansu suruka ba uwa bace afadar su,sai suka hade kai da Yaya ita ce ta dawo tamkar uwar dakin su,binta suke kamar zasu kwanta mata,yawwa sai Yayah ta kara sakan kancewa ana kara hura mata kanta da yayi girma,tana fadin rai duk inda zataje suna bayanta kamar jela.
Duk da wannan biyayyar na bata musu rai haka suka shanye tunda kowacce da kudurin da yake ranta,bangaren yaya da Sani sun kara dinkewa babu mejin kansu,har wani dakin sirri suka ware wanda babu wanda yasan da wanzuwar sa sai su da sukasan da zamansa.
Wannan lokacinne mahaifin su Alhaji Darma ya bawa kowa jari me tsoka danya tsya da kafafun sa,kudi sun samu sai Sani ya fara facaka dabin matan banza,suma sauran babu wanda ya tattala yayi kasuwancin dazai Amfane shi,tasawa sukai agaba suda matansu suka dinga figar Kaji,abun har gasa ya zame musu yau in wannan ya yanka kaji biyu,to gobe wannan hudu zai yanka,kai wasa wasa sai aka dawo gasar yanka raguna,dan danan saiga Haj Kubrah ambarka kiba bata wasa ba.
Babu wadda take kokarin taro mijinta saima kara ingizasu da sukeyi,akwana atashi sai kudin suka zamo sai ragowa,nan fa fada ya kaure atsakanin in matan suka ce miko suka hana nan fa zakajiyo kansu adaki ana cin uwar sabada.
Hhhhh ci aciki maganin asara
Bangaran Mijin Momma da Dad Yusuf sàidai ace Alhmdlh komai yana tafiya yadda ya kamata,Allah ya habaka arzikin su,garin Lagos anan ya dasa kasuwan cinsa,canji ya farayi dayake yana da manyan kudade ahannun sa be wani sha wahala ba,dan danan sunan sa ya fara zagaye garin Lagos dama wasu garuruwan.
'yan uwan sa babu wanda yasan ya sayi gagarumin fili gari guda,a Victoria Island estate guda ya fara ginawa,ginine akeyi na burgewa so yake yayi musu surprise dayake ya saki bakin Aljihu dan danan gini ya kammala komai na more rayuwa ya zuba musu,mazauna gidan kawai akejira su karaso.
Mrs Baba Bello Abubakar
.......✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
Kulsoom Ismail Idris
Page 84_85
Samun mahaifin su yayi akan komawar su Lagos,sosai ya nuna farin cikin sa da sake hade masa kan iyalin sa da yayi,har kukan farin ciki Alhaji Darma yayi yana yi masa Addu'a,haka iyayan su mata sunyi matukar farin ciki,su Haj Turai sai rawar jiki ake zaa komai dauka,jirgi guda su kadai ne aciki suka sakata suka wala,sanda suka shiga estate din kasa rufe baki sukai,gudun rigima sàida Alhaji Muhammad yasa kowa aka lika sunan sa akofar shiga part dinsa.
Ai Sani ji yayi wani gumin masifa na tsatstsafo masa har yana ina kanin kanin sa yayi wannan kudin,tashin hankali zubewa yayi awajan ya fashe da Kuka,kowa kallonsa ya maida kansa da mamakin me yasashi kuka,saurin waskewa yayi wllh dan uwana ba Abinda zance sai dai Allah ya kara budi Kayi mana Abinda bamu taba zato ba,mungode Allah ya saka da Alkhairi kukan farin ciki nake.
Iyayan su sakin Murmushi sukai da jindadin yadda suke kauna junane su,cikin Murmushi Mahaifin Ziyad ya rungume shi ai jiyayi kamar ya rungumi taransfoma yadda kasan ya daddage ya hankade shi daga jikin sa,amma babu hali haka ya dinga yaken dole zuciyarsa naci sa wuta, Yayah ma na gefe bakin cikin Duniya ya kare mata aka,bata taba kawowa ko amafarki dan iskan nan zai zartasu ba,yanzu ko yayi musu nisan da bazasu iya kamo shiba.
Wannan abu inta tuna yana bakanta mata ranta,haka kowa ya shiga part dinsa,wasu sunji dadi wasu kuma hassada ta gama cinye zuka tan su.Part din iyayan su na Musamman ya gina musu yafi ko ina kyau da tsari a cikin estate din,lokacin da suka dawo Momma nada ciki,wannan ciki yana shan gata awajan kakannin sa da mahaifinsa,Abinda ya tashi hankalin su Haj Suwaiba akan suma sai sun haihu,tako ina suka fara fadi tashi da farautar ciki amma shiru babu wani Labari.
Wata tara Momma ta sunkuto san kacecen danta,kyakkyawa duk wadda ta dauke shi bata fatan ta ajiye shi,gata iya gata ya sameshi awajan kakannin sa da iyayan sa.
Ranar suna ansha suna anyi wadaka shanu haka aka dinga yanka su kamar basu san zafin nema ba,dangin Momma sun so daukar ta,amma ganin yadda Hajja Umma ke kulawa da ita sukaji kunyar rokon hakan daga gare su,sun tabbatar da irin kaunar da surukanta ke mata.Ranar suna yaro yaci suna Ziyad tun wannan lokacin kakansa ya saka masa Darma saboda tsananin kamannin da suke da shi.
D ya taso cikin gata da kulawa tako wane bangare,duk da aciki bakowa ke kaunar sa saboda Allah ba amma sun barwa zukatan su,Alhaji Sani sonda yake nuna masa kamar zai goya shi haka take lelensa,matukar yana gida to yana hannun sa,in Yayah ta dauke shi intaga babu me kallon ta saita gantsara masa mintsini abunka da yaro saiya daina yadda da ita,sam ko ganin ta yaki jini yayi,data miko hannu zai fashe da Kuka sarai ya gane ta.
Abun be mata dasu ba,taso shima taci ubansa kamar yadda ya dingayiwa mahaifinsa abaya,dan dole ta hakura da cewar zata dauke shi. D na girma kyansa na kara bayyana saiya zamto sam Momma batasan fita dashi ko ina,miskiline na gasken gaske da wuya kaga dariya akan face dinsa,in kaga haka to yana tare da kakannin sa ko Momma da Abbun sa.
Wannan soyayyar da ake nunawa D saita kara zaburar dasu Haj Maimuna ganin har wannan lokacin ko batan wata babu wadda tataba yi acikin su,haikan aziman suka tashi suna fafutukar samun ciki,babban burin ko waccan su ta haifi mace,dan ance daka haifi gomna gwara ka haifi matar sa,da wannan karin Maganar sukai amfani da hurawa mazajan su wuta ko sune basa haihuwa,rigima fa kaurewa tai atsakanin su,fadin matan ya zama wajibi atafi asibiti a aunasu asan wanene da laifin sune ko su.
Yayin da Mazan suka ce babu inda zasuje lafiyar su kalau sàidai in sune basu da Lafiyar,sàida Alhaji Darma ya tsawatar akan suci gaba da addu'a, Allah ne zai basu haihuwa sam basu saurari maganar sa ba kamar busa yayi musu akunne,sàida D yayi shekaru 15 sannan suka sami ciki kamar hadin baki,sai kowacce ta fara fankama da kafafa,da jin cewa itace zata haifowa D matar da zai Aura,babu Wadda tasan da kudurin yar uwarta kowacce ta barwa cikin ta.
A wata ranar Alhamis ne aka tashi da tashin hankalin ta suwar su Alhaji Darma,Hajjo Umma,da Mama Mairo,babu wanda beji wannan mutuwar ba,Momma har kwanciya sukai a asibiti tsanar kaduwa,anyi yunkurin kaisu hospital, Alhaji Sani ya shiga ya fita akan tunda sun rigada sun rasu a kyale su Allah ne ya hukunta rasuwar su lokaci guda,haka aka shirya su dan kaisu makwancin su.
Tsahon sati biyu akai ana karbar gaisuwa da yake da abun sai tururuwar shigowa akeyi,dayake mutuwa ce babu wanda aka hana shigowa,masu sata nayi,ba dangin iya ba na baba wasu in suka zo sai sunci na safe sunci na rana sunci na dare sannan zasu hakura su tafi,to washe gari kuwa sassafe zasu kara bayyana,ganin Abun yayi yawa security suka hana shigowa gidan baki daya.
Lokacin da akai rasuwar D baya nan yana Madina nan Abbun sa ya fitar dashi karatu,babu wanda ya sanar dashi rasuwar su sai daya kammala exam din da ke gabansu awannan time din aka fada masa,aiko yasha kuka dan bakaramin san kakannin sa yake ba,haka daya dawo gida aka lallabashi dakyar ya wuce Oxford University anan ya dora karatun sa, pilot Abbun sa ya zabar masa haka yaci gaba da karatunsa cikin hazaka,duk inda ka zagaya akasar babu inda ba'asan D ba.
Zuwa wannan Lokacin su Haj.Mamaimuna sun haihu kuma kowaccen su mace ta haifa,nan fa kowacce farin ciki ya cika mata Zuciya musamman za'ai musu wanka susha kwalliya akaiwa Momma su wai sumzo su gaisheta,karbar su take dan Akwaita da san yara,haka zata zauna tana wasa dasu kamar ita ce ta haife su,hakan ba karamin dadi sukeji azukatan su ba,Haj Maimuna nace ta fara kai Surayya,tunda sauran suka kyalla ido suma suka ara suka yafa,har dambe sun tabaci akan kai 'yayan su ai itace ta fara kai Surayya.
Hakadai suka gama fadan su suka shirya, ahankali sunan D ya fara shahara saiya zamto ya fara boye kansa,yammata kuwa sunsha dambe akansa,ko wacce D,koda ya kammala karatun sa kin dawowa yayi,babu yadda Abbun sa beyi dashi ya dawo ba saiyace akwai wani abu da yake son karasawa.
Samun guide dinsa ya samo asaline gidan marayun babansa, jindadin yadda ya tsaya akan rayuwar su shiyasa suka lashi takobin suma zasu tsaya su kare lafiyar dan sa,tun D bayason bibiyar sa da suke harya hakura ya saba dasu,a wannan Lokacinne ya lura amfara farautar ransa,duk Iya yadda ya zauna yayi tunanin wanene makiyinsa da zai dinga harinsa haka,amma sam ya kasa tunawa shi atarihin rayuwar sa bazai nuna mutum daya yace wannan makiyin sa bane.
Sam baida wani abokin gaba,koda wasa be taba sanin yanada wasu abokan gaba ba,manyan kudin dayake samu saiya zamto harya zarce Mahaifin sa kudi, business yake kala kala,ko ina zaka samu hannun jarin sa,kamar yadda yaga Abbun sa nayi haka shima ya gina gidan marayu sama da guda biyar,kowane gida yara da manya ne kai hatta tsofaffun da basu da galihu sai yasa adakko su adinga kulawa dasu.
Ita ma Momma ta haifi Little ba dadewa da haihuwar su Safna.
Ranar wata Juma'a da bazasu taba mantawa da ita ba,Abbu yasha fararan kayan sa zai tafi masallaci,har bakin motar sa Momma ta rakoshi,yana daga mata hannu tana daga masa,ko 30mint beyi da fita ba,sukaji mummunan labarin yayi hatsari motar ta kine kurmus,gaba daya ahalin sun girgiza,Momma yanke jiki tai ta fadi,haka aka kwasheta sai asibiti,su Yayah haka akadinga suma ana farfadowa.
Wannan bakin Labari yasaka D dawowa babu shiri,yayi Kuka kamar hawayansa zasu kare,yana tsananin son Mahaifin sa,ga Momma da batasan inda kanta yake ba,saidatai sati biyu kafin hawaye ya fara zuba daga idanun ta,da tashin hankali ya hanata tai kukan saidai idanunta sa sukai jajir alamun kukan Zuci take,yan uwanta sunso tafiya da ita,yaya tace sam babu inda zataje tazauna awajan 'Yayanta haka suka tafi babu yadda suka iya.
Hakan yasa D ya sake zama miskili da wuya kaga dariya akan face dinsa,bashi da wani aboki wanda ya wuce sir Ayub shine abkin sa,kuma dan uwansa
Daga wannan lokaci rayuwa tayiwa Momma zafi kullum cikin Kuka take,haka D zai sata agaba yana rarrashin ta,shima daurewa zuciyar sa kawai yake.
Bayan Momma ta gama takaba,nanfa Alhaji Sani ya samu wajan zuwa bini bini ya shige part din Momma,data ganshi zata dinga jan a uziyya dan kallon shedani take masa,tundaga yanayin kallon dayake binta dashi na rukakkun yan Duniya.
Mrs Baba Bello ABUBAKAR
......✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 86_87
Hankalin Haj Maimuna ba karamin tashi yayi ba,har daki haj Turai ta bita cike da kilbibi take kallinta,amma dai wllh Maimuna bansan ke sauna bace sai yau,ashe wayon banza ne dake,ga Mijinki can yana zawarci amma ke nan kina zaune bude da baki,to wllh saidai kiji ana ayyiriri mudai yan kawo amarya ne takarashe maganar ta cike da dariyar mugunta,kinga Turai ya zaki zo har dakina kidinga gayamun magana me kike nufi da wadannan kalaman naki,sake turo daurinta tai gaba,to bari nayi miki dalla dalla tunda ke yarinyar goye ce.
Mijin ki Sani shine yake zawarcin waccan jaja Amaren wllh muddin baki farka ba saidai kijiyo mummunan labari,jabar Hah Maimuna ta zauna,zancan gaskiya kike fadamin kona wasa,natabai miki zance irin wannan to da gaske nake fada miki wannan magana tun wuri kiyiwa tufkar hanci,shiru Haj Maimuna tai tana kallon Turai Wadda take jiran taga yadda zata dauki kamarin,so take tatari Alhaji Sani da masifa harya dankara mata saki uku,tana sane da dama ba son Maimuna yake ba.
Dan muskutawa Haj Maimuna tayi,tare da sakin wani munafikin murmushi wanda yaba Turai mamaki,ya naga kina dariya Maimuna,yo ba dole nayi dariya ba,ai wannan yakin ba nawa bane nikadai ba Turai,yakin mune gaba daya dani daku ahada karfi da karfe amagance matsalar,bangane inda kika dosa ba,kefa ake shirin Aurewa Miji ba niba,yar dariya Maimuna tasaka Turai kenan ai ina tabbatar miki kaf mazajan mu munafukai ne,babu wanda baya sonta acikin su,ke bari na takai ta miki koninan da kika ganni sa Namiji ce wllh da yanzu nashiga layin neman Auranta,sam banga laifin suba babu wanda baya son kyau da tsari,gata yar sawaiwai da ita.
Ya isheki Maimuna ya daga abun arziki zai zama na tsiya,to nikam bata isa Mijina ya sota ba inadarai aduniyar nan Mijina be isa ya karo mun kishiyasa cikin huci Turai ta karasa fadin hakan,anxo wajan matukar ba kyason ta shigo miki Gida matsayin kishiya sai muntashi tsaye,dama atsaye nake Maimuna na sake tsayawa akan kafafuna zakice,fuuu tafice daga part din Haj Maimuna baki daya,yar dariya Haj Maimuna tasa munafukar banza da abanza zakizo ki dagamun hankali kabarni aciki ina kema kije kiji abunda naji,na tabbatar na fiki shiga tashin hankali amma dayake nafiki iya duniyanci aigashi na shanye tashin hankali na,dariya takara sawa kafin ta mike zumbur ta fara zagaye parlonta.
Aranar suka shiga meeting din gaggawa su hudu dama tasu tafi zuwa daya sauran ba wani shiga shirginsu suke ba,awannan daren suka cimma matsaya,washe gari kuwa suka bazama,nanfa suka bude bakin Aljihu,su tsugunna acan su tsugunna anan,ahanyar da wowa daga gantalin su suka hadu da yaron Malam,shine yayi musu tayin uban gidan sa gobe da nisa,babu jin wata dar awashe gari suka nufi nijer aiki yayi musu gagari mi haka suka dawo cikin Farin ciki.
Ance tsafi gaskiyar meshi ba'a shafe sati daya ba Momma ta kwanta jinya,tun tanayi kadan kadan harta dawo ta gagara tashi,daga karshema komai nata daina motsi yayi, hankali fa ya tashi su Mammi babu inda ba sukai Momma dan sama mata lafiya ba abu ya gagara,haka su Haj Turai za'a zo azagaye Momma ana sharar hawaye,harta yaya ta jijjiga dataga yadda Momma ta dawo lokaci daya tasak dawowa yar farat.
Tun suna zuwa duniya daga karshe kowa ya watsar ya fara harkar gabansa,tunda Alhaji Sani yazo ya duba ta sau daya yaga yadda ta koma be kara bi takanta ba,dama badan Allah yake sonta ba danya kashe kwadayin sane,to yanzu kuma yaga abun da ya jima yana hari saiya dauke kafar sa dif.
Ahankali ya sauke ajiyar Zuciya na zuzzur fan tunanin daya gamayi ayanzu,damuwa cunkushe a zuciyar sa.
Cigaban Labari
Gidan marayun sa yasa aka wuce dashi,cikin yara kanana ya shigo ko zasu debe masa kewar halin da yake ciki,takoji sassauci duk minti biyar yana tuntubar Dr Obi danjin jikin Imti yana sanar dashi halin da ake ciki,sai yamma lis ya fita daga gidan marayun katafaran gidan sa dake BANANA ISLAND nan ya nufa gidan daya tsara yadda zasu sha soyayya shida Imti dinsa,gidane estate guda kai saika dauka akasar waje kake,inna ce zan zauna na fasalta muku gidan zan iya karashe Littafin batare dana gama ba.
Wani part ya shiga me Azabar kyau tundaga hanyar shigowa part din grass carpet ne shimde awajan wani kayataccen parlo ya shiga komai blue ne a parloun Saboda yadda na rude mika wuya nake kamar zai tsinke,tunda nake bantaba ganin kayataccen estate irin wannan ba,ma'aikatan gidan kaf mazansu da matansu turawa ne sukadai suke shawagi agidan,aikinsu shine lura da gidan da tsaftace shi kafin mamallakiyar gidan tatako cikin sa.
Wani azababban toilet ya shiga kamar daki haka toilet din yake tsarin turawa haka toilet din yake,abunda ya ban mamaki hadda wata makekiyar plasma a toilet din,can kan wani hadaddan table jarida ce akai,hmm abundai sai wanda ya gani,bewani jima aciki ba ya fito kwakwalwar sa tadan samu sauki na halin da take ciki, yanzu ne tunani mekyau zai iya zama akwanyar sa.
Hospital din ya sake komawa tana yadda ya batta,Asibiti wayam kamar basu ne dazu sukai cincirindo ba,kowa ya kama gabansa,Allah sarki sai Momma da Little da Mammi sai Dad Yusuf dayake ta kaikawo,kusa da Momma ya zauna da take kallon sa cike da tausayawa da kaunar sa,dan murmushi ya sakar mata,sam bayason yaga damuwa a face dinta,hannun sa ta kamo Noor dan Lumshe idanun sa yayi yana kaunar wanann sunan arayuwar sa.
Idanun sane suka ciko da kwalla tunawa da Abbun sa wani abu me daci ya hadiye a makoshin sa,shine wanda yasaka masa wanann sunan shine Momma ita ma take fada masa,tunawa da Mijinta sàida kwalla ta zubo mata,tana kewar sa,tayi rashin miji nagari,tayi rashin gwarzon Miji,kasa daurewa tayi fashewa da kuka tai me taba zuciya,abubuwa sun mata yawa,inta gama da wannan masifar saita fada wanann wace irin kaddara ce wannan.
Mammi ce ta fara rarrashin ta,sam ya gaza rarrashinta sa kalaman bakin sa,kalaman sun kare babu wani dadin baki da zai sakeyi mata,anya yayiwa Momma adalci kuwa,tambayar da D keyiwa kansa kenan.
Shine wanda zai kwana awajan Imti dakin da take kwance zagaye yake da jami'an tsaro karfe 9 ya shiga dakin da take, Numfashinta ya daidaita koda wane lokaci zata iya farkawa,zama yayi akan wata kujera da take gabanta hannayan ta acikin nasa,kallonta yake cikin so da kaunar ta,ze so ace sata farka taga Ummeen ta,saidai sam bazai iya hakan ba,yadda iyayanta suka bashi ita sumul kalau haka zai kaita gare su sumul ba tare da wata larura ba,ya kusa kaita nanda lokaci kadan.
Hannayan ta na cikin nasa bacci ya gara fisgar idanun sa,wajan karfe ukun dare,dara daran idanun ta tafara budewa wadanda sukai matukar yimata nauyi,tuno abunda ya faru adazu,yasata fara zubda hawaye ta tabbatar ta rasa farin cikin rayuwar ta,sunkashe shi shine abunda take ayyanawa acikin zuciyar ta,karfin kukanta ta kara,gaba daya bata tantance akwai wani akusa da ita ba.
Jin Kuka sama sama yasashi bude idanun sa da sukai masa nauyi,dora su yayi akanta bilhakki take kuka,duk sanyin dakin gumi take hadawa,sambatu take wanda ita kanta batasan me take fade ba,sake damke hannun ta da taji anyi shiyasa ta tsagaita kukan ta,in har hancin ta ya fada mata daidai kamshin nan dayake kwantar mata da zuciya,kamshin nan da take marmarin shaka tun tana Imti wanka,kamshin nan da take kaunar mamallakin sa shi take juyowa ahancin ta.
Ahankali ta karkato da kanta inda taji kamshin na fitowa,akansa ta daura idanun ta,wadanda suka matukar azabtuwa jigatuwa da so da kaunar sa,kallon cikin ido sukewa juna wanda basu taba yin irin sa ba,zabura tai cikin tsananin farin cikin ganin sa,jin kafadar ta adaddaure tayi saurin komawa tana och da sauri ya ruko ta,daidai ta mata zama yayi ajikin sa,kallon ta yake farin ciki na zagaye jinin sa,sam ya kasa furta ko wace kalma agareta,Godiyar da zai mata sam harshan sa bekai ya furta ba.
Hade bakin su yayi tare da lumshe idanun sa tarbar mijinta tayi hannu bibbiyu duk da ciwon da yake jikin ta,godiya iya godiya yayiwa Imti saidata zubar da hawayan farin ciki,ji take tafi kowace mace sa'ar Miji,jitai kanta ya dada girma jin irin kalaman da D yake fesar mata,yake fallasa mata asirin ziciyar sa.
Sàida tai sati a hospital kulawa take samu tako ina,a hakan bata fasa waya dasu Ummee ba dan karta gane abunda ya sameta.
Doctor Sera ce ta shigo da fara'ar ta Momma ce agefen Imti sai D dayake can gefe azaune,sai Mammi datake gefan gadon ita ma, Maman baby kana kokari sannu ala raba lpya,kallon kallo akeyi kowa yana san gano wace Maman baby,abun dariya Mammi har daga rigarta take ko itace take da babyn bata sani ba.
Ganin suna kallon ta ta nuna Imti gashinan Maman baby,tsura mata idanu sukai tana zaune sai zare idanu take sam batagane inda zancan su ya nufa ba,amma sun cika sha sha shai abunda Mammi da Momma ke ayyanawa a zukatan su,yarinya dauke da ciki gaba daya babu wanda ya lura acikin su.
D kuwa zubawa Imti idanu yayi ya rasa wane irin farin ciki zaiyi, Momma bakinta kamar zai yage haka take kallon Dr Sera gold din wuyanta ta ciro dan kunne da zoben sai makullin motar da yake hannun ta ta mikawa Dr Sera,hannu na rawa Dr Sera ta mika hannu ta karba cikin tsananin Mamaki,Fuskarta dauke sa murmushi wannan kyauta ce daga gareni ta albishir din da kikai min.
Dr Sera ta kasa magana lallai itako da diro duniya a sa'a,kanta dawo daga hayyacinta Mammi ta zuge jakarta,ita kanta batasan iya adadin kudin data debo ta mikawa Dr Sera ba,nima ga nawa tukuicin,Imti gaba daya ta susu ce suko wannan Family wane irin kudi suke dashi,kyautar miliyoyi basu dauke ta komai ba.
D zubawa Dr Sera idanu yayi tunanin sa shiko me zai bata wanda zaiji aransa tabbas ya bata kyautar da zata faranta mata rai kamar yadda ta faranta masa ransa.
💃💃💃Akwai shagali Imti da ciki wayyo,harna hango su Haj Turai kowane hali za'a shiga kuma oho.
Hmm nima kamata yayi asan dani nime dakko rahoto bekamata su Momma subarni haka ba,koya kuka ce fans.
Mrs Baba Bello Abubakar
........✍️✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 88_89
Zatai Magana Momma ta daga mata hannu basai kince komai ba Sera tukuicin uban gayyar yana tafe,gyada kai tayi hawayen farin ciki na zubo mata,ashe dama haka musulmai suke da karamci,dama sun san darajar dan Adam kamar haka,duk da ba addinin su daya ba amma sun daraja ta,iyayaye da kakanninsu sunsha sanar dasu musulmai ba kaunar su suke,sudin ba akan daidai suke ba,sune akan daidai,ashe ba hakan bane yaudin sun tabbatar mata basu da nuna banbancin Addini ko nuna kabilanci.
Harta juya ta dawo da baya agaban Momma ta tsaya wadda suka zuba mata idanu danjin me zata furta,ina so ku marayimin bayani akan Addinin ku,Fuskar suce ta kara fadada da farin ciki hannunta Momma ta ruko gaba daya kusa da ita ta zaunar da ita.
Kamar yadda kika nema daga garmu yanzu zakiji menen Addinin mu.Addinin mu shine Addinin musulunci Addinin da Allah ya aiko Annabin sa Annabi Muhammad dan ya sanar damu musulunci shine Addinin gaskiya.
Farko ki yadda da Allah cewa babu abun bautawa da gaskiya sai Allah,karki hadashi da kowa a wajan bauta,shikadai yake bashi da Abokin tarayya,sannan ki shaida Annabi Muhammad S A W bawansa ne kuma manzan sane,ki tsaida sallah,kiyi azumin watan Ramada,ki bada zakka,ki Ziyarci dakin Allah,kinga wadannan dana lissafo miki sune rukunan Musulunci.
Nan Momma taci gaba da bata karfafan misalai da hujjoji,aya da Hadisi tadinga jawo mata,sàidata tabbar zuciyar ta sake kwadai tuwa dasan shiga Musulunci,ta gamsu kwarai da gaske saitaji san ma'abota Musulunci ya mamaye zuciyar ta,ita ma tana bukatar tashiga wannan Addini,kallon Momma tayi wani form zan cike dan shiga wannan addinin naku.
Allahu Akhbar suka furta gaba dayansu, Malam Babba ne ya shigo da Dad Yusuf, tambayar su sukai me yake faruwa Momma ce ta kora musu bayani,Ma sha Allah suka furta jin Musulunci zai samu karuwa, Malam Babba ne ya kalli Sera saboda me kike son shiga Addinin Musulunci kin tabbatar ba saboda wane abun duniya ne ya saki jin san shiga Addinin ba,Addinin Musulunci ana so ka shige shi da zuciya daya badan wani kyale kyalen duniya ba,kashiga saboda Allah.
Gyada kanta tayi,saboda Allah zan shiga Addinin ku a bayanan da Maman yallabai D taimin na sake tabbatar da Addinin Musulunci shine addini na gaskiya,ma sha Allah Malam Babba ya furta,take awajan ya lakana mata kalimatush shahada ta maimaita, rungume ta su Mammi sukai saboda farin ciki,wane suna za'a saka miki tace Fatima cigaba dayi mata bayani Malam Babba yayi yadda zata fahimta ahankali zata gane sauran abubuwan.
Take awajan D ya mika mata makullin wani gidansa dake agege,tare da alkawarin kujerar Hajji agareta,tayi godiya harta rasa me zata furta, office dinta suka dunguma dan yiwa Imti gwaje gwaje,cikin wata uku da sati biyu ne ajikin ta,D jiyake inama sukadaine daya nuna mata murnar sa ya tabbatar mata babu wata afadar zuciyar sa ta mamaye komai,ita kanta wani irin farin ciki takeji,zata zama uwa,ta godewa Allah da wannan ni'ima daya bata.
Zata jajirce tayi koyi da Ummeen ta,tana rokon ALLAH karya jarrabeta Kamar yadda ya jarrabi Ummeen ta,ta dinga fama da ita,zata zamo uwa tagari agun 'yayanta,aranar aka sallami Imti Kamar kwai haka sukadinga lelenta,gudun motar ma rageshi akai saboda ita,sanda suka isa estate su Haj Kubrah ana zaune a harabar anashan iska duniya sabuwa agare su, yanzu su suke zuba mulki a estate din yadda ransu ke so.
Zubawa Motocin idanu sukai,jin wata Hassada na shiga zukatan su,tunda Momma tasamu lafiya suke cikin garari,kowacce kaffa kaffa take da Mijinta kar ya kyalla ido yasan Momma ta warke,abunda basu saniba mazajan su basa gaban Momma kaddarar da zatasa ta Auri daya daga cikin su tana neman tsari da ita,fitowar Imti itace taja hankalin su,jikinta yayi wani irin fresh Kamar tarwada haka jikinta ke kyalli,yadda kasan ba jinya tayi ba.
Wani abu suka hidiye wanda ya tsaya a makoshin su,mikewa sukai suna aro jarumta suna yafawa a kan face din su,sannu da hanya suka fara yiwa su Momma fuska sake suke amsawa,sakare sukai suna kallon yadda suke farin ciki sai wani lallaba Imti suke kamar zasu goyata,Abinda ya sake bata musu rai kenan,shikuma uban gayyar yana daga bayanta,duk inda ta cire kafa nan yake dora tasa.
Kai tsaye part din Momma suka wuce hannun Imti Momma ta fada har cikin katafaran bedroom dinta,abakin bed ta zaunar da ita,zauna anan Aysha karki wahalar da kanki, murmushi kawai Imti ta saki kallai wannan da zai samu gata,tunkan yazo duniya anfara tattalin sa, Momma da kanta ta hadawa Imti ruwan wanka,jitake inda da halima da kanta zatai mata wanka,hannayanta ta kama har toilet din ta kaita kafin ta futo taja mata kofa tana kara jadda da mata tayi ahankali.
Parlon ta futo su Haj Maimuna sai yaken dole akeyi,zama tai suka kara gaisawa sam babu wani yanayi atare da ita,sai zallar farin cikin da yake shimfide akan Fuskarta.Haj Kareema ce ta shigo da fara'ar ta zama tai suka gaisa da Momma cikin mutunta juna,ah ina me jikinne zuwa nai na kara dubata da jiki,Allah dai ya kara kiyayewa,karabamu da mahassada da magulmata,da masu fuska biyu,Ameen Mammi ta furta tuni tadauki haske ta tabbatar gugar zana ce takewa su Haj Turai.
Aiko sun shaka kamar idanun su zai fado suke hararar ta,ko ajikin ta batama nuna tasan sunayi ba,an rasa kuma wadda zata tanka,sun san wacece Haj Kareema tsaf zata kwance musu zani akasuwa,shiyasa suka rufawa kansu asiri sukai shiru,toshe hanci Haj Kareema tayi waini mushene ya mutu a parlon nan naki Momma,kallonta suke dan su sam basu ji wani wari ba, Girgiza kai Momma tai kai gaskiya banajin haka nidai har yanzu banji wani wari ba zamana awajannan.
Tabe baki tai nidai naji imma wani ke sakin takashi yana tusa yaje shida Allah dan ba yafewa naiba,haka kawai wata katuwa ta zauna tana fidda cutar cikinta mu tadinga dura mana aciki,shiru sukai babu wanda ya tanka,wani mugun kaikayine ya taso Haj Maimuna agaba babu yadda zatai ta kasa jurewa,banakade zani tai da nufin sosawa jikake wani gunus ya daki hancin su.
Saurin tashi Haj Kubrah tai daga kusa da ita,haba Maimuna aisaikiyi bayani ashe kece ke wanann warin kamar na rubabban kwai haba dan Allah nidai kin dauki hakkina,cike da takaici Haj Maimuna ke kallon ta,kinga Kubrah banason cin fuska daga kunji wari haka kawai sai kice nice ki fita daga idanuna na rufe,inna kifa cikin fusata ita ma Haj Kubrah ta maida mata martani,aiko yanzu za'ai batacciya wllh saidai ayi mutuwar kasko aikin banza,fuuu Haj Maimuna ta bar part din alla alla take tabar part din taje nata ko zata samu damar susa yadda ya kamata.
Binta sukai da kallo cikin al'ajabin warin dake tashi daga jikin ta,da kyar takai kanta part dinta bed dinta ta fada ta warware zani hannu bibbiyu take susa,azaba ta isheta fashewa tai da kuka ta rasa wace irin masifa ce wannan,kamar da wasa ta farajin kaikayi yana dan damun ta,ta dauka abun wasane saiga karamar magana tana neman zama babba,ga shegen warin dake fita daga jikin ta,wani irin ruwane ke zubowa daga gabanta me matukar doyi da wari.
Tundaga wannan Lokacin Haj Maimuna take killace kanta bata yadda ta shiga cikin mutane,duniya fa tayi mata zafi,ko Alhaji Sani bata yadda ya ganta ta kulle kanta adaki, haka Surayya zatai ta bugu amma bazata bude mata ba,dan danan duk wannan jikin nata saiya fara zai zaiyewa dai idanu awaje,su Haj Turai suka abubuwa sun fara jagule musu wani irin kuraje ne suka fitowa Turai a fuska wanda ta rasa na menene,bazama tayi asibiti babu maganin da bata shaba shiru babu wani cigaba.
Alhaji Sa'id da kansa yasata agaba ya kaita asibiti duk yadda aka kai da bincike ankasa gane musabbabin ciwon nata,haka zatai ta susa ga azabar kai kayi.
Yau tun safe azaba ta ishi Turai face dinta ya hadu yayi jajawur kamar tumatur, maine parlo ta futo ta zauna ko ina yayi mata zafi,duk sanyin AC dinnan bata jinta,wani gumi me keto mata,Haj Kubrah ce tashigo hango Turai azaune yasata tahowa wajan ta,turus taja ta tsaya tana kare mata kallo,Turai gobara akai afuskarki ne ko yaya kinga yadda kika dawo cikin Dariya haj Kubrah ta karashe fadar abinda yake ranta.
Akufule Turai ta mike kinga Kubrah banason ciki da wulakanci kamme larura ta saman zaki dingamin dariya,ah kinga daga nafadi gaskiya shine zaki ga laifina wllh naga abun dariya dole na dara,kuma dama ba wani abu ne ya kawo ni ba kudina nazo ki bani,wane kudi kike Magana akai ai banga aiki yaci ba dan haka asara keta kama amma bandani sisi ni Turai bazan biya ba,na cinye na karfine in mace ta isa tazo ta kwata,fadane ya kaure daga karshe aka fara cacar baki da abu ya sake tsamari kokawa ce ta kaure.
Zagin juna suke na rashin mutunci,kamar ba iyaye ne suka haifesu ba haka suka rufe idanu suna zagin iyayan su abundai ba dadin ji. Haj Maimuna ce ta shigo hannun ta aka tana rusar Kuka kamar tababbiya Alhaji Sani na biye da ita yana jinbagar ta da bulala kamar sabon kamu,dan dole suka tsaya da fadan sunga fadan daya ci uban nasu.
Yayace ta shigo har zanin ta na neman kuncewa kai Sani mezan gani kake dukan matar ka metai maka,ina bayajin Yaya daga bulalar hannun sa yayi ya shimfidawa Yayah gaba daya idanun sa sun rufe,yau inbe kashe Maimuna ba shiba dan halak bane,da gudu Yayah ta koma gefe zafin dukan ba karamin ratsata yayi ba,Momma ce suka shigo hankali tashe ganin yakin da akeyi tsakanin Alhaji Sani da Haj Maimuna yana dukanta tana zagin sa.
Dakyar samarin gidan suka ruke Alhaji Sani da zuwa Lokacin yayiwa Haj Maimuna fata fata,gaba daya jikinta yayi rudu rudu sai kuka take kamar ranta zai fita, Surayya na rungume da ita tana Kuka na fitar hankali,Imti na gefe tana kallon ikon ALLAH bata taba ganin irin wanann masifa ba.
Mazan gidan magidanta duk basa nan sai matasa,cikin alhini Momma ke tambayar Alhaji Sani me Maimuna tai maka kake mata irin wanann dukan Alhaji karashe maganar tai cike da bacin rai sam ta tsani taga ana cin zarafin mace,cikin kunar zuciya yake kallon Momma kinga Aisha wanann matsiyaciyar matar ko kasheta nayi ban huce abunda ta jawo min ba, Numfashi ya sauke cikin tafasar Zuciya,wannan Annamimiyar da kike ganin ta, yanzu daga Hospital muka dawo aka tabbatar mun tana dauke da cuta me karya garkuwar jiki wato H I V.
Kamar saukar aradu haka sukaji maganar ta sauka akunanan su,dif zuciyoyin su suka daina aiki na wucin gadi,agidan ubanwa ta kwaso ya karasa furtawa maganarsa na rawa.
Caraf Turai ta cafe ni nasani nasan inda ta kwa so, Surayya ma ba 'yarka bace!!!
Hmmm tofa kaka kara kaka,ana wata ga wata,uhm tashin hankali da ba'a sama sa rana.
Kubiyoni Fans danjin yadda zata kaya.
Mrs Baba Bello Abubakar
.......✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 90_91
Wuta ce ta daukewa Alhaji Sani dama kaf jama'ar dake parlon,Momma kanta hannun ta akirji yake jin yadda zancan yake dukan zuciyar ta,Imti jin jiri na niyyar kayar da ita ta daddafa ta zauna,yuuu akaga Alhaji Sani ya tafi zai zube akasa,cikin azama aka taro shi kamashi akai aka kwantar dashi akan kujera,gaba daya babu Numfashi a tattare dashi,ruwa me shegen sanyi aka dakko a fridge aka zuga masa Numfashi ya kawo, zabura yayi kamar wanda akayiwa allura.
Babu wanda yaga sanda ya dira agaban Turai wata muguwar shaka ya kawo mata,uban wane ya fada miki Surayya ba 'yata bace!! cikin tsawa ya karashe tambayar da yake yi mata ta ruwa akai ana ceton Turai ruko yayi mata bana wasa ba,alokacin Magidanta suka fara shigowa hankali tashe gaba daya Yayah tai musu waya gida ba lafiya,da kyar aka samu ya cika Turai idanun sa yayi wani irin ja meban tsoro.
Kowa haki yake nacin damban da akai na raba Alhaji Sani da Turai,cikin huci Turai ta sake bude baki akaro na biyu bata daddara ba,wllh kome zakayi sedai kayi amma Surayya ba 'yarka bace,ba 'yar halak bace shegiya ce!!! abufa ya girmama cikin tsabar kaduwa Maimuna ke kallon Turai jin abinda take alakantata dashi aina tasan wannan maganar,tabbas nima shaida ce Haj Suwaiba ta furta cike da kara san iza wutar.
Kallon mamaki haj Maimuna keyi musu wasu zafafan hawaye taji suna zuba daga idanun ta,dama badan Allah suke tare da ita bag? Ashe sun jima suna jiran wata masifa ta fada mata? tsahon shekaru suna tare komai tare suke kullawa,ashe yaudarar ta suke,aikuwa bazata taba yadda ya kwana aciki ba,yanzun nan halin kowa zai bayyana,dukkan abunda suka dade suna kullawa tsahon shekaru yanzu saita warware shi,kamar yadda sukai mata sintair abainan nasi suma saitayi musu.
Nan fada ya sake kaurewa kokawa ce ta sarke tsakanin Haj Maimuna da Turai yar tone tone ake na tashin hankali,sàida kunnan kowa ya nemi daina aiki jin abunda suka jima suna aikatawa kaf wani mummunan aiki sàida suka zubeshi awajan, Momma kasa tsayuwa tai akan kafafunta, kallon su takeyi Mamaki na kashe ta,dama tsahon shekarun datai akwance sune sila,sune meta tsare musu,metai musu suka zabi su kassara rayuwar ta,hawaye ke kwarara a idanun ta.
Imti ce ta taso ahankali cikin nutsuwa da aro jarumta,tabbas dukkan bayanan su sun doketa,amma meyasa duk akan duniya suka aikata haka,yanzu wa gari ya waya,gaban Momma ta durkusa neman wanda zata kwanta ajikinsa tai kuka take dama, rungume ta tai tafashe da kuka ta tabbata makiyanta ne,sun tabbata basa kaunarta,yanzu duk azabar da tsasha sune sila,duk da dama haka Allah ya rubo to mata kaddarar ta,amma komai yana da sila,tana tuna irin azabar data sha.
Tana kwance ne kamar bata duniya,mazauna kusa da ita sune ke ganin kamar batajin ko wane irin ciwo,ita kadai tasan metake ji,an wajiga Duniyar ta,an firgita tunanin ta,azabar dataji bata fatan ko makiyinta yaji makamanciyar ta,wani irin zafi ta dingaji ajikin ta yadda kasan ana hura mata wuta haka ta dinga ji,sauran maganganun su bata mata rai suke,sake hautsina tunanin ta suke,fahimtar hakan yasa Imti kamo hannun Momma hakan dama take bukata mikewa tai ko ganin gabanta batayi.
Har bedroom dinta Imti ta kaita,baki ta dinga bawa Momma haka Mammi ta biyo bayan su tana rarrashin Momma,duk da anzalinceta tabbas sun cuceta matukar cutarwa shekaru ta shafe akwance batare da tasan inda kanta yake ba,arude D ya shigo jin abunda ke faruwa a estate dinsu,gefan Momma ya zauna ajikinsa ta kwanta taci gaba da raira kukan ta,bece mata komai ba sai bubbuga bayanta da takeyi alamar rarrashi, ahankali zuciyar ta tafara sanyi jin sanyin zuciyar ta akusa da ita.
Mammi ya kalla alamar tambaya,kora masa bayani tayi dan runtse idanun sa yayi,ya dade yana hasashen dama akwai sa hannun dangin sa,tun sanda suka dakko wanann halittar ya dasa ayar tambaya akan su,ashe sudinne,to me suke nema awajan Momma,meta tsare musu.Imti ya kalla wadda ta zuba musu idanu cikin matsanan cin kaunar su da tausayin su,bayan Ummeen ta da Dad din sai D da Momma Little da Mammi sune mafi soyuwa agare ta,dan murmushi ta sakar masa alamar karfin guiwa,dan kallon ta yayi zuciyar sa na sanyaya a dalilin ta.
Su Haj Suwaiba bayan angama tone tone kowacce ta nufi part dinta,Haj Maimuna zatai nata part din afusace Alhaji Sani ya fusgota gidan ubanwa zakije bazaki sake kwana awannan part din ba kije na sakeki saki,da sauri Alhaji Kabir ya toshe masa baki haba Yaya kar kai abunda zakazo kana nadama daga karshe bekamata ka saketa ba,kabari ayi komai a sannu, gaskiya zata bayyana,alama yayiwa Haj Maimuna ta wuce tafiya tayi ranta bace,babban tashin hankalinta aina ta gogo wannan cutar,.
Fusge hannun sa yayi daga na Kabir afusace ya fice daga estate din back daya,zuciyar sa kamar ta bindiga.Surayya tana zaune tasa Haj Maimuna agaba kan tagaya mata gaskiyar wanene Ubanta da gaske ne ita shegiya ce,cikin fusata Maimuna ta dauketa da mari,karki sake tambayata kibarni naji da Abunda ya sameni Surayya zanyi mugun saba miki.
Tashi tayi ta futa tana kuka yanzu idan ita shegiya ce ina ta kama,ina zata tsoma ranta taji sanyi.
Karfe 8 na dare Alhaji Yusuf ya tara kaf mutanan gidan yaran ne banda su amma daga kan yammata da samari da iyaye maza da iyaye mata wajan dan suma a bun ya shafe su,D ne karshan shigowa face dinnan tayi cidin cidin kamar be taba dariya ba,sam Imti kin biyo su tai tunda taron be shafeta ba.
Taro aka bude da Addu'a Yayah tasha hijab da carbinta a hannu dagaskefa Yayah ba karamin laushi tayi ba,gyaran murya Alhaji Haruna yayi kanine awajan baban su Alhaji Darma,adazu Alhaji Yusuf ya kirashi dan baya gari ya rattaba masa Abunda ke faruwa,shiyasashi dawowa ba tare da yayi shiri ba,kallon Alhaji Sani yayi wanda yakejin kamar ya tashi ya shake Maimuna harsai ta daina Numfashi.
Numfashi ya sauke ya maida kallon sa kan Alhaji Sani,Sani dakai zan fara kome Maimuna ta aikata maka be kamata kazo gaban yayanta kana dukan taba,abunda hakuri bebada shiba rashin sa bazai nada shiba,cikin kufula Alhaji Sani ya kalli shi baffa bakasan abunda waccan muguwar matar ta goga min ba,bayanin abunda Maimuna ta aikata masa yayi,shiru baffan nasu yayi yana girgiza kai Subahanallahi wannan abu beyi dadi ba sam.
Kaganta nan baffa dama can ba kaunarta nakeyi ba ashe ba matar arziki bace ko Mutuncin ta bata kawo min ba,abazawara aka maka min ita ba budurwa ba,cikin kufula Maimuna take fadin kaine babban munafuki,wanene ya lalatani inba kaiba,ko ancema bansan akuyancin da kake yi agari ba,kazama kamar ayu duk inda kaga mace saika bita,ko Aisha ma bansan yadda ka dinga bibiyar ta ba,Allah ne Kawai ya tsallakar da ita daga kaidinka.
Cacar bakice ta kaure atsakanin su sai tone tone suke, Momma tsuru tai tana kallon Alhaji Sani tabbas biri yayi kama da mutum,ashe dama zaryar da yake yimata a part ba dan Allah yake zuwa ba,shiyasa tunda can bata kaunar sa,tatsaneshi matuka ashe binta yake da sharri,kowa zubo masa idanu yayi yana jiran ya kare kansa,amma babu wata kwakwkwaran Magana sai borin kunya da yakeyi.
Zaba masa idanu D yayi duk wata kima da Mutuncin Alhaji Sani suna kwaranyewa daga zuciyar sa,Mahaifiyar tasa yake bibiya, innalillahi yameja ko zaiji sauki aruhin sa,matukar be danne zuciyar saba tabbas zai tashi yayiwa Alhaji Sani dukan kawo wuka,hannunsa Momma ta rike dan gujewa aika aikar da zai iya aikatawa ayanzu,hakwaran sa ya datse saboda tsananin fushi har huci yakeyi.
Da katar dasu baffa yayi ganin suna neman su tashi su doku,dan su abun kunya gaba suka bashi ba baya ba,tsawatar musu yayi kafin suyi shiru suna maida numfashi,ina wadda tace itace shaida, tsulum Turai tace gani,kallon ta baffa yayi kin tabbatar Abinda zaki sanar damu yanzu gaskiya ne,kwarai kuwa baffa bayan nafada har shaidace dani awayata,saurin kallontà Haj Maimuna tayi tashin hankali na rufto mata,gyada kai yayi muna jinki.
Muskutawa tai tana faman susar Fuska amma tsabar Munafurci ya hana taji da kanta,kamar yadda na tabbatar muku na sani to hakanne,Akwai wata rana na shiga part din Maimuna bata parlou,maganar dazan gaya mata awannan lokacin jinake in ban sanar da ita ba bazanji dadi ba,har bedroom dinta na bita bata ciki,jin ana Magana a toilet na karasa kusa da kofar,Abinda naji tana furtawa shi yayi matukar dukan Zuciyata,asukwane na fiddo wayata hannuna na rawa na danna record.
Cikin farin ciki take furta dan Malam Alhmdlh komai yayi daidai kamar yadda asirina ya rufu akan Surayya tundaga wanann lokacin na kara yadda da ingancin aikin malamin ka,ni yanzu abunda yake damuna yawan kirana da yakeyi akan na kawo masa 'yarsa ya ganta,ni babban tashin hankali na karya kwace min yarinya babu abunda nake so.sama da ita dan Malam.
Bansan meya fada mata ba naji tace to babu damuwa zan shiryo asatinnan na kawo mai ita yaganta ko hankalin sa zai kwanta,jin tagama wayar zata futo da sassarfa na fice daga bedroom din, parlou na koma bayan na daidaita nutsuwa ta da rawar da jikina kemin saboda yadda na kadu,duk makircina sainaji Maimuna tafini,lallai dole nayi taka tsantsan da ita,ashe dama munafukace ta dade da sanin yaron Malam sanda muke neman mafita akan Aysha saita nuna lokacin mukafara haduwa dashi.
Sallama na rangada a parloun saigata ta fito saika rantse babu abunda ta tattauna,cikin makirin murmushin ta ta tareni,abunda ya kawoni saina kasa fada mata,gaba daya yake nakeyi adaddafe nadan jima a part dinta, alokacin ne take sanar dani zataje garin su kakarta ta wajan uba,fatan alkhairi nayi mata na baro part din,kunji yadda akai nasan Surayya ba yar Sani bace.
Kuka Maimuna ta fashe sashi Allah ya isa tsakanina dake Turai,asirina arufe bantaba tunanin asirina zai tonu ba,amma saboda Munafurci irin naki sàida kika tonamun asiri banyafe miki ba,daga mata hannu baffa yayi,ba wanann muka nema daga gareki ba maganar data fada gaskiya ne ko yaya,gyada kai tayi gaskiya ne baffa kowa zubo mata idanu yayi,kukan Surayya ne yasa suka maida kallon su kanta Kuka take kamar zata mutu.
Tsanar Mahaifiyar ta ta mamaye zuciyar ta ashe ita din ba kowa bace,face najasa shara me yasa tai mata haka,wanann itace mafi cutarwar da wani mahaluki zaiyi mata,da yawa kallon tausayawa suke mata,wasu kuma abun yayi musu dadi ransu fes,irin su Hajiya Turai ai su yau take sallah.
Cikin Kuka Maimuna ta fara fadin,sanadin rashin Haihuwa ne ya jefani awannan halin,lokacin danaga Aisha ta haihu sai hankalina ya tashi matuka,ganin yadda ake kaunar Ziyad hakan ya tashi hankalina,sainaji babban burina na haifo diya mace danta Aure Ziyad ganin yadda tun yana karamin sa mutane da dama suna kaunar sa,naga yadda kowa yake kaunar sa,sai san haihuwar mace ta dasu a zuciyata,naji duk duniya haihuwa nake so,haikan aziman na fara fafutuka.
Lokacin dana taso Sani da fitina kan dole muje Asibiti a dubamu,haka ya bini bayan duk wasu gwaje gwaje da akaimana,Dr Tayo ya sanar dani Mijina bazai taba haihuwa ba,hankalina yayi mummunan tashi,nan naroki Dr Tayo karya sanar dashi,saboda zai iya sadamuwa aransa har wata cuta tazo ta sameshi,da wannan yaudarar na shawo kan Dr yayi shiru da bakin sa.
A daran wannan rana kasa bacci nayi saidana samo mafita sanann na kwanta na runtsa,awashegarin ranar ne natafi asibiti da nufin aimun dashan kwai asamo ko nawane Namijin nema adasamin ni ba damuwa ta bace indai zan haihu,a hanyane na bige yaron Malam bayan na fito namai sannu,yar maganar damukai dashi yake tambayata kamar ina da damuwa,dan jim nayi ganin bashi da hurumi da matsala ta,ganin ya matsa anan na sanar dashi matsalata,aiko nan ya sanar dani akwai wani Uban gidansa a nijar babu aikin da bazai min ba,har maganin haihuwa zai bawa Mijina.
Cikin farin ciki muka ajiye Magana,aranar na makaman ce Sani akan zanje bikin kawata,harda tsarabar gudummawar sa ya bani,washe gari zakara ya bani sa'a sai Nijer,abunda najeyi daban abunda na aiwatar daban,ai tunda mukai ido hudu da Malam me kankat mukaji wani abu azukatan mu,ganin ba wani babba bane gashi kyakykyawa bazaka taba cewa yana wani aikin malanta ba,amma hatsabibin kansa ne.
Hotel na jashi anan na kama mana daki,karammu ba babbaka muka dinga ci,yadda kasan mijina haka muka dinke,saidai muka shafe sati biyu tare,kafin na tattaro kayana na dawo gida aiko da wowata da sati biyu na fara laulayin ciki,nan fa nadinga iyayi shikuma Sani ya dinga lallabani duk abinda nake so shiyake yimin,wata ranar laraba ina zaune naga kiran me kankat, aguje na dauki wayata na shige bedroom na kullo kofa.
Bayan na dauka yake sanar dani yana sane da ajiyar sa dake cikina yasan da abinsa,naci gaba da kulamai da ita,babu wata damuwa a fuskata na sanar dashi ciki na samun kulawa sosai,bayan wata tara na haifo Surayya kyakykyawa da ita,saboda ni take kama babu wanda ya gano koda wasa ba jinina Sani bace,sai waccan annamimiyar ta wurgowa Turai harara cikin tsananin tsana,ita ko Turai sai murmushi take saki.
Alhaji Sani fashewa yayi da Kuka ALLAH ya isa tsakanina dake Maimuna kin cuceni,kin haifamin shegiya agida to bazan taba zama dake ba,ai wllh matukar Aurena ya mutu suma duk sai ansake su aiba ni kadai na aikata mummunan aikin ba,Turai bari na gaya miki inke wakiliyar shedan ce toni shedaniyar ce da kaina.
Mijin Turai ta kalla Sa'id kaga wannan matar taka bazataga Annabi ba ita da Kubrah da Suwaiba,in kaji Abunda suka aikata kare ma bazai ciba, afirgice suke kallon Maimuna,wani shegen murmushi Maimuna ta saki,kwarai ku kalleni ko angaya muku bansan abunda suka aikata ba,kowa zubowa Maimuna ido yayi suna kallon ta.
Kiyi mana bayani yadda Zamu gane,cewar Alhaji Yusuf dayake binta da kallo,zukatan mazajan su sai bugawa take suna tunanin wane mummunan aiki matan nasu suka aikata.
Alokacin da suka haukace wajan neman haihuwa kamar yadda idanuna ya rufe haka nasu ya rufe,takanas suka nufi India,basu taba zatan wajan malami daya suke zuwa ba,ko nace boka abunda basu sani ba boka daya ne yake musu aiki,abunda akace wannan ta aikata shi akacewa wannan ta aikata,babu imani ba tausayi aka umarce su da su samo jaririya mace sabuwar haihuwa tunda mace suke san haifa,haka suka bazama sako da lungu duk tsaron asibitin kasan matsafinnan ya basu sa'a yadda babu wanda zai gansu.
Haka sukaje suka sato yayan jama'a suka kai masa babu ruwansu da suma iyayan wayannan yaya da wuya suka same su, àah su san zuciyar su ya hanasu su gane hakan,sai wani magani da aka basu kowacce ta zubawa Mijin ta acikin Abincin da zaici haka suka aiwatar,dama can Allah ya kaddara sai sun damu ciki awanann watan gajan hakuri ne ya jasu suka aikata mummunan aiki, hankali kwance suka dawo.
Awannan watan kuma suka samu ciki kowaccen su tayi Murna ita da Mijin ta,haka sukaci gaba da rainon cikin su wata tara suka haihu,tundaga wanann lokacin basu kara farin ciki ba, Kubrah data kwanta zataga wanann jaririyar data sato tana binta babu kai ajikin ta tana kuka da kiran sunayan iyayan ta,haka zata farka tana Kuka ta zama kamar zautacciya.
Kamar yadda Turai tamun labe haka naiwa Kubrah labe,anan naji irin san batun da takeyi cikin Kuka tana bayan gado tana rusar Kuka Masifa ta isheta sai firgitata akeyi,tungada sanan na fara bibiyar su harsai dana gano halin da suke ciki,ita ko Suwaiba ba damar ta zauna sai taji kukan jariri a cikin kunan ta ko ana yimata tafiyar tsutsa haka rayuwa tai zafi agare su,amma duk da haka basu saduda ba,bazama sukai suka koma india,nan matsafin nasu ya tabbatar musu fatalawar yaran da suka kawone daga wannan rana yayi musu tsakani da yaran.
Sai suka sake mike kafa,suka faracin duniya sabuwa,kowacce ta fada farautar D burin su yayan su Aure shi,inta kama daga karshema akasheshi akwashe dukiyar sa,shiru Maimuna tai tana maida Numfashi gumi gaba daya ya wanke wa su Turai jiki,kowaccen su Mijin ta kallon tsana yake mata,wata irin Kunya ce da nadama ta lullube su.
Nadama mara amfani ita sukeji awannan Lokacin,Kuka suke shabe shabe,Inama da basu aikata ba,ina ma basu bi san zuciyar su ba,zasui Magana kenan sukaji an rangada sallama abakin parlon.
Maida kallon su sukai akan kofar,wadanda suka gani atsaye shine abunda ya razana zukatan su tashin hankali yasa suka dinga karo da junan su wajan gudu,gaba daya Yayah kasa gudu tayi da rarrafe ta dinga tafita,haka Alhaji Sani jinsa da ganinsa sun dauke fatansa ya fice daga parlon,kamar anyi yasa haka parlon yayi wayam,sai Momma da D da suke tsaye cikin kaduwa da razani a zukatan su.
Wai shin suwanene wadannan mutanan da kowa ya nemi wajan buya saboda ganin su?
Meya hana Momma guduwa ita D?
Kubiyoni a page na gaba
Mrs Baba Bello Abubakar
......✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 92_93
Cikin rawar hannu Momma ke nuna su da hannun ta ilahirin jikin ta rawa yake,jikin D ta fada ta fashe da kuka,Ziyad mafarkin da nadade ina yine dan Allah karka farkar dani ko agske nake ganin su,shima idanunsa cike yake da Hawaye sakin D din tai ta sake maida kanta bakin parlon suna nan atsaye Fuskar su dauke da Murmushi,a hankali ta fara takowa Zuciyar ta na sake raunana,hawaye na zarya akan kuncin ta,gaban Mama Mairo ta tsaya wadda take kallon ta cike da so da kauna.
Rungumeta tai suka fashe da Kuka tare,Mama dama baku mutu ba meyasa Kuka boye kanku,taya akai kika rayu bayan an bunneki Mama,tarin tambayoyin da Momma ke jefo mata kenan, Murmushi take hawaye na zuba a idanun ta,shafa kan Momma take amma sam ta kasa magana,kallon Abbu tai wanda yake binta da wani Irin kallo,kallon so da kauna kallon nayi kewar ki.
Ahankali D ya tako Zuciyar sa aranane rungume Abbun sa yayi,wani abu da yayi shekaru a makoshin sa sai yau yaji ya fada,hawayan farin ciki ne ke silmiyowa daga idanun sa,Abbu ya furta a hankali cikin so da kaunar Mahaifin nasa,kallon Abbun yake kamar wanda aka kara nasa kyau duk da yayi rama amma kyansa yana nan,kallon Mama yayi data bude masa hannu alamar ya taho,matsawa yayi ya rungumeta,Darma ta furta cikin karayar zuciya fashewa tai da kuka tunowa da mijin ta,abun santa farin cikin ta,amma ayau din babu shi suntafi sunbarta.
Inama bata tashiba ta bisu,tanajin daci da ciwo aziciyar ta,daya bayan daya suka dinga dawowa fuskokin su dauke da mamaki da al'ajabi,kowa ya hallara banda Alhaji Sani tun ya cikawa wandon sa iska,sai yaya da take rawar dusko gaba daya fuskarta ta jike da Hawaye,zama sukai suna sake kallon Abbu da Mama da suma.su suke kallo,ina Sani Mama ta furta ahankali sai lokacin kowa ya lura da babu shi awajan.
Dan murmusawa tai dama tayi tunanin haka,kallon D tayi akawo munshi gabana cikin mintuna biyar,tofa nan aka fara kallon kallo jin abunda Mama ta fada,waya D ya dakko maganar minti daya yayi ya aje wayar,abunda be gaza mintuna uku ba saiga Alhaji Sani an cukui kuyo shi aka wani guide gansameme ya dakko shi,sai daya dire shi agaban Mama tukunna ya juya,zuba masa idanu tai wani kallo take masa wanda kowa ya gaza fassara shi,hatta D kallon Mama takeyi gaba daya kansa ya kulle meya aikata mata haka.
Duk hakuri Irin na Mama amma yau nina fushinta take afili,maida kallon su sukai kan Alhaji Sani wanda yake zazzare idanu,idanun sa kamas babu wani alamun nadama tartare dashi,sai zuciyarsa ma datake tafasa na dawowar makiyansa,tabbas sun shammace sa,amma taya akai hakan ta faru,ya akai suka tsira da rayuwar su,shine abunda yake san ji daga gare su.
Sani Mama ta furta tana kallon sa,kasa kallon ta yayi saboda kallon tsana dayake hangowa acikin idanun ta,dan murmushin takaici ta saki inaso kai musu bayanin taya kakashe mu nida iyayanka,wanda harni kayi tunanin kakashe sai dai kash,kamanta babu wani bawa daya isa ya cutar dakai dan uwansa face Allah ya rubuta hakan gareshi,da sauran shan ruwana agaba ba haka kaso ba ko? Jefo masa tambayar tai tana kallon sa.
Kaf parlourn babu wanda be shiga rudani ba,kowa ya zaku yaji abunda Sani zai furta,muskutawa yayi cikin bacin rai da tafasar zuciya.Kamar yadda kika fada tabbas nina kashe iyayena,tsit parloun ya kara dauka kowa ji yake kamar kunnan sa be fada masa daidai ba,gyada kai yayi alamar tabbatar wa,badan kuma komai na kashe su ba sai saboda wanann dan naki,ya nuna Abbu cikin matukar fusata tsanarsa karara take kwance a idanun Alhaji Sani.
Zuba masa idanu Mama tai tanajin wani daci azuciyar ta,nafara tunanin kashe iyayena ganin yadda suka dauki son Duniya suka daurawa Abbu,nine Babba amma gaba daya sai aka maidani ba komai ba,tun muna yara nakejin dacin hakan,komai ya taba sai Allah ya saka masa Albarka,niko komai na taba saiya kare,hakanne ya kara ruru wutar kiyayyar sa azuciyata.
Sanda na kyalla idanu naga zukekiyar matar daya Auto nan ma sai raina ya sake baci,wai meyasa Muhammad yake fina komai,meyasa komai nasa na musammanne,meyasa ni bani da sa'a arayuwata,babu wani abu da Darma yake yabata akai daidai komai yace nayi koyi da dan uwana,in yana futtamun wanann magana kamar yana watsamun dalma haka nake ji.
Duk wata hanya da naso jan ra'ayin Aisha sai hakan bata samu ba,akai rashin sa'a ma babu wanda taji ta tsana sama dani saboda irin kallon da nake mata,sandana fuskanci ta tsaneni hankalina yayi mummunan tashi nayi Kuka awanann rana ganin abar sona ita tsanace karara kwance a idanun ta.sanda aka takamun burki da shiga wajanta har Zazzabi nayi na tashin hankalin rabamu da akai.
Kwatsam aka auramun Maimuna dama abokiyar watsewa tace,abunda nayi niyya nagama cin moryarta na zubar da ita,saidai kash wancan tsohon ya kakabamin Auranta da sharadi me zafi akanta,awanann lokacin na sake kullatar sa,sanda Muhammad ya kawo mu wanann estate kadanne ya hana Zuciyata ta buga,saboda tsabar bakin ciki da hassada data cikamin zuciya.
Sanda Aisha ta haifi Ziyad sai naga soyayyar dayake wa Muhammad ya ninka ta akan dansa,abundaya girgizani can cakat ya dauki sunan sa ya manna masa wato Darma,nan ma nayi bakin ciki matuka daga wanann lokaci na dauki kudurin sai yabar Duniyar nan tako wace hanya na dinga tunanin taya zan gashesa cikin sauki ta yadda babu wanda zai gane.
Wata rana ina zaune a office dina kawai sai naga tsaka wata katotowa ta fito tana shawagin ta sainaga wasu jarirai guda biyu suna biye da ita,kura mata idanu nayi ina tuni irin dafin da take dashi, Murmushi na saki na samo hanya mafi sauki,da azama na tashi fridge dina na bude bana rabo da nono kindurmo cikin wani boket na dakko ta sai tashin kamshi take,indanaga tsakar nan nabi anan na ajiye kindurmone.
Aiko kamar sunsan shirina sukaci suka dinga sa baki suna lasa,abunda yaban mamaki saina gansu suna tafitowa ashe dama akwai inda suke rayuwa a office din sam bansan dasu ba,akalla kusan guda bakwai ne suka fito suka kewaye nonon suna lasa,sàida suka gaji dan kansu sukabar wajan,wata guda daya ce akai rashin sa'a ta fada ina kallon ta banyi yunkurin curo ta ba harsai data mutu.
Tsam matashi daga wajan zamana,cireta nayi daga ciki na wulla ashara,fura na dakko na dama na zuga suga na kara maida ita fridge yadda zatai kara sanyi,ina tashi daga office gidan na nufa,kai tsaye kuma part dinsu na wuce ina sakin fara'a,suna zaune shida Umma suna hirarrakin su,zama nai mukai gaisa suna tambayata ya aiki,ina Alhmdlh cup din dana shigo dashi Darma ya kalla,Sani meka zo mana dashi haka nakejin kamar kamshin mutuniyata,fuska sake nace aiko itace.
Mika masa nayi ya karba da Farin ciki yana samun Albarka,sainaji jikina yayi sanyi kamar na fasa kudurina,amma sai naji ina gwara dai ya kauce ya bani waje,Umma ce tai caraf nima zansha,saidanaji wani dum a Zuciyata Allah ya sani ina kaunar mahaifiya ta kamar na hanata sha,saina tuna itama tana kawomun cikas a al'murana bishi dama mijinkine kwa hadu acan,da kaina na dakko musu cup na zuba musu,sunan sha muna hira,hirar da basu taba zama dani sunyi ba sai gashi aranar suna jana ajiki.
Har tayi sukaimin nima nasha,na nuna musu aini nasha tawa,ko minti biyar basiyi da gama shaba suka shiga wani irin mummunan yanayi,tun suna zaune har zaman ya gagare su dafinta ya fara zagayawa ajinin su,hannu suke mikomin na taimake su amma ko kadan banji tausayin su ba,suna cikin wannan Halin Mama ta fito daga dakin ta aguje tataho garesu,jatai ta tsaya tana kallon a cike da tuhuma,afirgice nake kallon ta gaba daya na manta da ita,hanyar kofa tai danta sanar akawo musu dauki cikin zafin nama na damkota fitarta waje na nufin tonuwar asirina.
Gaba daya sam bata fahimci ina da hannu akan abunda ya same su ba,cika ni mana Sani naje kira sauran adauke su akai su asibiti,cikin rudu da tashin hankali take fadin hakan,dariyar dana bushe da ita shine dalilin dayasa ta dago tana kallona,cikin firgici da mamaki,dariyar me kake Sani? wata dariyar na sake bushewa da ita,Maryama kenan kina tunanin zan barki kifita ki tona mun asiri,ina tabbatar miki kamar yadda na kashe su kema yanzu zan kashe ki,dama mijin ku daya kinga acamma sai ku kara jonewa nakarasa fada ina dariyar mugunta.
Hawaye ke zuba afuskar Mama kallo na take bakinta na rawa,meka aikata musu wannan ce sakayyar da zakai musu,wannan ne tukuicin da zaka basu na haihuwar ka da sukai,wannan ce tukuicin kaunar da sukai maka,dakata!!! nafurta cikin fushi wace kauna suka nunamin,wane gata kike magana akai,danki kawaii suke so shi kadai suke kauna,sakamakon zunubin da suka aikata ba san makiyina wannan shine tukuicin su,duk da ban so na hada har tsohuwa taba kwadayine ya jamata.
Kema yanzu bazan barki ba yanzu zaki bakunci lahira,sake yunkurin guduwa Mama tai,tsatstsauran ruko yayi mata,ba karfin su daya ba,haka ba shekarun su daya ba,jikin girma ya fara bayyana atare da ita,Inda Mijinta yake da abokiyar zamanta ke yashe ta kalla zuwa lokacin babu rai tattare dasu,fashewa tai da kuka kallon tsana Mama ta dinga bina dashi a wanann lokaci,ta karfin tsiya na dura mata kindurmon da suka sha,amma tsabar taurin kai ko gezau banga tayi ba.
Afusace na dakko filon kujera na danne mata hanci babu ta yadda zatai tai numfashi,harse data daina motsi na kyaleta,saidana duba na tabbatar babu me rai acikin su,dauke ragowar furar nayi motata nakai ta,kafin na dawo na goge duk wata shaida dazata nuna nine na kashe su, hankali kwance na fice daga part din babu wanda yasan da shigata,wannan abu yayi min dadi,kai tsaye part dina na nufa raina fes nahaye bed dina lokacin dare yayi nisa sosai.
Asubar fari na dinga jin koke koke a firgice na fita aijin labarin rasuwar iyayan mu lokaci guda har suman karya nayi,ana yayyafa mun ruwa ina sake komawa,ba suman komai nake ba saina farin ciki,yanzu sai target dina na gaba,indai na kashe Mahaifina ban kashe Muhammad ba aita banza nayi.
Bayan anyi arba'in na fara sakawa da kwancewa sam na gaza samun matsaya,kai har akai shekaru kusan uku ina bin hanyoyi dan ganin bayan Abbu amma abu ya faskara,tunawa nai da Zuwaira tabbas nasan kaidin mata,tunowa da wanann ayar ta Alkur'ani inna kaidu hunna Azim,aise naji kwarin guiwar tunkarar Zuwaira.
Sanda nasameta tana zaune aparlo tana kada kafa,Saboda aduniya tana son mulki haba ainan na fara wasa Zuwaira tuni kanta ya kara girma tana hura hanci, azuciyata dariyar mugunta nake mata.Sani nasan wannan kirarin ba'a banza ba,me kake so me kake da bukata ni kuma ayanzu nai maka shi, murmushi ya sake saki,kafin ya muskuta ya gyara zama,ni Zuwaira sai naganki kamar kina cikin damuwa,kara sanja fuska tai kamar kuwa kasani,akan mijin waccan faratun ce,ko bata fada ba nasan wa take nufi,Anzo wajan dama abunda yake sonji kenan,me kuma yayi miki,jijjiga kai tayi babu wani abunda yayi min kawaii Inajin haushinsa acikin zuciyata.
Bata rai Sani yayi tabbas nima Inajin haushinsa Zuwaira,kuma wani abu da baki sani ba akwai wasu makudan kudin mahaifin mu ahannun sa,amma kinji yayi shiru da'alama ya cinye,shiru yayi yana kallon yadda tadauki maganar,aiko tuni yaya tahau dan lamarinta da kudi ba sauki,sai hura hanci take,dariya ce takecin Sani kallon sa tayi afusace tawace hanya zamu karbo kudin mu,ta hanyar mutuwar sa,saidata dago ta kalleni arazane jin na ambaci mutuwa.
Ganin zata kawon cikas na dinga kalaman ceta dayi mata dadin baki,shiru tayi na wani lokaci kinga Zuwaira matukar ya mutu Allah kadai yasan irin arzikin da zami,dama naji maganar wata kwangila dayake zata shigo kwannan ta biliyoyin kudi shikenan zata zama tamu,duk wata hanya da nasan kayannan su dawo hannun mu Zanyi,jin maganar mahaukatan kudade yasa Yayah gyara zaman ta.
Indai wanann ne ba matsala bace,dama Inajin haushinsa,ga kuma haushin matar sa saboda tafi kowa Kyau agidannan,dariya ya saki Zuwaira kishi nidai ba wannan ba,menene shawarar ki,ni sharata guda daya akwance masa birkin mota yadda sai sun hau kan babban titi su casa tsayawa duk yadda za'ai kuwa.
Cikin farin ciki nai ihu na rungume Zuwaira ina dariyar murna,gaba daya banyi tunanin wannan hanyar ba,kibar sauran aikin a hannuna,amma da sharadi bakinki kanin kafarki kija kisamai zip din karfe,ai basai kafada ba Sani,ficewa nai daga part dinnata,aranar na samu wani amintacce acikin yarana,acikin motata na dakko shi babu wanda yasan dashi saini,saidana tabbatar idanun mutane ya dauke sanann nace ya fito,motar da nakeson aiwa aikin na nuna masa,cikin kankanin lokaci ya kammala aiki na sallameshi.
Tunda na idar da sallah nake zaune a parking space,ina jiran naga wace mota za'a wanke masa,ganin wadda nasa aiwa aiki ita zai hai zuciyata fal natashi nakoma part dina,kwanciya nayi na mimmike agado ina birgimar farin ciki,ko sallar Juma'a kin zuwa nai ina zaune ina jiran saka mako,aiko bandade ba kyakykyawan sako ya meni na mutuwar sa, mummunan sako akunan maso yansa,nafi kowa nuna tashin hankali na,nai kuka nayi azuciyata nadinga tsinewa wannan aikin banza da aka sani,bagaira ba dalili na bige dayin kuka.
Dago jajayan idanun sa yayi yana dakkon Abbu da Mama,amma sai gashi rana katsam kun dawo duk wahalar danai kuna nufin tatashi abanza,ubamme nene ya hanaku mutuwa,wane dan iskanne ya taimake ku ya tsallakar daku daga kaidina,wanene shiii ya furta cike da amonsa na wadanda zuciyar su ta gama kekashewa,babu nadama ko dana sani,babu rahama atattare dashi.
Kowa kallon sa yake da kaduwa da tashin hankali,haj Maimuna duk mummunan aikinta sai taji ashe ga Babanta,ko giyar wake tasha bazata iya kashe iyayanta ba,iyayan nan da sukai dawai niya da ita,iyayan nan da suka nuna mata gata,iyayan nan da babu meson ciganta kamar su,saiga mijin ta shi ya rufe idanun sa ya akshe nasa,anya befita aikata zunubiba,acikin su wanene jakadan shedan?
Cakwakiya kenan.
Haryanzu fa zuciyar Alhji Sani a kekashe take,tariga ta bushe babu imani kokadan,Allah ka rabamu da keka sheshshiyar Zuciya.
Mrs Baba Bello Abubakar
......✍️✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 94_95
Maimakon su bashi amsar maganar sa,sai yaga suna sakar masa murmushi abunda ya daure masa kai kenan,Mama ce ta kalle shi Sani kenan kadauka kaikadaine me kwakwalwa,to kaima da kake da kafurar zuciya ka iya wannan wasan balle mu,kaika buga wasa amma tsarawar tamu ce,ware idanun sa yayi a kanta gyada masa kai tayi alamar tabbatar wa.
Tun Sanda kuke matasa kafin kuyi Aure na dade da gano baka kaunar dan uwanka,baka sonsa kwata kwata,inna kalli cikin idanun ka babu abunda nake gani sai zallar kiyayyar sa,tundaga wannan lokacin nafara bibiyar ka,tabbas naji araina akan kiyayyar sa zaka iya kisa.
Amma bantaba kawowa koda wasa wannan kiyayyar zata shafi iyayanka ba,har kayi yunkurin kisan su,tabbas awannan lokacin ka shammace ni,wadanda nake lissafin zaka iya kashewa babu su aciki amma tabbas nima nasa kaina ina daga cikin wadanda zaka iya kashewa dannima ina cikin makiyan naka.
Sanda kai yunkurin hadawa haddani a wadanda kakashe atunanin ka,to ban mutu ba dogon suma nai,bayan an gama hadamu zaa kaimu abinne mu,awannan lokacin numfashi na ya dawo gaggar jikina,jina adaddaure kamar huhun goro gashi antomun hanci da kunne sai hankalinka yayi mummunan tashi,atunanina ma har an binne ni batare dana farka ba,hakan yasa wasu zafafan hawaye suka fara sintiri a fuskata, dagaske dai nima lokacin mutuwa yazo.
Jin anshigo ya sani dan motsawa,akan idanun Yusuf da Zainab na motsa da azama suka tsugunna agabana,bude fuskata sukai mukai ido hudu dasu,cikin farin ciki suke kallo na, Mama dama baki mutu ba,babu bakin magana sai binsu nake da ido,da sauri suka kwance ni mikewa Zainab tai da nufin taje taiwa sauran albishir caraf na rike hannun ta,juyowa tai tana kallo na girgiza mata kai nayi alamar kartaje idanuna har Lokacin be daina zubar da hawayan rashin mijina da abokiyar zamana ba,tare dajin zazzafar tsanar Sani araina.
Ya yanke min rayuwar jindadi,da farin ciki,rabani da Darma kamar ya kasheni da rainane dan nasan bazanji dadin Duniyar nan ba,amma na godewa Allah daya tasheni zannunawa Sani kamar kwakwalwa ce dashi,duk da yake Namiji nima Zanyi amfani da baiwa da basirar da yamin ta mace,zan tabbatar masa da mata ba kanwar lasa bane suma Allah ya basu tunani da hangen nesa.
Kallon Mamaki sukeyimin ganin yadda nake Kuka bilhakki da girgiza musu kan alamar karsu sanar da kowa,Hankalin sune ya tashi matuka suka tabbatar da akwai gagarumar matsala,jin alamun za'a shigo yasa su saurin lullube ni batare da sun tashi daga gabana ba,alokacinne kashigo kana kukan munafurci har wani faduwa kake kana tumami ana baka baki kayi hakuri,awannan lokacin ji nake Inama na mike na tona maka asiri,saidai hakan baida amfani ba yanzu zan kama ka ba.
Yusuf da kansa ya dauke ni ya sani amotar da aka saka mijina da abokiyar zamana,sabida inda za'a binne min akwai nisa,shima amfanin yaye da hikimarsa,akwai wani abokin kakan ku a ABUJA shi Yusuf ya kira dan ya bashi shawarar ya za'ai,sai akai sa'ar yana Lagos din yazo wata ta'ziyya,kuma makanarta daya za'a kaimu,hikimar da sukai babu wanda ya lura gawa biyu aka fito da ita daga motar,da aka hada da wancen sai suka zamo gawa uku.
Dayake ansan juna da wadan can sai kowa yayi zatan dan tasa jana izar aka dungumo haka,su namu suna zatan mu uku aka abinne hardani,su kuma wadancan suna zatan gawa biyu har tasu gawa uku kenan,haka akai abunda ya dace nikuma ina mota ina hangen mijina,toshe bakina nayi jin yadda Kuka yake zuwar mun gudun kar wani ya jini yasa na kunshe kukana.
Kai tsaye Yusuf da wannan Aminin mijin nawa motar suka dawo babu wanda yace kala sukaja motar,ba estate suka nufa dani ba,Banana Island suka nufa dani wato gidan D,acan na samu Zainab tana jiranmu,rungume ni tai tana sakin Kuka haka ta kamani har toilet ta kaini nayi wanka,ina futowa ta bani kaya na saka zama sukai suka zagayeni dan jin tabaki na.
Shiru nayi na sunkuyar da kaina maganar tanayimin nauyi akan harshe da baki,dago jajayan idanuna nai na zubasu akan 'yayan nawa nan na labar ta musu dukkan abunda ya faru,sun girgiza matuka,sun tabbat da Sani baida imani ko kadan baida tausayi,yanzu ya za'ai Mama Zainab ta tambayeni cikin rawar murya, murmushi nadan saki,abinda za'ai Zainab wannan ya zamo sirri atsakanin mu banason kowa yasan cewa inanan da raina ban mutu ba.
Zanbar kasar nan gaba daya,amma kunne na yana nan duk wani motsin Sani kune zaku dinga sanar dani ta hakanne zamu gane mene shirinsa na gaba,gyada kai sukai alamar sun amince,duk da nasan Zanyi kewar Aisha da Mijinta da jikana D amma haka na daure,a washe garin ranar nabar kasar nan na tafi Misrah acan nai zamana har nagama taka ba.
Duk wani motsin mutanan gidan yana dawowa kunne na,kamar yadda yayi amfani da Zuwaira haka nima nai amfani da ita,batare da yasan dawa take mu'amala ba na sanar da ita,sonake duk motsin dan uwanta Sani ta dinga sanar dani,tanemi sanin wacece ni na tabbatar mata bata da hurumin tace seta sanni kudi take nema kuma zata samu.
Mahaukatan kudadan dana ambata zan bata shine yasa Zuwaira ta manta da duk wata abota da Amintar datake tsakanin ta da sani,yadda nasakar mata bakin aljihu nima saita sakar min bayanai har ranar dayazo neman shawarar yadda za'a kashemun dana,kodata fadamin abunda ta gayawa Sani hankalina ya tashi,cikin gagawa na sanar da Yusuf duk yadda zaai kar Abbu ya shigo wannan motar,ya tabbatar min hakan bazata faruba,kuma.zai dawo gareni muzauna tare.
Zasu nunawa Sani aikin sa ya kammala,hakan kuwa akayi,a ranar Yusuf hanashi shiga motar yayi yace atasa zasuje masallacin,daya dagacikin guide din D ya nema yaja wannan motar da aka kwancewa burki,amma ya tabbatar sannu ahankali yake tafiya kuma karyayi tafiyar data wuce 30mnt,cikin bin umarni ya amsa yes sir,jan motar yayi ya fice daga estate din.
Hakan daya umarce shi ya aiwatar fita yayi daga motar, ba'a da zabi wanda ya wuce akonata,wuta aka saka mata ganga ganga ta dinga ci,awannan time din sako ya same ku Abbu yayi hatsari ya rasu,gaba daya besan abinda ya faru ba dan danan yaji gari ya dauka da labarin mutuwar sa abun ya Matukar daure mass kai,kallon Yusuf yayi akan yayi masa karin bayani mene yake faruwa,bebashi amsa ba har ya kawo shi gabana,lokacin na zo nigeria kuma a Banana Island na sauka.
Sanda ya ganni zaucewa yayi dan yayi zatan fatalwa ta ya gani,nan na tabbatar masa da cewa nice saida nayi masa bayani hankalin sa ya kwanta,yasha kuka jin dan Uwansa ne ya aikata musu haka ya kashe iyayan su,anan na sanar dani zai dakko Matar sa da yayansa,na nuna mai àah in yayi haka zai bata mana wasa ya barsu acan suna tare da kariyar ubangiji.
Sanda Aisha ta kwanta ciwo komai tana zuwa kunnan mu kuma hankalin mu ya tashi matuka,kuka Abbu zai sani agaba yayi ta rusamun nima ina taya shi kan na barshi ya bayyana kansa cewar be mutuba sam naki yadda da hakan lokacin hakan beyi ba, Zainab tana yiwa Momma vidio ko Yaushe muna tare da ita,haka D da Little muna ganin Abunda yake aikatawa.
Sanda muka ganshi tare da wanann yarinyar munyi farin ciki matuka,da Yusuf yayi mana bayanin Matar sace,yanayin yadda ta dinga kulawa da Aisha sai hakan ya dasa mana kaunarta matuka azukatan mu,dukkan wani shiri da sukai akansu muna sane min kyalesu ne ganin zasu saukaka mana hanya,atunanin su ba Matar sa bace karuwar sace,sunyi amfani da kwaya me karfin gaske wadda zatasa ya kasa control din kansa,atunanin su zasu yi amfani da wanann vidion su bata masa suna.
Kamar yadda suka shirya tsaf haka muka shirya,Ayub da Zainab su sukai mana wanann aikin,afakaice nasa ta gyara yarinyar yadda abun bazai mata illa ba har ya jawo wani mummunan abu ya same ta hakan akayi Zainab ta amsa bukatata,lokacin da suka ajiye wayar a ma'adanar sirri wanda babu wanda yasan da wanzuwar ta awajan,ko 10mnt basi ba Ayub yazo ya cire ta batare da sunsan da hankan ba.
Abunda sukai mu Alkhairi ya zamar mana sai suka kulla wata irin soyayya atsakain su me zafin gaske,munci riba su kuma asara ce agare su,duk wani hari da ake kaiwa D muna sane Sani kaike kai masa wanann harin,har harin karshe kasa aka harbi matar sa atunanin ka shi aka harba,hakanne ya fusata mu yin shirimmu na nufin zakaci galaba akammu,wannan shine Abunda kanemi ji daga gareni.
Hayaniya ce ta kaure a parlon,sauran yan Uwansa sun harzuka ashe shine ya maida su marayu,Yaya kuwa jikintane ya fara rawa,tana tsinewa kwadayin ta da dogon burinta,ashe ita atsakiya suka sakata kowa aiki take masa Saboda san abun Duniyar ta,Sani kuwa kallon su yake jin yadda sukai masifar raina masa hankali,ashe wasan daya bukaga shine ya kasance atsakiya ana tamola dashi.
Fashewa yayi da wata mahaukaciyar Dariya wadda kowa ya razana da ita,Bazan yi aikin banza ba wllh saina kashe wanann dan naka kamar yadda na kudurta,tun yana jariri naso murde masa kai Lokacin na rasa menene ya hau kaina ban aiwatar da shirina akan saba,bindigar sa ya dakko wadda babu wanda yasan da ita,kowa a tsorace take kallon sa,saita D yayi da bindigar wanda ko motsawa beyi ba.
Kamar zararre yake jiran saina kashe ku gaba dayan ku saina kashe ku zan zauna nikadai na kwashe dukiyar ta zama tawa ni kadai, momma ce tatari gabansa ta kare D wllh Sani saidai ni kakashe ni agabana ba zan yadda ka kashe dana ba,cikin Kuka ta kara sa furta hakan,me mukai maka meyasa ka tsane mu haka,menene bamiyi makaba,wane girmane Mijina da dana basu baka ba,wave soyayya ce basu nuna maka ba,dama ance makashinka na tare dakai,in har kaga ka taban da to ka fara kashe nine wanann kuwa bani da yadda zanyi na kare shi.
Babu wani alamun yana saurarar ta,zuciyar sa ta makance,idanun sa sunrufe cikar burin sa kawai yake so,danna kunamar bindigar yayi da nufin farawa takan Momma karar harbi ce tasa kowannen su kwanciya a kasa,hankali atashe zufa ce take keto musu,jin parlon ya dauki shiru kowa ya fara bude idanun sa ahankali,bakin kofa suka kalla yan sanda ne birjik tsaitsaye awajan sune suka harbi hannun Alhaji Sani wanda azaba ta hanashi Kuka,sai Lokacin ya fashe da Kuka jin yadda azaba take zagaye jinin jikin sa.
Takowa sukai har gabansa suka buga masa ankwa hannu da kafa sukai waje dashi,sai zullo yake yana zan barwa,sai Lokacin kowa ya saki ajiyar Zuciya,daya bayan daya suka dinga zuwa suna rungume Abbu duk wani haushinsa da Sani ya dasa musu aransu yanzu babu shi,suna jinsa kamar uwa daya Uba daya suke,gaban Mama suka matsa sunai mata barka da zuwa,shafa kansu take cikin tsananin kaunar su,yanzu ta tabbata ita kadaice Mahaifiyar su,kewar Mijinta da Abokiyar zamanta ne ya dawo mata sabo fashewa tai da Kuka tanajin wani irin daci da ciwo azuciyar ta.
Bazata taba yafewa Sani wanann yankan kauna da yayi mata ba,cin soyayya suke da Mijinta yadda kasan Amarya da Ango,sam basa tunawa suna da 'yaya harda jikoki, Love dinsu suke zubawa suna cikin shan roman soyayyar su yazo ya datse mata rayuwa,jitai ana share mata hawaye,dago idanu tai tana kallon sa D ne idanun sa yayi jajawur betaba zatan bakar zuciyar Sani hartakai haka ba,shikansa baffa ya girgiza jin wai dane ya kashe iyayan sa.
Hannun Abbu ya kama da Momma,wadanda suke jifan junan su da wani irin kallo na tsantsar soyayya,Mama yayiwa inkiyar tataso hannunta Mammi ta kama sukai part din su,su Haj Turai gaba daya jiki yayi sanyi nadama ta baibaye su suna dana sanin Abunda suka aikata.
Sanda suka shiga Imti na kwance ita da little a parlo duk wannan gumirzun da aka sha basu da Labari,dago idanu sukai suna kallon bakin kofar,ware idanu Little tayi akan su,wata hantsilawa tayi bayan kujera abunda ya firgita Imti kenan,aguje ta mike itama tana neman wajan buya,dan ita bataga meya tsorata little ba,cikin zafin nama D ya damkota ganin zataje tai masa asara,sai cin gudu take abun Dariya tarasa inda zata samu ta buya,jinta ajikinsa kankamesa tayi tana sakin Kuka sosai ta razana.
Ita ma Little na bayan kujera tana karanta ayatul kursiyyu,Kuka take shabe shabe ta tabbatar fatalwa tagani yanzu bada jimawa ba,Dariya suka saki ganin yadda Little take Kuka bilhakki tun tana Addu'ar azuciya harta fito fili,dakyar Momma ta jawota rungume Momma tayi tana rawar jiki taki yadda ta bude idanun ta.
Murmushi Momma tasaki ai tasan dama dole su razana musamman Little datasan su wanene,ita kuma Imti abunda Little din tai shine ya razana ta,zubawa D idanu sukai da alama ya manta dasu a parlon ya kankame yar mutane kamar zai maidata ciki, Momma ce ta isa har kusa dashi kai cikamin yarinya,ka kama ka danne mata ciki ko sai kaji mata ciwo,sai Lokacin ya ankara da sauri ya saki Imti wadda kunyar duniya ta gama lullube ta.
Kasa kallon Momma tai Saboda kunya,Mama ce ta kalleta da murmushi a face dinta taho kishiyata haka kawai za'ai min kishiya tun tsufa bai kamani ba,Dariya suka saka,kallon matar tai tana kama da D matuka Ahankali tataka har gaban Mama dan rungume ta tai cike da so da kauna,kama hannun Imti tai suka zauna,idanun tane ya fada kan wani kyakkyawan magidanci me tsananin kama da D da Little murmushi taga yanayi mata,ita ma murmushin tai,zama sukai har Lokaci little tana makale jikin Momma.
Zamowa Imti tai tana gaida bakin da tagani tare dasu Momma,da sauri Mama ta ruko ta kul kina irin wannan tsugunnon kinji,gyada kai tayi alamar to,komawatai ta zauna,da kyar Momma taiwa little bayani Abbun ta be mutu ba,da gudu ta haye cinyar sa tana sakin kukan farin ciki,shima rungume ta yayi ba karamun kewarta yayi ba,sai Imti taji itama tana kewar iyayanta,Momma dake kallon ta tsaf ta karan ceta,dan murmushi kawai ta saki.
Hira sukai sosai,D silalewa yayi ya koma daki,shirin zuwa Abuja suke ba tare da Imti tasan da zuwan ba,sun gama shirin su tsaf agobe kuma zasu daga,Mammi da kanta takai Imti gyaran jiki akai mata kitso da kunshi,yaki zanu kitson kamar zana mata shi akai,ba karamun kyau tayi ba,jikinta luwai luwai ma sha Allah,cikin ta harya fara Futowa da kaganta kaga me ciki,har wanann lokacin basu samu zama da D ba tana tambayoyi fal aranta da take so tai masa,meya kaishi gidan su har yake drive dinta.
Washer gari karfe 11 jirginsu ya daga,D ne da kansa ke tukin jirgin wata irin shiga sukaiwa Imti ta alfarma,duk wanda zai ganta yasan cewa eh gaba taci ba baya ba,haka suma shiga sukai ta kece raini kamar Larabawa haka suke tsabar fari da kyau da Allah ya basu.
Sunan dira airport guide din sa sukazo da Motocin tarar sa,bil adama ne dan kam a airport din kamar sun san da zuwan sa,D badai farin jini ba cikin wadanda suke marmarin ganin sa harda Fauza wadda yau taci alwashin saitaga wanann D din inda raboma yayi wuff da ita lol.
Tunda ya fara Futowa daga jirgin kowa ya zuba masa idanu dayawan mutane basu san da ya ainihin fuskarsa take ba sai yau, Little ce agefan sa face dinta dauke da murmushi wani irin farin ciki takeji azuciyar ta,nan hasken camera ya fara tashi ba karamar sacewa sukai ba,tuni mutane suka fara yada Vidion shaharran matashin nan wanda ya shahara fagen kudi farin jini da taimakon talakawa Ziyad M Muhammad Darma da wata tsaleliyar budurwa agefen sa wadda ba'a san wacece ita agare shi ba,abinda ke yawo kenan a social media.
Fauza dake tsaye duk wani tashin hankali ya rufto mata aka inhar idanun ta sun nuna mata daidai Imti wanka take gani, agefen dan tahalikin da take masifar so takejin in bashi bazata iya Aure ba,hannu ta dora aka ta fashe da kuka bubu wanda ya san tana yima balle ya rarrasheta.
🤣🤣🤣Lallai Fauza bakin ciki yana neman kasheta,kin hadu da aiki Imti ta riga ta zarce ki.
Mrs Baba Bello Abubakar
......✍️✍️✍️✍️
💕💕IMTINAN💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 96_97
Idanun Imtine suka ciko da hawaye,ashe Abba dama gata yayi mta,Allah ya sakata acikin ni'ima da gatan da bata taba zatan zata sami irin saba,da kyar take daga kafafunta jin yadda sukai mata wani irin sanyi,hannunta ya ruko tare da sakar mata wani lallausan murmushi wanda ya kara narka Zuciyar ta.
Ummee da Dad na zaune suna kallon News kamar da wasa sukaga ansa sunan Darma baro baro,maida hankalin su kan tv din sukai baki daya,Dad ne cikin jin haushin D ya kalli Ummee kigafa dan bansan yaronnan ya sake shigowa ABUJA Allah ya soni ban fita ba,balle garin harbe harbe a harbemin kai,cikin Dariya Ummee ke kallon sa zatai magana kenan aka fara nuno airport din,ido suka kara fiddowa suna kallon juna.
Kaini Dad kamar nasan wannan Fuskar amma na rasa a ina,nima abunda zan ce miki kenan Amina,kamar nasataba sanin wannan Fuskar,wadda aka nuno hannun su sarke dana juna shiyasa network din kansu ya tsaya na wucin gadi,hannun Ummee har rawa yake wajan nuna Imti,anya ba tsokanarta idanunta ke mata ba,ina 'yarta ina gogaggya da kafar dar shahararran matashin nan,cak Ummee ta sauka daga kan Kujerar tsabar yadda jikinsa ya kasa daukarta da rarrafe ta isa gaban tv.
Haka shima Dad ya kasa tsayuwa akan kafafun sa rarrafawa yayi har gaban plasma din,kamar kauyawa haka sukaje daf da tv din kamar zasu shiga ciki,anya wannan Imtin suce kuwa abunda suke tunani kenan aran su,basu gama wannan tunanin ba sukaji karar bude get motocine duka dinga shigowa kamar bazasu kare ba,gaba daya harabar Gidan tayi musu kadan,Hamisu tsabar firgita toilet ya afka batare daya sani ba.
Su shehu da Malam manu ne sukai jarumtar tsayawa sai rarraba idanu suke,Imti ce ta fara fitowa cikin zumudin ganin iyayanta,kai tsaye maine parlourn su ta nufa,tsayawa tayi abakin kofar fuskarta shimfide da Farin ciki,idanun su suka zuba akanta sai su kalleta su kalli tv din kamar wawaye haka Ummee da Dad suka koma,ganin kamar nasa hayyacin su ya sata takowa idanun ta na cikowa da kwallar kewar su.
Ummee ce tai jarumtar mikewa zuciyarta na tsalle da al'ajabin ganin gagarumin sauyin da 'yarta ta samu,tana nan tana tunanin IMTINAN dinta na kauye ashe abun ba haka yake ba,ta zama wata tauraruwa sai walwali take,hannaye Ummee ta bude mata alamar tazo gareta,wani irin sanyin dadi Imti keji,da sassarfa ta fada Jikin Ummeenta tare da sakin Kukan farin cikin sake haduwar su.
Jin wani abu na tokarin Ummee tai saurin dago Imti daga jikin ta,tsayar da ita tayi tana kallon ta da wani irin farin ciki,lura da kallon da Ummee kewa cikin ta yasata saurin rugawa dakin Ummeen dake kasa,dariya Ummee tasa kamar ta zuba ruwa akasa tasha dan murna,sai Lokacin ta lura da bakin da Imti ta taho dashi,fadada fara'ar ta tayi tanai musu sannu da zuwa,cikin farin cikin haduwa da junan su sukewa Ummee sannu ita ma.
Dad mikewa yayi yana mamakin wadannan hamshakan mata da suka shigo gidan sa,tarba ta musamman sukai musu,kamar hadin baki saiga su Abba da Hajiya Umma,sai iyayan Ummee da suka shigo atare,D ne ya shigo daga karshe Ayub na take masa baya,zuba masa idanu Ummee tai cikin madaukakin mamaki tabbas in har bata manta ba wanann Ziyad ne,Ziyad dai driver,bangaran Dad wani gumine yake keto masa wanene wannan,yake kawai yake amma kasan zuciyar sa cike take da furgici.
Abbu da Dad Yusuf har kasa suka due dar kusa suna gaida Abbah da fara'a yake amsawa,abunda ya daurewa mutanan parlourn kai kenan kamar fa sun san juna, murmushi Mama ta saki Alhaji Kamal min sameku lpy,lafiya lau Maryama,sai suka kara dilmiya su a tunani tabbas sun san juna,hatta D kallon Mama yake da Abbun sa danneman karin bayani,kauda kansa Abbah yayi daga kallon D yana yiwa Allah godiya daya kasance rabon jikar sace.
Little ce ta kalli Ummee,Ummee ina Aunty murmushi Ummee tai ta nuna mata kofar dakin da Imti ta shige,mikewa Little tai ta shiga dakin da Ummee ta nuna mata,tana kwance idanun ta alumshe,dan duka Little ta makamata acinya,occh tace tare da mikewa ta tarama wanann ai wulakancine ina kwance ina hutawa zaki daken,au abunma yar haka ce,ashe kama kuke da Ummee amma tafiki Kyau,dariya Imti tai bawani banda sankai malama,babu batun san kai.
A parlo Ummee kiching ta shiga da sabuwar me aikin tatayata kwaso drinks sàidata cika gabansu da kayan ciye ciye,dan Ummee bata rabo da kayan snacks,kadan suka taba suka ci gaba da hirar su kamar sun san juna,dayake ita ma Ummee tana da wayayyan kai ko ba'a sanar da ita ba,tasan makusantan Ziyad ne.
Sàida komai ya lafa Imti ta fito daga room Little na take mata ta zumbula Uban hijab,a kaikaice D yake kallon ta,hada idanu sukai ta kurguda masa baki, murmushi kawai ya saki kusa da Dad dinta ta zauna tare da lafewa ajikin sa,shidai Dad ganin abun yake kamar a mafarki,yana ta tunanin yarsa nacan ta zama yar kauye,saiya ganta yadda ko amafarki betaba zatan zata dawo haka ba.
Abbah ne yayi gyaran murya,taro ya bude da Addu'a,kowa shiru yayi yana jiran yaji abunda Abbah zai furta, Alhmdlh na godewa ALLAH daya sake hadamu akan Auran Ziyad da Aisha kamar yadda abaya muka taru kamar haka,duk da babu wasun mu dake zaune ayanzu alokutan baya,kamar yadda kuka sani ban bada Auran Aisha ba sàida nasan wanene Ziyad.
Kamar yadda yazo gidannan matsayin Driver bansani dalilin zuwan saba,tun ranar dana fara ganin sa na shaidashi,nasan shi amma ni be sanni ba,ni aminin kakan sane,akwai zumunci me karfi atsakanin mu,Maryama da Muhammad sun sanni farin sani,lokacin danaga Ziyad agidannan na sanar da Maryama halin da ake ciki na ganin Ziyad agidan dana Alkasim,Sunyi mamaki matuka,amma tarokeni na dinga bibiyarka harna tabbatar da menene ainihin abunda ya kawo ka.
Ahankali na fara karantar ka,dukkan wani motsinka nasan dashi,aduk sanda wata rigima ta hadaka da Aisha zallar kishinta nake karanta a idanun ka,wanda kai alokacin ka dauke shi matsayin kiyayya toba kiyayya bace,sonta ne ya mamaye zuciyarka harkakejin zafin intayi shigar dabata dace ba ta fita kake samun kanka da bacin rai.
Hakan dana karanta na sanar da kakarka Maryama ita ta bada shawarar a hadaku Aure ita ma Aisha za'a samu atarota daga tabarbarewar da Ubanta yasaka tayi,abunda mukai shiri sai yazo akan gaba sainai amfani da fushina wajan cewa atake Anan zan daura muku Aure,lokacin nakira wayar mahaifinka yanajin komai a kan kunann sa aka daura maka Aure da Aisha.
Dama haushinta kakeji awannan lokacin kana kwasarta kayi kauye da ita,naji dadin wannnan hukuncina da kai mata wannan shine silar daura muku Aure,kai kanka zakai mamakin danace aranar kajata kutafi dan nasan wanene kai shiyasa nabaka ita kuka tafi tare,shiru Abbah yayi mmaki ya kashe Ummee,Dad,Imti,D, Little dajin irin wannan Aure.
Amma Yanzu ma bata baci ba in har yanzu Aisha bata karbi Ziyad matsayin Miji ba sai awarware wanann Aure,kallon Imti yayi Aisha haryau kina kan bakar ki ko kin sakko kin karbi mijin ki,sunkuyar da kanta tayi,wata zufa ce take ketowa D dan tunanin amasar da Imti zata bayar,karkacewa yayi zai dakko hanky daga aljihunsa,atunanin Imti takadda zai sakko,babu wanda yaga sanda ta taso ganin kawai akai agaban D ta rushe da Kuka.
Ni wllh na zubar da makaman yakina,ko sanda nake cewa seka sakeni Allah da wasa nakeyi ina sonka yanzu wllh ina sonka, fashewa da dariya su Momma sukai Little har fadowa tai daga kujera dan dariya,shima D kansa dariya yakeyi,sàida tafito da hannun sa taga abunda ya dakko wata kunya ta lullubeta,saurin sakin sa tayi takoma bayan Mammi ta buya cikin tsananin Kunya.
Dariya Mammi tayi lallai yarinyata ta fada da yawa,dariya suka sake saki baki dayan su cikin matsanan cin farin ciki,Ummee zuciyarta fes kamar takadda,haka Dad jiyake kamar ya tashi ya taka rawa,sai kunyar D ta rufeshi ya tuna yadda yadinga cemai matsiyaci,ashe abun ba haka yake ba,saiya karayin nadama duk yadda dan adam yake ba abun wulakantawa bane.
Ummee apart dinta ta sauke su,D wani part daban aka kaishi Imti tana makale ajikin Ummee tana bata labarin bayan rabuwar su,sai dataga karfe 9 ta kalli Imti tashi maza kije wajan Mijinki,nidai Ummee awajan ki zan kwana,hararar ta Ummee tai ni kuma nawa mijin fa,nima zuwa zanyi na kula dashi ki tashi ki tafi kawai,kamar zatai kuka take kallon Ummee,au Kuka zakimin,sauka tayi kamar me ta tata tafice daga part din Ummee.
Kiching ta wuce ta dafa masa tea yasha kayan kamshi,a cup ta zuba tabdauki spoon ta tafi inda tasan an sauke shi,a hankaki ta murda handle din bakin ta dauke da yar karamar sallama,baya parlo direct ta wuce bedroom,baya ciki karar ruwa da taji yasata tabbatar da yana wanka, phone dinsa da tagani akan table ta dauka,da password aciki gwadawa tai tayi amma ta kasa cankar abunda ya saka.
Sunan ta tasaka daga karshe saiko gashi ta bude, murmushi ta saki hadda gyara zamanta.Gallary tashiga picks dinta ta fara cin karo dasu babu adadi,wani pic din in tazo kansa har mamaki take yaushe ta dauke shi,tana dubawa mamaki yana kara kasheta azaune,hatta a class sàida taga pic dinta ita dai batasan sanda ta dauki hoton ba.
Jitai an amshe wayar hannun ta,wanna kama kina min bincike a phone,dan firgita tai sam batasan yazo inda take ba,daukowa yayi daidai saitin fuskarta,dan runtse idanu tai kwarjinin sa yawa yake mata,gashi dagashi sai towel ta kasa sabawa da ganin sa haka,lakuce mata hanci yayi kafin ya ruko hannun ta cak ya dagata yayi hanyar toilet da ita,saurin kallon sa tai nayi wanka fa,ban yadda da ingancin saba saina sake yi miki sabo.
Zata sake magana ya rufe bakin da nasa,sun shafe kusan 1hour a toilet din kafin su fito kowannen su face dinsa dauke da farin ciki,karamin towel ya dakko ya tsane mata gashin ta tas ya gyara mata shi,kayan data zo dasu ya maida mata kayan baccine masu taushi,shima kayan baccinsa ya zura kan ya kamo hannunta su zauna a bakin bed din,akan cinyarsa ya dorata,tea din ya dakko wanda ya gama hucewa,bata face yayi kinsa tea dina ya huce,hararar wasa ta wurga masa kasa dai.
Zan tafi ta furta a hakanli,ina? Bcci nake ji zanje na kwanta,ai kinzo kenan bazaki kona ba sai gari ya waye zan daukeki na kaiki har gaban Momma nace ga amanarta nan ban gutsire ki,dan ware idanun ta tayi tana murmushi ai bazaka Iya ba,haka kika ce,eh haka nace dan murmushi kawai ya saki,ki zuba idanu ni bansani gatse ba,kuma Anan zaki kwana ba fashi,kwantar da kanta a kirjin sa,am dama zan tambayeka,kallonta ya danyi inajinki.
Hannayan ta ta fara murza wa,hannunsa ya zura acikin ta, Ahankali yake murza cikin daya fara tasowa,meyasa kazo gidammu matsayin Driver, murmushi ya saki kece kika kawoni,kallonsa tayi cikin rashin Fahimta,daga mata gira yayi alamar tabbatar wa, princess kece kika kawo ni.
Kin tuna wata rana da kika sha gaban wata mota,akokarin ki na lallai saikin wuceta,karo muka kusa yi har muka kusa bige wata tsohuwa,abunda yaban mamaki yakuma dauremun kai maimakon kiba tsohuwar hakuri,sai naga kin bude kofa afusace,kallo daya nai miki na kauda kaina ganin irin kayan jikinki,zagin da kikewa tsohuwar ne yayi masifar bakanta min rai,na tsani naga ana wulakanta dan Adam, guide dina na kalla da.sauri ya fita daga motar,har gabanki ya tsaya yana nuna miki illar abunda kikewa tsohuwar.
Tas naji kin dauke shi da mari da kausasan kalamai agareshi,anan naiwa kaina alkawarin sainaga wacece ke,niyyar saceki nayi tun sanda nazo gidan saina tabbatar na koya miki hankali,amma kirkin Ummee yasa naji bazan iya sakata agarari da tashin hankali ba,sàida na matso kusa dake na tabbatar da rashin kunyar ki,ashe abunda kikaiwa tsohuwar nan kadanne,inajin zafi matuka innaga kinsa kayan da kike mu'amala dasu ada,jinake kamar ana babbaka mun wuta akirjina.
Ban farga na fara sonki ba sàida mukaje kauyan su ya kumbo,tunda natafi na barki banda sukuni,daurewa kawai nake dan inaso ki canza, musamman na roki Ayub ya nemi schl din ku,dan kawai ya dinga kulamin da motsinki,ya tabbatar min babu wani Namiji daya isheki kallo a school din sai hakan yasa nadanji sanyi araina,duk da alokacin narasa dalilin dayasa na damu da irin halayyar ki da dabi'unki ashe sone ya kawo haka.
Shiru yayi yana kallon Imti da take zubar da hawaye inta tuna rayuwarta ta baya takanyi nadama,irin yadda ta dinga wulakanta duk wanda taso,ashe Dad dinnata bakowa bane ajerin masu kudima baza'a saka shiba.Zatai magana ya rufe bakin da tattausan hannun sa, sleep Jijjiga ta yadanyi kafin ya kwantar da ita kamar baby, soyayyar ta kullum nunkuwa take azuciyar sa,haka ita ma kullum sonsa kara girmama yake a zuciyarta.
Mrs Baba Bello Abubakar
......✍️✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 98_99
Washe gari tunda asuba ta gudo saga dakin D sàidata tabbar yafita Masjid ta sulale ta gudu, ahankali take sanda dan kar wani yajita,sannu da zuwa taji an ambata abayanta,tsayawa tai kafin ta juya tana hade fuska,Dariya little ta kyalkyale da ita,kinga Hajiya mene abun bata rai daga yimiki sannu da zuwa,harara ta maka mata wai meyasa little kika sakamin idanu ne,fari tayi da idanu to nima kisamin mana matar yaya,duka Imti ta kawo mata tai saurin gocewa tana Dariya,ita ma Imti dariyar tayi tai gaba.
Bangaran Fauza kamar mahaukaciya haka ta koma gida,yadda take kuka saida Umma ta razana,arude take tambayar ta ko Mutuwa akai yadda taga tana kuka shabe shabe,takaicine ya kama Umma cikin hasala take dan Ubanki bazakimin bayanin abunda yasaki wannan kukan ba,kamar wadda akace uwarki ta mutu,nashiga Uku Umma wllh Zuciyata zafi takeyi kamar zatai fashe,kifito kimin bayani Malama.
Cikin rishin kuka Fauza kefadin Umma ina wanda nake baki labari bilonia dinnan wanda duk inda kika zagaya sunan sa me tashi,har mafarki nake munyi Aure amma yau rana tsaka naganshi tare da Imti narasa gane menene alakar su,ita da aka kaita kauye amma naganta ta fito daga jirgi,tayi gagarumar shiga kamar matar shugaban kasa,tayi fresh tayi fes,nidai Umma ban duro Duniya asa'a ba.
Wani dogon tsaki Umma taja,au wai dama akan wanann kike kuka fuji an kamar zautacciya,to bari na fada miki abunda baki sani ba,bakar zuciyar ki da kyashi hassada bazasu taba barinki kiyi gababa,ko zakiyiwa kowa bakin ciki bantaba zatan zakiyiwa Aisha ba,yarinyar da ubanta ya dauki nauyin karatunki tundaga primary har university,ashe abun naki ya girmama,to aidama ba kalar ki bane kina tunanin kina cikin gidan nan zaizo yace yana sanki,bance hakan bazai faruba tunda komai nifine na Allah.
Amma bakar zuciyar ki bazatasa ki cika burinki ba tunda badan Allah kike so ba saidan dukiya abarda zaki mutu kibarta anan,shawara daya zan baki Fauziyya tun kafin dare yayi miki ki rungumi masu zuwa neman auranki kidaina hangen inda matsayinki bekai ba,ki Auri daidai ke,gaba Umma tai.tabar Fauza tana cigaba da Kuka baji bagani,Lallai Fauza aiki ya sameki.
Suna zaune suna hira da Mammi Ummee tashiga,ananan ana zantawa ta furta fuskarta dauke da murmushi,kamar kuwa kin sani hirar bikin 'yata nakeyi,wacce kenan Ummee ta jefawa Mammi tambaya,Imtinan mana aikin san babu ta yadda zaai ai wannan bikin batare da duniya ta shaida 'yayan gata sunyi Aure ba,babu Inda Aurannan bazai zagayaba sako da lungu,rike haba Ummee tai au biki kai kema Mammi kina da rigima badai anriga anyi ba.
A'ah Ummee ai wannan lami akayi shi,yadda kikasan an dafa kaza babu gishiri,uhm to ai maganar tana hannun ki nima sàidai nazo a yar gayyata,Dariya sukai dukan su,sosai Ummee take burge su babu ruwanta da wani kunya zama take susha hira kamar kawaye.
Kwanan su biyu suka juya amma banda Imti ambarta awajan Ummee da kyar Momma ta kada keyar D suka koma Lagos kamar zayyi Kuka baya son rabuwa da sahibar sa.Shirin biki aka fara tako ina gyaran jiki Ummee takewa Imti gagarumi takanasa ta dakko fanna yar maiduguri ce ita kewa Imti gyaran jiki,damma cikinnan yayi musu cikas baya bari ayi mata abunda ya kamata, abubuwan da aka bata ma wadanda bazasuyi mata illa bane.
Lefe Momma da Mammi da kansu ba sako ba suka nufi Japan,daganan suka wuce India,sannan suka dira a Dubai,kaya ne kamar wadanda zasu bude store,wasu azababbun akwatuna ne masu matukar kyau da tsada,ranar da suka dawo haka su Haj Suwaiba da jiki yayi La'asar tuni suka yadda makaman yakin su,amma sukadai sukasan masifar da suke ciki ko baccin dare basa iyayi,ga mazajan su da suka tsane su matuka,kowacce za'a dan karo mata kishiya Budurwa me jini ajika.
Akwatuna 50 kowacce shake da kaya,mutanan adamawa dana jimeta tuni suka diro dan wannan shagalin dasu za'a yishi,sune suka tafi kai kaya haka Motoci sukadinga layin shiga gidan su Imti,ita ma Ummee danginta sun hadu,haka dangin Dad tarba ta musamman akai musu,kayafa sun gigita jama'a Gold din da aka zuba mata ba iya,makullan motane dan kara danka guda biyu,abundai sai san barka,tukaici gagarumin suma su Ummee suka bayar aka tsaida ranar da za'a sha shagalin biki.
Get pass din Dinner da zallar gold aka rubutashi,duk wata tv redio zan can bikin akeyi,Abbu kasa kasa haka yadinga gayyata,haka D jiga jigan abokansa yan kasashe daban daban haka ya gayyato su,amarya fa tayi kyau hatta gaji,inka ganta ba Lallai la gane ta ba,kullum tana makale da Mijinta awaya kamar zasu hadiye kansu.
Tana zaune a maine parlo suna hira da Ummee su fidy da Lubna suka shigo,ihun murna suka saka suna rungumeta,cikin tsananin kewarta suke kallon ta,Lallai sun yadda Allah ya sake daga Imtinan din su,Ummee suka gaishe ta amsa fuskarta asake,kallon su Imti tayi naganku ku biyu,toda mu nawa zakigammu,ina Fauza,wani tsaki Fidy taja tanacan bakin ciki da hassada suna neman kasheta adaki,wai ashe duk korar samarin data dingayi mijin ki take so,ba karamun dadi taji ba daakace a wullaki kauye ranar kamar ammata albishir da gidan Aljanna.
Ni dama na dade da karantar ta,zugakin da takeyi kina rashin mutunci dan sunan ki ya bacine,nasha gaya miki dama ba kaunarki take ba yanzu kin yadda da maganata Fidy ta karsashe Magana tana hararar Imti cike dajin haushinta,dan murmushi ta saki na yadda Fidy na tabbatar ku masoya nane,sanda bana tare daku na gane hakan,nagode friends tafawa sukai suna sakin dariya,duk hirar su Ummee najin su,tabbas mutum abun tsorone dama duk cikin kawayan Imti tafi tsanar Fauza dan hassada muraran take gani a idanun ta.
Wai da bamu zoba bazaki gayyace muba,mikewatai kutaso muje dakina,mikewa sukai dariya suka saki,ke memuke gani kodai kaya kika cusa,harara ta maka musu bansaniba,hhh Lallai wannan bikin na musamman ne ga dan baba aciki,masu bikin 'yan gayu,tsokanar ta sukai tayi,tsara yadda bikin zai kasance suka sakeyi dan babu abunda zai hanasu dagawa Lagos kafar su kafar Amarya.
Rana bata karya saidai uwar diya taji kunya,yaune za'a gudanar da gagarumar Dinner din Ziyad da Amaryar sa Imtinan,bikine fa akeyi na manya masu murza naira, airport din kewa yayi da bil'adama,jirage na musamman Abbu ya ware kawai dan jigilar dakko masu zuwa wannan biki,aiko haka aka dinga tururuwar shiga bayan an caje ki tas tukunna za'a baki damar shiga,wani irin cord less aka dinka,tun ajirgi za'a baki kayan ankon ki da zaki saka,jakace shake da kaya,babu wani abu dazaki bukata Komai na kwalliyar ya mace akwaishi aciki.
Kayan da kawayan Amarya zasu saka daban yake,haka abokan Ango,kayan iyaye mata daban,na iyaye maza da ban,su Alhaji Yusuf sune agaba komai an damkashi a hannun su shida Mammi,kai tsaye da aka dakko Imti estate akayo da ita,har Ummee da Dad akayo gayya,farin ciki ya cika zukatan su ganin irin cigaban da Allah ya basu,saidai su gode masa.
Karfe 9 aka fara daukar masu tafiya,ranar babu wanda akaiwa get da shiga estate din,Allah sarki Surayya tana dakinta kuka take kamar ranta zai futa,tuni dama tadan D yayi mata nisa,bakin cikin ubanta boka gata shegiya shiya hadu yayi mata yawa,kamar mahaukaciya haka ta koma,Mammi da kanta tazo har part din Hah maimuna wadda warin da take yanzu ya gawurta,babu me zuwa kusa da ita,duniya tai mata atishawar tsaki,lallashin ta tayi tajata sàidata tabbatar tai wanka ta bata kayan da kawayan Amarya zasu saka itama ta saka,da kanta ta zauna ta tsara mata kwalliya.
Haka Mammi tabi su Safnah kowaccen su kuka take sunsan D ya tsere musu,irin kayan data sawa Surayya shi tasaka musu,saiga su haj Turai da carbi ahannu,itama Yayah ba abarta abaya ba cikin shigar iyaye ta futo,gaba daya jikinta yayi laushi,yadda ta godewa Allah Abbu be mutuba,har gaban Mama taje tana neman yafiya Mama tace bakomai ai ita taimakon ta tayi ma,da yanzu Sani ya kashe mata da,aiko Yayah taji dadi saita kara sakin jiki.
Amarya aka futo da ita, kawayanta na take mata baya,tamkar kasace ta ka gudu haka tai tsananin kyau,babu wanda bazai gane cikine da ita ba,ba karamin kyau cikin yayi mata ba,motar da D yake ciki nan aka sakata,yayi azabar kyau kayansu iri daya,tana shiga yayi mata masauki akan cinyar sa,ba karamin kyau tayi masa ba,yayi missing dinta sosai,ganin yana neman goge mata kwalliya tasa rigima,dan dole ya kyaleta ya koma rarrashin ta.
Waje fa ya kawatu matuka,ko ina security ne ga kuma guide dinsa da suka cika wajan,cikin fararan suit suma wannan dinner dasu za'ayita.
Wakar Amarya da Ango aka saki,Amarya soyayya Ango shima Soyayya da dolos aka fara yi musu liki,sàida Imti taji ta fara gajiya dakyar suka samu aka barsu suka.zauna,hasken flash sai tashi yake kai abundai ba'a cewa komai,kowane tim da group din su,kowa harrakawa yake yana kimtsa cikin sa.
Canna hango tim din matan sirri,kowacce taci kwalliya ta kafa dauri,tana bawa cikinta hakkinsa,sirrin kwalliyar 'ya mace suma ba'barsu abaya ba sun amsa gayyata kyau sun zubashi,kowacce bakinta yayi dumu dumu da baman daweesu🤣lol.
Can na hanga nagano Makarantar 'ya Mace suma ba'barsu abaya ba,sun sha wanka suna bawa cikinsu hakkin sa,ga tim din Mace Tauraruwa Ladies sai harrakawa suke kowaccen su ta cakare,suma tim din Kulsoom hausa Norvel ba'barsu abaya ba sun hallara,ga tim din Mrs Baba Bello Abubakar sun amsa gayyata suma,sai muwalati suke da naman kaji,kai suma tim din ma'adanar sirri ba'barsu abaya ba,sai kulu washi rabu sukeyi babu kama hannun yaro.
Can dana hanga nagano tim din Sirrimmu mata,suma ba'barsu abaya ba,can na hango admin Hibba tanacin uwar sabada lol,tim din Mijin kwaila hausa Norvel ba'barsu abaya ba shan shagali suke abundai sai san barka,tim din Taskar Littafan hausa suma sun amsa gayyata shan sha'ani suke,tim din Gidan Littafan hausa suma sun hallara awanann biki na yayan manya,yayan Girma masu ji da kudi da izzah,tim din Hafsat hausa Norvel suka fa sun amsa gayyata sun taho da kwarin su ana harkar arziki tare dasu.
Dandalin 'yammata suma ba'abarsu abaya ba sàida suka hallara kowacce budurwa taci kwalliya,can na hango Khadija tana kara bada hoda ko zata samu wani dan baturen yayi wuff da ita🤣🤣.
Bikifa yayi biki Momma ta zubar da naira,haka Abbu Ummee ma ba'abarta abaya ba,Dad haka ya bude bakin aljihu yana zazzagawa shalelen sa,Abba da Mama suma sun nuna bajintarsu,anci ansha angodewa Allah.
Nikaina Kulsoom naci nayi kat tare da hubbyna dake gefena azaune baba bello babayn Alkhairi.
Ina da falajin duk wadda cikinta ya baci ta garzayo ta amsa,lol
Mrs Baba Bello Abubakar
......✍️✍️✍️
💕💕 IMTINAN 💕💕
Written and Narrated
By Kulsoom Ismail Idris
Page 💯
Last page
Sai guraran 12 aka tashi daga wajan Dinner estate suka kara tafiya da Imti atunanin D za'a bashi matar sa su wuce adarennan Momma tace be isa ba,kamar zai fashe haka yabar event din afusace,washe gari aka sake dora biki daga inda aka tsaya,ansha shagalin yan jarida da masu vidio tashashan TV sune suka dinga daukar rahoto da sanarwa wadanda basu sami halatta ba,yadda shagalin yake tafiya.
Imti ta jigata ainun shiyasa Mammi ta boyeta adakinta acan ta dinga shan bacci dama yanzu bata rabo da bacci,yau ankon atamfa aka saka iri daya,anci ansha anyi barin naira,sauka rantse babu wani talauci dan awannan bikin ba karamar barazana akaiwa talauci ba,ammasa fata fata,aranar ne kuma za'a kai Amarya shahararran gidan ta nagani na fada.
Karfe 6 na yamma ta tsala wanka cikin atamfa bubu saboda yanayin cikinta kartasa kayan da zai takura mata,gaban Ummee aka kaita gatan da bata samu ba awancan lokacin yanzu shi aka nuna mata,nasiha sosai Ummee tai mata,haka Dad,Momma ma ba'abarta abaya ba kamar Little haka take ganin Imti.
Mammi ma.tayi tata nasihar,su haj Turai ana rakube sai rarraba idanu suke,fuskarta daure da nikaf saboda munin datayi,inkaganta bazakaso ka sake kallon taba,haka Imti tana kuka aka saka ta amota,jerin gwano sukai suka nufi Banana Island estate ne guda,kai wannan Gida ya hadu fasaltashi ma bata lokacine,duk yadda kuke zatan kyawun Gida to wannan makura ne,katafaran bedroom dinta aka shigar da ira.
Wani irin sanyi da kamshine yake tashi me dadin shaka,anan ma sàida Mammi ta sake yi mata fada,afakaice su Hajiya suwaiba suka dinga share hawaye da yanzu yayan sune Acikin wannan daular.
Akwai wasu security mata da aka zube a bakin get in kinzo fita wata leda ake miko miki sai walwali take ga nauyi daka ganta kasan kayan arzikine aciki,sàida sukaje Gida suka bude,kayan snacks ne da gasashshiyar kaza da kudi 20k kyasha ruwa ahanya,haka kowacce zata zuge jaka ta sakaye kudinta,tana san barka da wannan biki da tazo.
Basu jima da tafiya ba D ya shigo be yadda kowa ya biyo shiba shikadai ya taho wajan sahibar sa,tana zaune kanta arufe tana shashshekar kuka,har Dariya ya saki kukan me kike daga jin wannan kukan na gulma ne,sake bare baki tai cike da shagwaba,narkewa tai ajikin sa cak ya dauke ta suka fada toilet.
Soyayya dai cinta ake kamar ba gobe,kamar su hadiye junan su,zallar soyayya yake nuna mata mara algus,dandanan ta kara habaka ta burun kasa,yanxu cikin ta ya shiga watan Haihuwa, Momma ta hura masa wuta ya Kawo ta amma yaki wai aishima zai iya kulawa da ita.
Sosai tayi nauyi kafafunta duk sun kumbura hancinta ya zamo badarere,yana zaune agabanta yana matsa mata kafa kallonta yayi kafin ya fashe da Dariya bakaramar dariya yakeba inyaga yadda ta dawo,bata fuskai tana hararar sa,kukan shagwaba tasa masa dama yanzu abun kadan saita kama kuka,rarrashin ta yahau yi,jitai cikinta ya hautsina bayanta ya rike.
Wash ta furta tana runtse idanu jin wata azaba da bata taba jiba,hankali tashe yake tambayar ta amma ta kasa magana sai yarfe hannu take,hijab ya sakko mata da sauri,daukarta yayi dakyar ya sata amota,a hanzarce aka amsheta labour room akai da ita.Momma ya kira ya shaida mata aiko dan danan suka cika asibiti,zagaye Kawai yake yana Addu'a,tsahon away daya doctor din tafito tana kallon su da murmushi a face dinta.
Akawo kayan baby da sauri ya koma mota yadakko akwati guda,tasauka lpy cikin murna suke Alhmdlh,sàida aka shirya su sannan aka basu damar shiga tana kwance tana bccin wahala,baby's suka hango guda uku,turus sukaja suka tsaya,dariya doctor din tayi duka nakune,har bangazar juna suke wajan isarsu bakin bed din,kyawawane yaran masu matukar kama da D dukansu matane,ji yake kamar amafarki wai shine me yara har Uku Alhmdlh ya dinga furtawa.
Daukar yaran suka dingayi,dandanan haihuta triple din ya kewaya lungu da sako,dam asibitin ya cika,Ummee har kukan farin ciki tayi jin Imti dinta ta haifamata jikoki har Uku, Dad ma yarasa inda zaisa kansa,aranar suka dungumo ganin baby's, sanda Imti ta farka taga wannan kyautar da Allah yayi mata bakaramin farin ciki taiba.
Dubata akai bawata matsala dunguma sukai Momma tace itace zata wuce da ita,D duk yadda yaso shawo kan Momma kin yadda tayi,Imti samun kula suke tako ina ranar kwana uku Ummee ta juya ABUJA itama zatai nata taron aciki,kyautar company Grand father ya basu kowacce dai dai bayan makudan kudin daya mallaka musu ,yara sunci sunan Momma Aisha,Mammi Zainab,Ummee Ameena,haka aka rada musu, Nick name din da za'a na kiransu dashi,Afreen Afrah,Amrah haka za'a dinga fada musu.
Ranar sunan shanu Uku raguna shida haka aka kayar aka yanka musu bayan naman suna da Abbu ya yanka sa ayi miyar suna dashi,bags calendar haka aka bubbuga da hoton jarirai,Imti tasha kyautuka naban mamaki,saiga wagar su ya Kumbo sun iso suma,ansha suna an rakashe an gyaguje,komai dai sai san barka.
Haka suka ci gaba da wanka cikin kwanciyar hankali,su Afreen nashan gata,sunyi bulbul sàida sukai wata biyu suka koma gidan su,yan aiki aka hadata dasu hausawa kar yaran su dakko irin hadin turawa.
Fauza dai haka ta karaci zaman jira tun samarin suna zuwa yanzu kowa ya gudu,sungaji da wulakanci da take musu,abun Duniya yayi mata zafi.su Fidy kuwa anyi bikin su Imti ta taka rawar gani,anyi bikin Little da sir Ayub su Imti sune agaba.
Abubuwa da dama sun faru bayan haihuwar su Afreen,ciki kuwa harda mutuwar haj Maimuna cikin kaskanci tazama abar tsoro,sai Alhaji sani da hannun sa ya rube saka makon harbin da akai masa,anyanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya,yayi nadamar da bata da amfani.
Turai ma da kyar aka samu fuskarta tadan farayin dama dama,su Haj Kubrah saidai kaga sukadai suna zabura babu wani cikakken hankali atare dasu,yayan su ansamu ammusu Aure suna gidajan su har Surayya aka hada wadda ta koma hannun Momma da zama bayan rasuwar mom din ta,anje neman mahaifinta aka tarar wuta ta cinye bukkar da yake tsafinsa ya babbake aciki.
D bai manta da Mutuncin su Malam manu me gadin gidan su Imti ba dasu Shehu gidaje ya mallaka musu da jari me tsoka,Hamisu dubu dari biyar ya bashi cike da kunya Hamisu ya dinga godiya.
Imti ta koma makaranta ta zama babbar mace yar kasuwa wadda ake damawa da ita,it's kanta yanzu kudi ne da ita bana wasa ba,ta kara kyau yayan ta sungirma sosai,ayanzu tana dauke da wani ciki,Dad shima arzikinsa ya kara bunkasa,D ya zuba hannun jari a kasuwancin su,sun canza kata faran Gida nagani na fada.
Suna zaune suna kallo Afrah ta tsokano Amrah biyota tayi zata daketa Imti tai saurin dauke Afrah, Amrah ta fara kukan saita rama D ya daga ta sama yanai mata waka,Afreen ce tataso nima Abbu tana daga hannu itama adauketa dire Amrah yayi ya bude musu hannu alamun su taho,dire Afrah tai suka.kasa tsere harda ita gaba daya ya hada ya rungume su,cikin wani farin ciki ya furta ina kaunar ku iyalina,muma muna kaunar ka Jannaty,dariya suka saka gaba daya.
ALHMDLH ALA KULLIHALIN
Ina me godiya ga ALLAH daya nunamun karshan wannan Littafi da rai da lafiya.
Godiya ta musamman agareka Mijina kaine kwarin guiwa ta,ina Addu'ar Allah ya barmu tare ya kara dankon soyayya.Allah ya faran ta maka kamar yadda kake faran tamin,Allah ya daukaka darajarka,Allah yayi ruko da hannayanka.
Ina Godiya da Admins din danake Update a group dinsu Allah ya saka da Alkhairi.
Ina mika Godiyata gare ku Fans masu bibiyar labaraina,ina jin dadin Addu'ar ku gareni,Allah ya faranta muku kamar yadda kuke faran tamin da kyawawan Addu'o'in ku.
Abunda na fada daidai Allah ya bada lada,kuskure ko tuntuben harshe daga gareni Allah ka yafe mini Allah kai mana afuwa baki daya.
Anan nake cewa daku......
Bissalam
Daga alkalamin Mrs Baba Bello Abubakar.
.......✍️✍️✍️✍️✍️✍️
ALHMDLH ALA KULLIHALIN
0 Comments